A Rubuce Take Book 2Hausa Novels

A Rubuce Take Book 2 Page 11

Sponsored Links

Part 02

Page 11

Yana turo qofan dakin ta kalleshi,irin kallon mamakin nan wanda tuni ta shiryama hakan

“A’ah,abban mimi ba kwanana bane” idanunsa ya zube fes akan fuskarta,yana iya hangen wani abu fake behind her face,sai ya lumshe ido kadan ya gyada kai

“I know” sai ya qarasa ya dauki duvet dinsa da pillow ya juya ya fice yana ja mata qofa.

Da kallon mamaki ta bishi,saita miqe ta nufi qofar yana leqensa,saman kujerun parlor din ya shimfidashi ya yada pillow din ya kwanta bayan ya rage hasken qwan falon,ranta yayi mummunar baci,wato ita bai isa ya kwana gurinta ba,saboda kwanan gimbiya ne?,har ta buda qofar zata iskeshi a falon wata zuciyar ta haneta,saita koma da baya ta maida qofar ta rufe.

A wannan daren haka kowa cikinsu ya kwana,kowa da irin abinda ke kai kawo a zuciyarsa.

*******Tun daga ranar suka koma ‘yar haka dashi,sai sa’ar gaske yake iya sanyata a qwayar idanunsa,tuni ta ajjiye girkinta dama komai da komai,iyaka ta gyara bedroom dinta da kanta,idan tana da ra’ayin hira ta kira wanda takeso cikin ‘yan uwanta,ummunta anty deena ko anty madeena koma mom dinta,ko kuma ta fice wajen maari susha hirarsu,ita kuma dake mata kallon me qaramin ciki tayita mata dafe dafe na abubuwan gargajiya,wanda da gudu widad din ke ci,don wasu abubuwan ma ta manta dasu sam,ummu ke musu lokaci lokaci a gida dama.

Ba wanda ta taba gayawa abinda ke faruwa,don sai taji abun baya ma wani damunta gaba daya,yammaci tana yi dab da zai dawo zata koma dakinta ta kulle.

Yadda hafsat take ganin damuwa qarara tattare da abbas din sai hankalinta yayi mugun dagawa,bata taba zaton baka ya damu da yarinyar ya kuma bata muhimmanci mai yawa cikin rayuwarsa ba irin wannan lokacin,ta auna ta auno……taga kaf zamansu bata taba irin wannan sakarcin ya damu da ita haka ko yabi ta kanta ba,hasalima wani lokacin saidai ta bude qofar ta tarar ya koma wajen aikinsa ya ajjiye mata dan note.

Kishi sosai ya tasata a gaba,ta daina jin dadin gidan gaba daya,ba zata iya jure ganin soyayya da damuwar abbas akan wata diya mace ba a gaban idanunta tana raye ba,sai ya zamana bata da aiki sai mita da qorafi

“Gaba daya qaramar yarinya na neman rikita maka lissafi,totally ka canza abban mimi,ba ita ta zabi haka ba,aiba wansa ya tilastata,saika qyaleta idan ta gaji ta watsar…..banda ma iyayin banza da samun waje,mema akayi mata?” Sai taja qaramin tsaki.

A sannan yana shiryawa ne bayan ya fito a wanka,sanda take wannan maganar ma yanata bulayin neman wankakkiyyar singlet da zaisa duka babu,ya watsar dana hannunsa yana duban idanunta

“Kin gaza ta abubuwa masu yawa,wannan ya sanya dole nayi kewar kebance kanta da tayi daga wajena,abubuwan da kika kasa ita din duka bata daukesu a komai ba…….ki jiqamin singlets dina da hypo zan wanke da kaina,na gaji da siyan sabbin undies,idan kin gama ki gyara parlor zuwa cikin dakin nan,idan Fresheners dinmu ne suka qare ki gayamin,idan na fita zan shigo da wasu,banason na dawo na samu gidan nan a yadda yake” daga haka ya juya yaci gaba da shiryawa.

