Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 49

Sponsored Links

aid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, masu buƙatar vip ko special kuma, suna iya garzayawa arewabooks ku searching sunan littafin*

A razane ta waiwaya tana kallon in da aka yi mata tsawar, wasu dogarai ne su biyu suka shigo suna baza riga, shigowar ta su yayi dai-dai da lokacin da rumaisa ke gatsali da sunan takawa.

“Hattara dai yarinya, hattara ‘yar talakawa, ba a furta wannan sunan hakan babu girmamawa”

Ɗayan ya juya ya kalli Adam ya ce
“gaba salamun baya salamun, takawarka lafiya magajin saraki, basarake ɗan basarake jikan basarake, mai babban suna, takawa magajin takawa, motsawarka lafiya ɗan gidan giwar galadima jikar fulanin gombe, ayi mana izinin bata horon yadda ake girmama wannan suna”.

Adam ya girgiza kai, tare da ɗaga musu hannu, ɗan risuna masa suka yi, sannan suka nufi sashin turaki, dan neman iznin shiga wurinsa.

Rumaisa ta ce “Yau na ga masifa, to naga annabawa ma ana faɗar sunansu, sai sunan wani mutum gama gari ace ba za’a faɗa ba, taɓ kun haɗu da wahala, wai wani ƴar talakawa sai ka ce su masu kuɗi ne”.

Usman ya ce “Dan Allah maiyasa ba ka saka sun ɗagata sun zaneta da bulala ba? Wataƙila a samu hankali ya shigeta”.

“Yaya usy ai ni yanzu na wuce duka yasin, sai dukan ruwa bari na je na gaya wa baba mai rawani ka ce ba zaka zo ba” ta wuce ta koma wurin turakar turaki.

Dogaran nan ta tarar a tsaye, suna jiran iso, amma ta zo ta saka kai zata shige.

“Ke! Ke hattara dai, tsaya a nan ina zaki ba ayi miki iso ba?” Ai ba ta ko tsaya ba, ta daka tsalle ta shige da gudu, ta tsaya tana jiran ko zasu biyota.

“Wallahi tura ta kai bango, abubuwan da ka ke aikatawa sun isa haka, kai ko kunya ma ba ka ji? Ka mayar da ‘ya’yanka ba komai ba, sai guda ɗaya shiyasa Allah ya kasheta a wulaƙance, saboda zaluntar ‘ya’yanka da kake yi, kuma idan ba ka yi wasa ba, kuma ba ka nemi afuwar yaranka ba, kaima a yadda ta mutu haka za ka mutu.
Ka binne wa mutane gaskiya, kun haɗa kai da giwa da ɗanta sai rainawa mutane hankali ku ke yi, tayaya za ace wannan yar yarinyar ce ta dawo da jariri, ta yaya aka tabattar ɗan aisha ne, wataƙila ma wani abun suka ƙulla, ya haihu da wata aka kashe aisha aka kawo yaron a matsayin nata, ba abun da ba zai iya faruwa ba, tun da dai ‘yar ka ce ba tawa ba, matsalar ku ce”

Turus rumaisa ta yi tana bin Hajiya saudat da ido, ta gama zubarta, ta nufo hanyar fita, cikin tsawa ta cewa rumaisa “Ke kuma ban hanya ko na yi gaba da ke” maimakon rumaisa ta matsa, sai ta tsaya tana ƙarewa ƙwayar idon mama kallo, ba tare da tsoro ko shakka ba.

Babu tsammani, rumaisa ta ji an ja ta gefe, an bar hanyar da mama zata wuce.
Hajiya sauda ta yi wa adam wani mugun kallo, ta fice. Rumaisa ta ƙwace hannunta, ta ƙarasa gaban turaki ta ce “Baba, mai ya sa ka tsaya matar nan take maka masifa, kai ba sarki bane ba? Ai ba a ɗagawa sarki murya in ji mama, haka ta ce mini kan mu zo nan”

Turaki ya ce “Yarinyar kirki, sarki a waje yake sarki, amma wani sarkin a gida bawa ya fishi power, kar ki damu zaki gane me nake nufi ” ya kalli Adam ya ce “Takawa, Biliyaminu nan sun kawo saƙon ‘ya ta, ba sai sun ganni ba, na ta ne a kai mini ita har gida, Allah ya yi miki albarka”.

