Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 6

Sponsored Links

P6

Iya ƙarfinta take ihu, tana kiciniyar sai ya sauketa, amma yayi burus da ita, sai da ya je soron gida, sannan ya sauketa ya ja hannunta zuwa cikin gidan.

Aliyu ne a tsakar gida yana yiwa mama wanki, ya ɗago ya kallesu ya ce “Ya dai, ya kake jan ta tana ihu, makarantar fa?”

Hauzaifa bai amsa masa ya tambaye shi”Mama tana nan?”

“Eh tana nan” Aliyu ya bashi amsa.

Jin ihun ruma ne ya sanya mama katse sallar walahar da take yi, ta fito tana tambayar lafiya.
Hakan yayi dai-dai da fitowar Yaya Umar, shi ma ya yi shirin fita. Duk suka zubo musu ido suna jiran jin ba’asi.

“Mama wallahi yarinyar nan ba ta da mutunci, daga sakata a makarantar nan ta fara tayar mana da hankali, yaushe yarinyar take da sikila ban sani ba?”.

Mama ta ɗan yi sororo ta ce “Wace irin sikila kuma?”

“To haka ta je ta ce wai sikila ce da ita, ta tashi tsaye ma ta ƙi sai a bayana na goyota”

Yaya Umar ya kalleta ya ce “Ke meya sameki?”

Cikin in da in da ta ce “Dukana aka yi, kuma wallahi na ji zafi sosai shi ne na ce musu sikila ce da ni, na ga wata ‘yar makarantar bokonmu ba a dukanta saboda sikila ce ita”.

“Shi ne ki ke yiwa kan ki fatan ciwo saboda baki da hankali, ke dama za a zauna da ke baki yi abin da za a dake ki bane ba, me ki ka yi aka dake ki?” Yayi maganar cikin tsare gida.

Cikin kuka ta ɗage ƙafar wandonta, shatin bulala ya kwanta a kan fatarta, ta kalli mama ta ce “Mama kin ga fa, dan Allah a cireni wallahi ni ba zan iya makarantar nan ba, wai ban iya karatu ba shi ne aka yi mini wannan dukan, ni wallahi ba zan iya karatun nan ba, ga duka ga karatu mai yawa, da wanne zan ji?”

Cikin tsawa Yaya Umar ya ce “Wuce mu je makarantar, sai kin ci ubanki yau, ai dama karatu aka turaki ba wasa ba”
A karo na farko ta yi wa yaya Umar gardama tana kuka, ta riƙe hannun Huzaifa, ta ɓuya a bayansa.

“Ni nake miki magana ki ke ɓuya a bayansa, ba zaki fito ki wuce ba”

“Dan girman Allah kayi haƙuri, wallahi idan suka san ƙarya nake, sai sun kusa kashe ni, wallahi duka ake na tashin hankali a makarantar nan” kuka take wiwi kamar wadda aka yiwa mutuwa, mama dai ta kasa magana.
Huzaifa kuwa janyota ya yi daga bayansa, ya ce Wallahi ba zai kareta ba sai dai ayi mata duk abin da za ayi mata.

Yaya Sadik ne ya fito daga ɗakinsu, yana zuwa ya ture Umar, ya kamo hannun Rumaisa, ya wuce da ita ɗakin su.

Suna shiga ya zaunar da ita, shima ya zauna ya ɗan ƙura mata ido sannan ya ce “Auta, meke damunki ne, kullum sai an yi rigima dake an ce ba kya ji, ke ko haushi ba kya ji?”

Ta girgiza kai ta ce “Wallahi ina jin haushin yadda aka tsane ni kullum ace bana ji”

“To yanzu meyafaru, har aka dake ki ki ke cewa sikila ce dake? Kin san sikila kuwa meyasa ki ke fatan wannan ciwon?”

“Gani nayi za a kashe ni da duka, ni bana son a dake ni”.

“Gaskiya ba ka kyautawa, dan me yarinya za ta yi laifi ka hana a hukunta ta, me kake ƙoƙarin koya mata ne?” Umar yayi maganar a mugun fusace.