Turqashi!,ita yake kafawa misali da widad din?,daya kafa mata misali da ita gwara ya buga mata misali da mutuwarta,sai ta rikice masa gaba daya itama,tana ganin bata da wani amfani a wajensa,baya ganin kimarta sam a cewarta,gaba daya saboda yarinya guda daya jal ya rasa walwalarsa ya rasa sukuni,yanata qoqarin shawo kanta tana wahal dashi,ita kuma da take iya bakin qoqarinta a kansa baya gani,bai dauketa da daraja ba.

A hankali sai damuwa ta fara yi masa yawa,tako ina ba dadi,widad itace sanyin idaniyarsa,ita ta zamewa rayuwarsa wani bango da zai jingina ya samu relief a duk sanda wani damuwa ta sakoshi gaba,ba damuwar hafsat kadai ba,hatta damuwoyi da matsalolin gurin aiki,don rigimar hafsat ya riga ya saba dasu,to amma a yanzun da suka hadu da juya bayan widad sai abun yayi masa tsauri da yawa,dole ya dauki hutun kwana biyu don ya samu ya gyara komai,bauchin da zasuje ma ya daga tafiyar sai satin gaba,bayason su tafi bauchi a haka,yasan bazai fahimci komai ba har suje su dawo.

Ranar farko wuni yayi a parlor din gidan shi da yaran,salla ce kadai take fiddashi,gaba daya zaman yayishi ne a bisa dole,don yadda widad din ke bashi kulawa ta musamman a duk sanda zaiyi wunar musu a gida irin haka bai samu koda quater din wannan daga hafsat ba,saidai ya share ya maida hankali ga yaransa da kuma gyaran bedroom dinsa da hafsat din ta tasamma sauya masa kamanni da halayen baqar qazantarta,ya gama sukayi gyaran parlor tare da yaran,baiko nema sa hannunta ba,saita fake da girki a kitchen.

Duk bidirin da akeyi widad din tana jinsu tana daki a kwance abinta,tunda ta fuskanci wunin gidan zaiyi sai taqi yarda ma ta bude qofan bare ya ganta,ta kunna data tayi chart sosai irin wanda ta jima batayi ba,daga baya ta koma youtube ta vidmate ta dauko K dramas da chinese masu yawa na soyayya ta shiga kalla abinta,abinda ya rage mata tsahon wunin sosai.

Da mamaki ya kwana,washegari bayan ya tattara su dukka ya kaisu wankin kai,don ya gaji da kallon buyagin kan hafsat din da bata damu ta gyara ba,daga nan yace ayi mata harda manicure and pedicure

“Amma dai…..da kudin yaran ka bari a hannuna,sai nayi musu su a gida” ko ta kanta baibi ba ya tashi motar yana cewa

“Idan kun gama let me know,zanzo na daukeku” yaja motar abinsa,don tuni ya tura kudin komai ta Account din kamfanin, gurin da widad ke zuwa ne,kuma gyaransu yana da kyau,already yana da details nasu dama saboda yadda ta saba da zuwa wajen duk bayan wani lokaci.

A masallaci ya fara tsaiwa yayi sallar azahar sannan ya qaraso da motar cikin gidan.

Duk da yasan babu kowa cikin Parlor din amma hakan bai hanashi yin sallama ba,kai tsaye ya doshi dakinta,yana jin cewa yau zaiyi maganinta,murdawa daya ga mamakinsa qofar ta bude,ya tura ya shige,ajiyar zuciya mai tafe da numfashi mai nauyi ya sauke, sassanyan qamshin nan da yayi mugun kewa shi ya fara masa maraba,ko ina na dakin fes dashi yana bada qamshin nan daya cakude ta turarukan jikinta,he missed her badly….. He missed komai da ya shafeta.

Ba kowa a dakin sai ya tura qofar toilet din,itama wayam ba kowa,saidai da alama ba’a jima da gama amfani dashi ba,farare qal qal din undies dinta shanye a ciki suna digarda ruwa fari tas da alama sun wanku da kyau,sai qamshi suke fiddawa dasu da toilet din gaba daya.

Da baya ya koma yana tunanin ina zata,ya tabbatar ba zata fita daga gidan ba ba tare da ya sani ba,tunani ya fado masa,saiya koma da baya yayi boys quaters.