Rumaisa ta ce “To baba dan Allah ka saka baki ya bani ɗana sabir, kaga na gaya maka anty aisha ta bar mini shi wallahi, amma ya ƙwace mini shi, kar na kai shi kotu ne a ga kamar ban kyauta ba, kuma ina ganin girmanku kai da mamansa, amma da wallahi nima kotu zan kai shi wurin alƙali, wata a unguwarmu ta taɓa bawa mama labari wai a kotu an ƙwato mata ɗan ta daga wurin mijinta an bata”

Turaki ya girgiza kai tare da murmushi ya ce “Subhanallah, ba za ayi haka ba, ai mu yanzu mun zama ‘yan uwa, za a duba lamarin in sha Allah, saƙonki yana mota Allah ya tsare”.

Rumaisa ta miƙe tsaye ta ce “To na gode sosai Allah ya saka da alkhairi, Allah ya biya maka buƙatunka na alkhairi Allah ya sa ka zama sarki, ka zama shugaban ƙasa baba”
Sunkuyar da kai turaki yayi, yana rife fuskarsa da rawani, dan sha’anin na rumaisa ba ya ƙarewa.

“Wuce mu tafi ina da wurin zuwa” Adam yayi maganar a kausashe.

“Ai ko ba ka ce ba zan tafi, ba sai ka kaɗani kamar wata akuya ba” ta yi maganar tana ficewa waje.

Tun da ta fito usman ke cigaba da aika mata harara ko ta ina, amma ta yi kamar ba ta gani ba, haka suka fita suka hau motar takawa.

Suna tafe a hanya, babu wanda ya kula rumaisa a cikinsu, usman ya ce wa Adam “Ina ga idan muka ƙarasa titi ka ajiyemu, sai mu samu abun hawa mu ƙarasa gida”.

Adam ya girgiza kai ya ce “A’a zan kai ku gida, akwai kaya ma, ba zai yiwu in ajiyeku a hanya ba” daga haka suka ɗan shiga taɓa hira suka cigaba da tafiya.

Tafiyar su takawa babu daɗewa, Samha ta dawo, har ta shiga ɗakinta ta canza kaya ta fito, ba ta ga gilmawar mama ba, dan haka ta bita ɗaki.
Ta iske mama na ta ƙananun maganu, da mita.

“Mama, wai baki san na dawo ba? Ke da waye ki ke ta mita haka ne?”.

“Ba dole na yi mita ba, ubanku na nema ta ƙarfin tuwo ya mayar da ni mahaukaciya”.

“Ohh mama, kullum cikin case da Alhaji, yakamata ku daina zuwa yanzu”.

“Ke dalla rufe mini baki, mai za a fasa? Ai yanzu aka fara ma ba ayi komai ba, na rasa abun da yake shiryawa da shi da adam, sai ɓoye-ɓoye suke yi, da rainin hankali wata shu’umar ‘ya ya kawo masa, wai ita ta dawo ɗan wurin aisha daga hannun ‘yan bindiga”
Cikin rashin fahimta samha ta ce “Yan bindiga kuma, wasu ‘yan bindigar kenan kuma? Ba a can in da take karatun aka ce ta haihu ba? To meya kawo ƴan bindiga ban gane ba”.

Hajiya Sauda ta yi ajiyar zuciya ta ce “Ke, adam wani abun yake shiryawa, aisha ba wani a ƙasar da taje karatu da ta mutu, a hannun’yan bindiga, da suka yi garkuwa da ita, ta haihu ta mutu a wulaƙance ko gawarta ba wanda ya gani, waya sani ko shi ya cinyeta ko ya kashe ta yayi tsafi da gangar jikinta”.