Yaya Sadik ya waiwayo ya kalli Hussainin na sa, ya haɗa hannayensa alamar ban haƙuri ya ce “Tuba muke, zan wa tufkar hanci in sha Allah, on behalf of her, ayi haƙuri gobe in Allah ya kaimu da kaina zan mayar da ita makarantar in basu haƙuri” gajeren tsaki Umar yayi yai waje, babu wanda yake masa katsalandan kamar yadda Abubakar yake yi masa, ya fuskanci idan aka biyewa Yayan nasa ruma tsiyarta zata tsula ba tare da an kwaɓeta ba, da tayi laifi sai ya ce ƙuruciya ce.

Wunin ranar kowa share ruma yayi, yaya Sadik ne kawai yake kulata, Huzaifa da yasir suka ƙare mata zagi tsaf suka tsangwameta.
Ko a jikinta, tun da Allah ya sa ba a mayar da ita makarantar an ce ƙarya take ba, hankalinta ya kwanta.
Washegari Yaya Abubakar da kansa ya rakata makarantar, aka dinga yi mata sannu ana mata ya jiki, ta basar ta dinga amsawa.

************

Sanye yake da fararen kaya ƙal, fuskarsa sanye da fari siririn glashi, taku yake cike da ƙasaita ya biyo wata doguwar baranda.
Sannu a hankali ya ƙarasa gaban wata ƙatuwar ƙofa, ya sa hannu ya murɗata a hankali. A take ta buɗe wani sassanyan ƙamshi ya daki hancinsa.
Da sallama ya shiga ya mayar da ƙofar ya kulle, babu kowa a falon sai wata matashiyar budurwa tana saka turaren wuta.
Amsa masa tayi tare da faɗin “Sannu da zuwa”.

“Yauwwa ‘yar aikin Ammi, ina ma’aikatan ne ki ke aikin da kan ki?”

Ta ɗan kalle shi sannan ta ce “Nima ‘yar aikin ce ai” yayi murmushi ya ce “Sorry idan haushi ki ka ji, ina Ammi?”.

“Bacci take” ta bashi amsa lokacin da take cigaba da saka turaren wuta.

“Ba kowa kenan?”
Cikin ƙosawa da tambayoyinsa ta ce “Duk sun tafi makaranta”.

“Ke me ya hana ki je makarantar?”

“Ohh God, uncle J am sick shi ya sa ban je ba, Ammi idan kana son ganinta ka dawo an jima, ina fatan zan iya tafiya na gama amsa tambayoyin ka?”

Ya girgiza kai ya ce “No, saura ɗaya ina yayan ku?”

Tayi murmushi ta ce”Wannan tambayar ai kai yakamata a yiwa, i don’t know ” daga haka ta bi wata hanya ta bar falon.

Ya girgiza kai a hankali ya ce “Wannan yarinyar ta fi mai kora shafawa, izzarki tayi yawa”
Wayarsa ce ta fara ringing, ya zura hannu a aljihunsa ya ciro wayar.

“Ke nifa kin isheni, ni kaina ban san in da yake ba, anjima kuma kilisa zan fita, zan neme ki amma” daga haka ya kashe wayar, ya saka a aljihunsa ya fice.

*********
Ruma ta sha kashedi a wurin su Huzaifa, a kan ta shiga hankalinta a makarantar nan, dan ba ƙaramin girmansu ake gani ba, halinta ba zai sa mutuncinsu ya zube ba.
Ta cigaba da zuwa makaranta, amma ba ta gane komai, idan Yasir ya zaunar da ita zai koya mata kuma, sai ta ce ita ta gaji ba ta so.

Ranar wata juma’a da yamma, Abdallah yana ta haɗa kayan miya, za a kai markaɗe, Yasir ya kalleshi ya ce “Abdallah kyanta na ɗau hotonka kana haɗa kayan miyar nan, na je na nunawa yarinyar nan mai awara”.

Haɗe rai Abdallah ya yi ya ce “A’a mai wake zaka nunawa ba mai awara ba”

Yasir ya yi dariya ya ce “Zaka ga mai wake, wallahi yarinyar nan ta mato a kan ka, kawai ka nutsu ku daidaita, wallahi shar da kai awararka zaka yi ta ci”

“Na rantse idan ba ka yi mini shiru ba sai na ɓarar da kai”

Yasir ya ce “Yaya ba zan ƙoƙari na tayata kafa gwamnatin ta ba, kullum sai ta kyauta mini”.