Dai dai sanda tayi rashe rashe abunta a dan qaramin parlor din maari tana cin dumamen tuwo miyar kuka,har tsakiyar kanta takejin dadin tuwon,maari na daga bakin famfo tana dauraye kwanukan da baba mai gadi ya gama cin nasa abincin,suna dan hira kadan kadan taji sallama daga bakin qofa.

Sam hankalin widad baikai kai ba,tuwonta kawai take azawa cikinta, maari ta aje kwanon taja mayafi ta leqa,sai taja da baya cikin matuqar girmamawa da jin nauyin abbas ta soma gaidashi,ya amsa mata a mutunce yana tambayarta widad din,tace masa tana ciki

“Zaka iya shiga yallabai” ta fada tana rabeshi ta fice a sassan ta wuce sashen hajiya,don dama akwai gyaran da zata mata yau din,gobe ko jibi zasu dawo daga balaguron da sukayi,tayi hakane don ta karanci kamar akwai ‘yar matsala ko sabani a tsakaninsu,batason saka baki ne a abinda bai shafeta ba,kuma ba’a yi mata tayin shiga ba.

A nutse yake ratsa tsakar gidan nasu har ya isa qofar rumfar tata,idanunsa ya zube a kanta yadda take cin tuwon nata kamar ta samu nama,harma batasan ya iso wajen ba,ya qare mata kallo a nutse,kallon da bai samu yi mata shi ba tsahon sati kusan biyu,ta sake wani mugun cika,hatta da idanuwanta sun qara haske da girma,farinta ya sake daduwa kamar jini zaiyi tsartuwa a jikinta,duk da akwai madaidaicin hijab a jikinta,amma hakan bazai hanaka ganin yadda qirjinta ya cika fam ba,daga inda take zaune kuma baka isa ka nuna ciki a jikinta ba,abun yana mugun daure masa kai,yadda cikin yabi jikinta sosai,kamar bayason a ganshi,ya lumshe idanunsa kishinta yana cikashi,haka ta sake cika amma kullum take baro dakinta tana wuni a nan?,ko waye da waye suka taba kallon masa ita?.

Tayi matuqar fusgar hankalinsa,wata kewarta mai zafi ta dinga taso masa,sai ya gaza jurar ci gaba da kallonta,ya tsugunna ya zare takalminsa,sannan ya miqe ya saka kansa rumfar maari,duk da ba haka yaso ba,amma yana jin kamar wani magnet ke jansa zuwa gareta.

Sai daya kusa isowa gareta sannan turarensa ya ankarar da ita,tana dagowa idanunsu suka sarqafe waje daya,ta tsame hannunta zata miqe,ya saka dukka wani zafin namansa ya riqeta gam,ya kuma jawota zuwa jikinsa suka zube a wajen,bai tsaya wata wata ba ya hade bakinsu guri guda ya fara sauke mata french kiss mai zafi,wanda ya sanya cikin lokaci kadan jikinsa ya dauki rawa gaba daya,kamar wanda aka watsawa ruwan qanqara a lokacin hunturun sanyi,yayin da bugun zuciyar widad din ya qaru qwarai,har tana jin yadda abinda ke cikinta ya takure ya cure waje daya kamar yasan abinda ke gudana tsakanin mamarsa da abban nasa.

Sai da yiwa zuciyarta laga laga,ya luguiguitar da ita,ya kuma sauke duk wani fishi dake maqare a zuciyarta sannan ya saketa yana maida numfashi,abun ya zame musu kamar wani faamin ciwo ne da tayar da tsohuwar soyayya da kewar juna da sukayi na nisantar juna da sukayi tsahon satittikan.