Cikin rashin fahimta samha ta ce “Mama kin yi wa kwanyata dabaibayi da zantukkanki, na gaza fuskantar ko da guda daga ciki, ki yi mini bayani gwari-gwari. Ƴan bindiga ne suka bi ta can suka sace ko kuwa?”.

Nam mama ta fayyacewa samha komai, duk da gargaɗin da turaki yayi mata a kan hakan.

Salati samha ta yi, tare da tafa hannuwa cike da tsananin mamakin sarƙaƙiya da ruɗanin lamarin, a fili ta ce “Oho musu, ko ma dai yaya ne, a wannan karon nasan babu abun da zai hanani mallakar takawa”.

Sheƙeƙe mama ta kalleta ta ce “Wai ke samha wace irin mara zuciya ce ne?, Au ke yanzu duk abun da ya faru da ke a baya, da irin cin kashin da yayi miki baki haƙura da batunsa ba?”

“Dan Allah mama karki ce komai, wallahi ina son sa haryanzu kuma abun da ya faru, ya riga ya wuce, dan Allah kiyi haƙuri ki bani goyon baya a wannan karon na auri adam dan Allah”

“Kin ga tashi ki je, ina da abun yi yanzu”.

Samha ta haɗa hannayenta biyu cikin magiya ta ce “Please mama”.

“Na ji, amma jeki yanzu, ki bari na yi tunanina” Samha ta tashi ta bar ɗakin mama, tana ta nazari da zancen zuci a kan abun da maman ta gaya mata.

Nusaiba ce ke ta bawa iman labarin rumaisa, da abun da ya faru ɗazu da suka zo, zasu je gidan turaki.
Iman ta ce “Allah sarki, na ji ina son ta tun ban ganta ba, ai mu duk mai son waninmu muna son shi”.

Nusaiba ta ce “Ke kin ganta, wallahi yarinya ce sosai, dan ba ta kaimu ba ma ko kaɗan, na yi mamakin yadda ta iya tsira da sabir”.

Iman ta ce “Ai babu mamaki a cikin lamarin Ubangiji, babu abun da bau iya ba”.

“Gaskiya ne, amma wai ya maganar uncle J ne, kun kuma magana da shi?”

Haushi ne ya kama iman ta ce “Dan Allah ki rabu da ni da wani uncle J”

“Dole na yi miki maganarsa, ke ma kin san rasuwar nan ce ta hanashi cigaba da bibiyarki, ina son nema miki mafita ne, idan ya je ya biyo ta saman fa kamar yadda ya gaya miki?”

Iman ta ɗan yi jimmm sannan ta ce “Bakomai, Allah ya fishi, mu bar maganar nan sai wani lokacin*.

Lura da yanayin yadda iman ba ta son zancen, ya sanya Nusaiba jan bakin ta ta tsuke.

Rumaisa kuwa bayan kayan takaicin da ta turawa su usman, suna tafe a mota tana yi musu waƙe-waƙe, tayi wannan waƙar ta saki ta kama wata, gashi galibin waƙoƙin na indiya take yi, sam ba ta san ma me suke faɗa ba, kawai dai tana yi ne, kuma cikin ikon Allah daga usman har takawa ba wanda ya tanka mata har suka ƙarasa gidan rumaisa.

Usman ya kalli Adam ya ce “Mun gode ƙwarai da gaske Allah ya saka da alkhairi”.

Adam ya ce “Bakomai, ni ne da godiya ai”.

“Hmm ai Yakamata in ƙara ma da baka haƙuri, a kan abun da rumaisa ta yi, ka yi haƙuri dan Allah” Adam yayi Murmushin gefen baki ya ce “Kar ka damu, akwai saƙonta a mota amma, bari na buɗe booth ɗin”

Ruma buɗe motar tayi, ta ruga da gudu cikin gida tana kwaɗa sallama.