Buut Ruma ta fito daga ɗaki ta ce “Yasir yakamata muje ka gabatar mata da ni, na dinga biyawa idan zan je makaranta”.

Tsaki Yasir ya yi “To munafuka waye ya sako dake, na zaci ma bacci take wallahi ”

Abdallah ya ce “Wallahi ko da wasa ki ka je, sai na kakkarya ki”.

“To ni ce maka ma nayi zan je?”

“Ke dai ki ka sani gulayya” Yasir yayi maganar yana hararta.

“Wallahi ni ba gulayya ba ce” shareta suka yi suka cigaba da hirarsu, yayin da Ruma ta koma gefe tana naɗar abin da suke faɗa.

Kamar yadda a islamiyya ruma ba wani ja take ba, haka ma makarantar boko ba uwar da take ganewa sai wasa.
Ta na cikin top 10 na marasa ganewa a aji, sannan ta farko a sahun marasa ji.
Yau bayan an taso daga makarantar boko, ta biyo ta hanyar da lambun mai unguwa yake. Ƙaton lambu ne da ya kasance mallakin wani a babba masarautar Kano, wanda yake ƙarƙashin kulawar mai unguwa, ba kowa ya san da hakan ba sai ɗaiɗaikun mutane.
Gaba ɗaya hanyar ba ta cikin jerin hanyoyin da zata bi su sada ta da gida, amma tun da ta ji ‘yan ajinsu suna labarin mangwaron lambun ya fito yayi kyau, tayi alwashin bi ta hanyar dan ganewa idonta abin da suka gaya mata.
Aikuwa babu ƙarya, lambun ƙato ne na gaske, wani wurin an kewaye shi da katangar bulo, wanu wurin kuma aka ƙarasa kewaye shi da waya.
Akwai bishiyoyi kala-kala a ciki, wasu duk sun yi ‘ya’ya kasancewar lokaci ne na damuna.
Mangwaron nan yayi ‘ya’ya sosai gwanin ban sha’awa.
Ƙatuwar ƙofar shiga wurin ta gani, babu kowa a wurin, dan haka kai tsaye ta kutsa a gaban wata ƙatuwar bishiyar mangwaro ta tsaya, yanayin wurin yayi mata kyau sosai da sosai.

Ta samu dutse, ta dinga jifan bishiyar, suna faɗowa tana ɗiba, ta tara ta cika jakarta, sannan ta nufo hanyar fitowa.
Tana fitowa wani matashi yayi caraf ya danƙeta yana faɗin “Alhamdilillah, shegiya ɓarauniya ashe ku ne masu shiga lambun nan suna ƙurguma mana sata”.

“Ban gane ba wace iri ɓarauniya me nayi maka?”

“Zaki ga me ki ka yi mini, gidan mai unguwa zan kai ki, ke saboda ƙwarewa ma, da ki ka sata sai ki ka biyo ta ƙofa zaki fita, kina ‘ya mace kina sata”

Cikin rashin kunya Ruma ta ce “Wallahi ni ba ɓarauniya bace ba, ta ƙofar nan fa na shiga, ba wanda ya haura gida ne ɓarawo ba?”

“To da ki ka bi ta ƙofar, wa ki ka tambaya ki ka shiga ki ka ɗebo abibda ba naki ba?”

“A’a, to ni wa na gani a wurin, kuma ma naga ai bishiyar ta Allah ce, Allah ne ya fito da ita, kuma sai ace sai an tambayi wani sannan za a ɗau abin da Allah ne ya fito da shi, kai iskar da ka ke shaƙa wa ka tambaya ka ke shaƙarta?” Saroro ya bi ruma da kallo, wata ‘yar cukul da ita sai shegen surutun tsiya.

“Zaki yi bayani, sai na kai ki gaban mai unguwa”

“Daɗinta shi mai unguwar ba shi da wutar da zai sakani, kuma duk in da za a je ai bishiyar Allah ce, kuma ka sakar mini hijjabi dan ni ba ‘yar iska bace ba.
Bai ko saurareta ba, ya figi hijjabinta ya fara janta.
“Ka dai na ja na haka kamar wata akuya, ba ƙaramin aikina bane na cire maka hijjabin nan na ƙara gaba.