Saida bugun zuciyoyinsu suka daidaita sannan ya sauke mata kallonsa da wani irin zazzafan kallo dake saka mutum a shauqi,tayita kauce masa tana jin nauyin yadda ta sake masa jiki haka ba tare data iya kare kanta ba,tabbas ta karbi saqo yadda yakeso,don yaga alamun haka a tattare da ita

“Widad….” Ya fada muryarsa a mugun sanyaye,bata iya amsa masa ba,shima kuma bai damu ta amsa din ba ya dora da cewa

“Fushi kikeyi dani?……wanne irin fushi ne haka widad?,so kike zuciyata ta buga?” Statement dinsa na qarshe ya sakata dago kai da sauri ta kalleshi,ya samu yadda yakeso,ya kuwa riqe qwayar idanunta da kyau ya hanata motsawa.

Fuska ta narke cikin salon shagwabar nan tata da yayi mugu mugun kewa

“Ba kai bane ba…..” Kawai sai ta fashe masa da kuka,gaba daya ta ida rikitashi

“Ya salam” ya fada yana matsowa gareta gaba daya yahau aikin lallashi baji.ba gani,har zuwa sanda zuciyarta tayi sanyi

“Pardon me please,I assure you it may not happen again” ya fadi hannayensa hade da juna,shi kansa yana mamakin yadda ya dinga misbehaving nata a lokacin,baisan me ya shiga kansa ba,amma a wannan lokacin sai zuciyarsa ke bashi kawai hafsat keda gaskiya,yasan ya mata abubuwa marasa dadi da yawa wannan shine kusan na biyar ko goma,amma ko a fuska tana qoqarin cinyewa,iyaka ta tura masa baki ya kama bakin yadan ciza shikenan an wuce wajen,a wannan karon ne itama ta gwada masa tata matantakar.

Kai ta gyada tana sharar qwalla,sai yakejin kamar tana yankar naman zuciyarsa ne

“Don’t cry mana,haba babyn uncle,It really hurting me when I see you crying” ya qarashe maganar yana tayata sharar hawayen.

Fadan masoya hutu inji hausawa,cikin qanqanin lokaci ya wanke kansa a zuciyarta,daga qarshe dai jawa maari qofar sassanta tayi tabi mijinta.

Tun daga parlor ya fara sauke mata dakon lodin soyayyarta daya dauka bashi,ta kuwa sakar masa kanta yayi yadda yakeso da ita,harma fiye da yadda ya zata,saboda sabon karatu data sakeyi wajensu fanna,kuka ya dinga mata saboda gaba daya ya gaza controlling kansa,duniyar da widad ke kaishi a duk sanda yake tare da ita……wata irin duniya ce mai nisan gaske da babu a inda yake nasarar zuwa nan idan bata bangaren widad din ba,’yar gaske ce ta wannan bangaren,mai madaukakiyar baiwa da ni’imar da ita kanta bata gama fuskantarta ba.

“Me kuma nayi maka uncle kake kuka?” Ta fada tana tura baki gaba,fuskarta a tsakiyar tafin hannunsa,idanunsa jiqe da lema ya girgiza kai yana murmushi

“Komai ma widad,komai ma kinyimin” saita zare ido,ya dora hannunsa saman lips dinsa yana fidda mata fararen mayanyan idanunsa

“Shshshs…..ba zaki gane ba ko meye zance miki yanzu, I don’t know how to stop my self from crying duk sanda na kasance tare dake,bazan iya misalta dad…..” Tasan me zaice,kalmar kuma na masifar bata kunya,hakan yasa tasa tafin hannunta da sauri ta rufe lausasan labbansa tana boye kanta,sai ya dora nasa hannun saman nata yadan ciji tafin hannun nata kadan

“Wayyo hannuna” ta fada tana janye hannun cikin shagwaba tare da yarfar dashi gefe,ya lakuce mata hanci

“Shagwababbiya kawai” suka saki dariya a tare.

Tare sukayi wanka,ta shirya cikin doguwar riga umbrella shape data bude sosai,mayyar dogayen riguna ce ita din,wanda hakan ya taimaka sosai wajen sake sirranta cikin dake jikinta,shi ya taimaka mata ta gyara shimfidar gadon da ya yamutsa,hatta da pillows a qasan gadon ya tsinto mata su,tanata tsokanarsa yasha mur cikin wasa yana basarwa

“Duk aike kika jawo”.
[09/05, 4:06 pm] +234 816 283 5575: *H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)

Back to top button