Kaya ne fal a booth ɗin Adam, da wanda ammi ta bawa rumaisa da wanda turaki ya bayar a bata.

Usman ya ɗauka ya yi wa Adam godiya suka yi sallama ya ce a gaida mama.

Ko da ya shiga gidan, rumaisan ya tarar har ta tuɓe kayanta tayi ɗai-ɗai wai ta gaji.

“Dan ubanki ni bawanki ne? Da zaki bar ni da kwaso miki kaya dan baki da kunya?” Shiru ta yi ba ta ce komai ba, ganin irin kallon da yake yi wa rumaisa ya sanya sanin cewa akwai abun da rumaisa ta yi.

“Usman, ya aka yi ne? Kun je ɗin?”

“Eh mun je, amma ba ta sauya zani ba, ta yi iya shegen na ta da ta saba”

Mama ta kalli rumaisa ta sake kallon usman ta ce “me ta yi?”

Nan ya gaya mata iskancin da ta din ga yi, mama ta girgiza kai ta ce “Wai rumaisa me bawan Allah nan yayi miki da ki ke yi masa wannan rashin mutuncin? Duk jan kunnen da na yi miki ba ki ji ba kenan?”

“Mama na faɗa komai fa”

Usman ya ce “To amma meye na cewa sai mun fita, a matsayin sa na mijinta yafi kowa buƙatar sanin meyafaru da ita”.

Mama ta ce “Meyasa baka kama mini ita ka zaneta ba”.

Ya ɗan ɗage kafaɗa ya ce “Ai kin san wasu lokutan sa’a ce da ita, daga zuwanmu ta dinga zuba tana yi wa dattijon shishshigi tana ce masa baba,  aikuwa ya dinga biye mata, saboda sakarci har da ci masa abinci a gabansa”

Huzaifa da yake banɗaki yana jin hirarsu, yana fitowa ya ce “Sai ka ce mayya daga zuwa baƙunta ki hau cin abinci”

Aikuwa ta ce “To zigazigi wutar maƙera, mai zuwa lahira da ƙoƙon dambu waya kasa da kai gwanin na iya”.

“Kin rufe mini baki ko sai na taushe shegen bakin naki”

“Wallahi mama ni ban ci abinci ba, wannan abun na kayan gara mai kamar kashin nan da suga shi kawai na ci”.

A fusace mama ta ce “Ni rufe mini baki, bera kawai” haka ta koma ta tura baki tare da jin haushin yadda kowa yake caccakarta.

Adam sai da ya fara biyawa yayi sallar la’asar, yana komawa mota ya tarar da missed calls ɗin Bashir.

Bin kiran yayi, bayan bashir ya ɗaga sun gaisa ya ce masa akwai issue, su haɗu a wani wurin cin abinci bayan sallar isha’i.
Adam ya amsa masa, ya yanke shawarar fara zuwa gida, kan lokacin sallar isha’i sai su haɗu da Bashir.

Ko da ya je gida, Ammi ta din ga tambayarsa yaya suka yi, da fari basarwa yayi, da ammi ta matsa ya gaya mata cewar rumaisa ba ta yi magana a gabansa ba sai da ya fita.

Ammi ta yi shiru ta ce “Wai ni anya Adam babu wani abu a tsakaninka sa yarinyar nan ƴar tsamar da ku ke ta yi yawa, ta rainaka da yawa”.

Ya girgiza kai ya ce “Ni ban santa ba sai a dalilin abun nan da ya faru, dan haka ni babu komai a tsakanina da ita”

“To, amma ina kyautata zaton akwai wani abu mai muhimmanci a bakinta, tun da taƙi faɗa a gabanka”.

“Haka nake tunani nima, amma zan koma wurin turaki, sai mu yi magana”.

“To shikenan, Allah ya yi jagora”

Ya amsa da amin.