 

Mama sai kallon agogo take yi, tana kallon hanyar shigowa, amma babu ruma babu alamunta.
Tsakar gida ta fito tana kiran Usman, kasancewar shikaɗai ne a gidan, ya dawo da wuri bashi da lectures.
“Ka ga haryanzu yarinyar nan shiru ba ta dawo ba”

Usman Ya ce “wataƙila tana can tana rashin hankali a titi da ƙawayenta, amma maybe ki ganta yanzu”.

“A’a zunnuraini, shi biyu da rabi fa take dawowa amma kalli yanzu ƙarfe ɗaya da rabi, hankalina ya kasa kwanciya”
Ya ɗan yi shiru sannan ya ce “Kuma fa kamar ma ga ‘yan makarantar su lokacin da nake hanyar dawowa, amma bari na je makarantar ta su” yana rufe bakinsa, suka ji ana ƙwala sallama a waje.

Usman ya amsa, ya nufi ƙofar gidan, aikuwa yana zuwa ya tarar da an riƙo ruma, tana rungume da jakar makarantar ta, sai kumbura baki take, tana cika tana batsewa.

Kallon matashin saurayin yayi, ya ce “Bawan Allah lafiya, ya zaka riƙo yarinya haka kamar ka riƙo ɓarauniya?”

Matashin ya ce “To kusan hakan ne, karɓi jakarta ka duba ka gani”

“Ka saketa mana” yayi maganar a fusace yana fincike hannun matashin daga hijjabinta.
“Me tayi maka haka?”.

“Nan matashin ya kwashe komai ya gayawa Usman”

“Wallahi ni ba ɓarauniya bace ba, tun da ta ƙofar wurin na shiga kuma ban ga kowa ba, ai ba haurawa na yi ba”

Usman ya fizgi jakar ruma, ya buɗe ya ga mangwaro ya kai takwas a ciki manya, nunannu da ɗanyu, sai goba guda huɗu.

Ya kalli ruma, sannan ya kalli matashin ya ce “Yanzu kai a kan wannan zaka danƙota ka keto layi da ita haka? Ka taɓa kamata ta shiga ta ɗaukar muku abu ne?”

Matashin ya ce “Ban taɓa kamata ba, amma ana haura mana, ayi sata”

“To kuma sai aka ce maka nice nake yi, ni wallahi ban taɓa shiga ba sai yau”.

Usman ya zura hannu a aljihunsa, ya ɗauko dubu ɗaya, ya miƙawa matashin ya ce “Na san dai abin da ta ɗauka, bai kai na hakan ba, gashi nan na biya, kuma kar ka sake kiranta ɓarauniya Please, ba halinta bane ba ba ta taɓa yi ba, dan ka ci sa’a da na biyewa zuciya sai na kifar da kai, saboda yadda ka riƙo mata hijjabi, ka keto unguwa da ita, saboda ɗanyen mangwaro”
Yana gama maganar, ya ingiza ƙeyar ruma zuwa cikin gidan, suna shiga gidan ya danƙota ya ƙwace jakarta, ya durƙusar da ita ya ce “Oya tsallen kwaɗo maza”

Waiwayo ruma tayi, ta kalleshi cikin mamaki, amma taga babu alamar wasa a tare da shi, cikin tsawa ya kuma cewa tayi tsallen kwaɗo.

Mama ta fito tana faɗin “Lafiya, me aka ce tayi, sallamar da ake kenan?”

Usman ya ce “Ƙyaleni da ita mama” nan ruma ta kama tsallen kwanɗo.

Duk yadda mama tayi a kan Usman ya gaya mata me aka ce ruman tayi, amma yaƙi, sai dai ruma ta ci ƙwal ubanta, dan ko miƙewa kasa wa tayi.

Duk yadda mama ta kaɗa ta raya, amma bai gaya mata ba, kuma babu wanda ya gayawa abin da ta aikata.

****
Islamiyyar su ruma, sanya mata ido suka yi, dan ba ta iya karatu balle kawo hadda, ko karatun aka zo sai dai a tsallake ta, dan ba iyawa take yi ba.
Malamin ajin ko sabgarta ba ya shiga, tun daga ranar da ya dake ta ta ce ita sikila ce. Yau dai ya kasa jurewa yace mata “Wai ke ba kya jin haushi yadda ‘yan ajin ku suke karatu, amma ke ba kya iya wa?”

“To malam karatun yayi mini yawa, yaya zan yi?”

“Su sauran da suke iyawa, da me suka fiki?”

Ita kanta ruma gaba ɗaya malamin bai yi mata ba, dan bai fi sa’an Abdallah ba, shi ma ɗalibi ne a makarantar, amma ya dinga takura mata.
Tayi masa banza tana kallon wani gefen daban.
“Magana fa nake miki?”

“To ya sayyadi me zance maka? Ni wallahi ba zan iya karatun nan ba, ni fa tun farko ba son makarantar nake ba, kawai dan yayana ya kawo ni ne”.

Ita gaba ɗaya kanta tsaye take faɗar magana, ko tayi maka daɗi ko kar ta yi maka kai ta shafa.

Tsaki yayi ya ce “Daƙiƙiya mara zuciya”

Ɗagowa tayi ta kalleshi ta ce “Malam wannan ba halin musulmi nagari bane ba, ba koyarwar addinin Musulunci bace. Saboda bana iya karatu dama duk ka bi ka tsaneni Allah ya buɗa mini ƙwaƙwalwata nima. Zuwa zan yi a canza mini aji” ta tashi ta ɗau jakarta ta bar ajin, ba tare da ko izini ta nema ba.

Ta bala’in jin haushin cin mutuncin da ya yi mata a gaban ‘yan ajinsu, wai daƙiƙiya mara zuciya.
Ofishin shugaban makarantar ta nufa, dan ta sanar masa a canza mata aji, malaminsu ya tsaneta, amma ta tarar baya nan.
Azuzuwa ta shiga dubawa, aikuwa ta ganshi a ajin su Yasir yana yi musu karatu.

A ƙofar ajin ta tsaya ta ce “Headmaster ina wuni?”

Ya ɗago ya kalleta, ba wanda yake ce masa wani head master sai yau a bakinta.

Ya ce “Lafiya lau”

“Malam zuwa na yi ka canza mini aji, ni na gajj da ajin nan, malamin ya tsaneni”

Dariya ‘yan ajin suka fara yi, Yasir kuwa ya sunkuyar da kai ƙasa.

Yayi murmushi ya ce “To shikenan, ki je ki jirani, idan an tashi sai mu yi magana”

“To, Yasir in jiraka idan an tashi mu tafi tare?”

Wani mugun kallo ya yi mata ya ce “Da tare muka zo”

Murguɗa baki tayi, ta koma kan barandar ajin ta zauna, shiru-shiru ta gaji basu tashi ba, ta kaɗa kai tayi tafiyarta gida.

A hanya ta biyo ta filin ball ɗin su Yaya Aliyu, maza sun yi cincirindo, ana kallon ball, ta tsaya tana leƙawa ko zata hango yaya Aliyu.
Kutsawa ta dinga yi, sai gata ita ɗaya a cikin maza.

“Ruma me ki ke yi a nan?” Ta ɗaga kai ta kalli mai maganar, abokin Aliyu ne.

“Yaya Aliyu nake nema”

“To ai yana cikin fili, ball yake”

“To ai na sani, kallonsa zan yi”

Ya jinjina kai ya ce “To ai shikenan”

Kamar daga sama ya ji ana kiran sunansa, da ‘yar siriryar muryarta.

Duk da yadda ya taso ball ɗin a gaba, amma sai da ya tsaya ya waiwaya.
Ruma ya hango a gaban garada, tana ɗago masa hannu.

Waro ido ya yi, ya nufi in da ruma take.
Coach ɗin su Aliyu ya fara masifa, dan ajiye ball ɗin da ya yi, ya waiwaya aka ci su ɗaya.

“Ke me ki ke yi a nan?”

“Wucewa zan na ce bari na zo na ganka”
Ya dafe kai ya ce “Innalillahi wa Innalillahi raji’un, ki wuce ki tafi gida”

“Dan Allah ka bari na gani”

Hankalinsa na kan ruma, coach kuma na ta masifa.
“Kai dalla wacece wannan, ku koreta daga wurin nan”.
“Wallahi ba inda zani, ai wurin yayana na zo”.
Aliyu ya kalli abokinsa ya cewa “Aminu, dan Allah jire mini yarinyar nan” ya koma cikin filin yana waiwayenta.