Kamar yadda suka shirya, suka haɗu da Bashir a wurin cin abinci, ya tambayi adam mai za a kawo masa ya ce ba ya jin yunwa.
Bashir ya ce “A’a ba zai yiwu ba, sai ka ci abinci ko na koma da labarin da na zo da shi”.

Da ƙyar adam ya yarda a kawo masa chips, bashir ya din ga yi masa hira, tare da gaya masa ya kusa komawa abuja wurin aiki.
Adam dai bai iya tankawa ba, jira yake kawai ya ji me Bashir zai ce masa.

“Wai ni kuwa ya ake ciki da maganar binciken da ka ke yi ne, na mutanen nan mutane hukuma fa suke jira, su ji sakamakon binciken ku, gashi wa’adin da kwamitin da gwamnati ta kafa ya cika ya wuce, amma ba su ce komai ba, kaima kuma kun yi shiru.

Adam yayi ajiyar zuciya ya ce “Bashir, sawun giwa ya take na raƙumi ai, ƙasar da ba ta damu da halin da al’ummarta suke ciki ba, tayaya zan cigaba da wahalar da kaina, a hukumar tamu ma kana gani sun rabu biyu, wasu suna goyan bayanmu wasu ba sa yi, a ƙasa kuwa talakawa ne kawai suke supporting ɗinmu. Ni yanzu hankalina yafi karkata ga binciko wanda suke da hannu wurin sace matata, dan a jikina nake jin na jikina ne”.

“Kenan kana nufin zaka fito ka cewa duniya sace matarka aka yi, bayan an gama jita-jitar a ƙasar waje ta zo haihuwa ta mutu?”

“Bashir dole hakan zan yi mana, ba zan bar mutuwar aisha ta tafi a banza ba, ko da haka yana nufin zubewar kimata ne a idon duniya”.

Bashir ya jinjina kai, ya saka hannu a aljihunsa, ya ciro naira ya ɗan daddana sannan ya miƙawa adam.

Adam ya karɓa ya fara dubawa, shafin wata jarida mai suna ciki da gaskiya ya buɗe masa.
Yana shiga ya ci karo da hotonsa, tittle ɗin labarin aka rubuta dara ta ci gida.
Shahararren jami’in tsaron nan na farin kaya, mai jagorantar wata tawaga da ta zama babbar barazana ga manya ɓarayin ƙasarmu, ko kuma dai ace, shugabannin da yake yi wa sharrin sata, wato Adam Sharif Galadima. Kwanaki kaɗan bayan kamala zaman makokin mutuwar mai ɗakinsa, An bankaɗo wani babban al’amari game da shi, in da lamarin mutuwar matarsa ya sha ban-ban da abun da aka sanar game da rasuwar ta ta, ashe ƴan bindiga ne suka yi garkuwa da mai ɗakinsa, har ta haihu a hannunsu, daga ƙarshe ta rasa ranta.
A wata majiyar kuma, aka ce da sanya hannunsa a yin garkuwa da matar ta sa in da ya kasheta yayi tsafi da gangar jikinta, kwatsam wata yarinya ta zo da jariri a zuwan ɗan matarsa ne, duk dan a ɓatar da hankalin mutane, da tunaninsu daga kan zargin shi wannan zaƙaƙurin bawa da yake jin cewa ya fi kowa gaskiya da adalci, masu bibiyarmu ko menene ra’ayinku game da wannan labari?!

Hannun adam har rawa yake yi a lokacin da ya kammala karanta labarin, wani irin wahalallen gumi ya din ga tsatstsafo masa, ya aka yi maganar nan ta fita? Waye ya yi masa wannan yankan bayan?.
Jiki na rawa ya ajiye wayar, ya miƙe tsaye, jin kansa ya fara sarawa, yana neman rasa nustuwarsa, bashir ya tashi zai yi masa magana, amma tuni adam ya sulale ya bar wurin.

Kafin ya cimmasa, ya hau motarsa yayu mata key, ya fice daga restaurant ɗin da gudu.

Back to top button