Aminu ya bata wata ƙatuwar jaka ta zauna a kai, ita kaɗai mace a cikin maza.

Yana ball ɗin amma hankalinsa yana kanta.

Ta dinga yi masa tafi tana bashi ƙwarin gwiwa, kusan duk hankali ya dawo kanta, gaba ɗaya ta bawa wasu dariya a wurin.

Da yaya Aliyu ya ci ball kuwa, ta dinga tsalle tana murna, ya ci ball biyu.

Da aka tashi har hoto aka yi mata, ita da Aliyu ta riƙe kofin da suka ci, kasancewar ball ce ta cikin unguwa.

Ba a tashi daga ball ɗin ba, sai ana kiran sallar magariba, mama tana can ta sa an yi sahu ya kai uku a makarantar su, ana nemanta.

Suna tafe a hanya tana yabawa yaya Aliyu, abokansa sai tsokanarsa suke yi a kan ruma.

“Yaya Aliyu, akwai wani wanda kuna ball ɗin, ya dakar maka ƙafa, na ji haushi idan na ganshi sai na buga masa dutse wallahi”.

“Ni ban saki ba, kuma baki ga an bamu pk ba da ref ya gani”

“Oho ni na san wani pk, amma da ka tsaya ja masa duka ka rama, daga wasa sai cin zali”

Haka suka ƙarasa gida, mama na tsaye da carbi a tsakar gida, tana tunanin ta ina ruma zata dawo.

Sai gata ita da Aliyu, yana riƙe da hannunta.

Mama ta kalleta ta ce “Ke daga ina?”
Sai a yanzu ta tuna daga islamiyya ko gida ba ta zo ba, ta kalli ya ya Aliyu ya kalleta.

“A ina ka ganta?” Mama ta tambaye shi tana kallon ruma.

Aliyu ya ce “wallahi mama nima kawai ganinta na yi a filinmu, ban san ina za ta tsaya ba idan na ce ta taho, shi ya sanya na ce ta tsaya”

“Kina mace uban me ya kai ki filin ball?” Huzaifa yayi maganar a ƙufiule, dan takalminsa har tsinkewa ya yi saboda nemanta.

Hararsa tayi ta sake noƙewa a jikin Aliyu.

Duka Huzaifa ya kawo mata, Aliyu ya tare ta, ya ce laifina ne duk Allah ya baku haƙuri.

Mama ta fara tunanin anya ba zata kai ruma wurin malaman ruƙiyya ba, abin na ta ya fara bawa mama tsoro sosai da sosai.

Kamar yadda ruma ta saba kwatsa zance, bayan kowa ya halarra, haka yau ma sai da kowa ya halarran, an gama cin abinci sannan ta gyara murya ta ce “Yasir, wai yaushe ku gama karatun ɗazu da naje ajinku”.

“Ban sani ba” ya bata amsa.

“Mhmm ai dama ba zaka sani ba, nifa gaba ɗaya mutuncin malamin nan ya zube a idona, wallahi mama idan kin ji me yake gaya musu sai kin riƙe baki, duk da wani abun bana ganewa, duk basu san daga waje ina jiyowa ba, kuma maimakon Yasir ya fito daga ajin nan, amma ina yana zaune ana koya musu abin da bai kamata ba.

Saroro yasir ya yi, ya ji me aka koya musu da bai kamata ba, suna haɗa ido da ruma, ya tuna karatun da aka yi musu, kan ya kai ga ɗaukar mataki ta ce “Ina ji ai yana ce muku, wai ko idan mutum ya rungume mace alwalarsa ba ta karye ba, ko kiss, dan Allah wannan mama ba iskanci bane da ɓata tarbiyya, nan idan muna kallo aka nuno kiss ɗauke tashar ake yi, amma wai malaminsu yake gaya musu.
Kuma naga ai turawa ne kawai suke rungume-rungume da kiss, mu wannan ba ɗabi’ar mu ba ce amma yake gaya musu, wallahi makarantar nan ɓata tarbiyya ake yi”.

“DANƘARI!!”

Back to top button