Hausa NovelsMatan Ko Mazan Book 1

Matan Ko Mazan Book 1 Page 7

Sponsored Links

EPISODE 7️⃣
THIS PAGE IS FOR YOU ZEE, MY NUMBER 1 MOTIVATOR, I LOVE YOU❤️❤️
Saukan tambayanshi Ummi taji kaman daga sama saikuma takai hannunta ta taba kirjinta daya buga, to kodai sabida yanda taketa tunaninshi tun jiya yasa taji kaman yace mata zata aureshi? Ta tambayi kanta, me Alhaji zaiyi da itama in banda shirmen tunainta hakan yasa tace “na’am banji abinda kace ba Alhaji?” Ijiyan zuciya Nura ya sauke wlh yadade baiji murya mai dadi kaman na yarinyar nan ba komi nata sanyaya mai zuciya yake, the feelings he’s developing for her is growing a fastest rate, cikin taushashiyar murya dake kashewa mace zuciya yace “ina sonki da aure Ummi zaki aure ni?” Yanda gaban Ummi ke bugawa saida tacire wayan dasauri daga kunninta takifa shi kan cinyanta tadaura duka hannayen ta biyu kan wayan ta runtse idanunta tana breathing so fast this is unbelievable, yasan tana sonshi ne? Yasan tana tunaninshi ne? Ta tambayi kanta takai almost minti daya sannan tamaida wayan kunneta daidai Nura nacewa bakice komiba, itama wlh bala’in nauyi da kunya takeji tace ta yarda haba saikace jira take, kaman yana magana da little Amal yace “Ummimy” yanda yakira sunanta har cikin jinin jikinta taji itama anarke tace “Na’am” cikeda so da bege Nura yace “ataimaka abawa Alhaji amsa eh Hajiya Ummi na” rufe fuskanta tayi dasauri akuma kunyace, murmushi yadan subuce daga bakinta da yaji karan kadan hakan yasa yayi murmushi yace “Ina jinki” Abala’in kunyace tarufe fuskanta da hannu daya tarike waya da dayan hannun akunnenta tace “idan munje kauyen mu ka tambayi Gwaggo na” murmushi yamata shi babba ne this amsan kadai ya wadatar da curiosity dinshi yace “okay yanzu kije kiyi sallama da matan gidan kice mata zakije kauyenku gobe an kiraki daga gida, kada ki fada mata wani abu bayan haka kinji” gyadamai kai tayi tace “toh” dan ijiyan zuciya yasauke kaman kada yayi sallama da ita yace “tom saina dawo” akunyace still tace “mezan dafa maka”? Cikin kashe murya yace “nabarwa Hajiya Ummi zabi” dasauri ta cire wayan daga kunnenta takashe sai murmushi take, amsanshi melt zuciyanta, wai itadai Alhaji keso ya aura ikon Allah, takai awa daya awajen zancen zuci take ita kadai sannan ta tashi tawuce sama sallama da knocking tayi gaban dakin Hadiza akace shigo bude kofa tayi ta shiga Hadiza na kwance kan gado da babban IPad dinta na apple tana kallon cctv footage na shagonta yanda yau takasa zuwa shagon dan batada karfin zuwa dukawa Ummi tayi tace “sannu da hutawa Anty” kallo daya Hadiza tamata tadauke kai tace “lafiya?” Kan Ummi na kasa tace “Anty tafiya takamani kauyen mu gobe!” Dasauri Hadiza ta yunkuro ta kalleta hakan yasa Ummi tace “Gwaggo na batada lpy tace tanason ta gani maza maza” wani kalan harara Hadiza tamata tama kasa magana to idan ta tafi yaya zatayi da yaran nan gashi kafin su sami wata yar aiki dazasu saba da ita sai an wahala, cikeda asalin rashin son ta tafi tace “inhar kinsa kafa kinbar gidan nan da sunan tafiya to kisani na sallameki daga aikin nan kinajina”? Gyadamata kai Ummi tayi ahankali tace “toh” tsaki Hadiza taja danta dauka she will start begging her tace tafasa tafiyar, rai abace tace “sabida dan rashin lafiya ne yanzu harsai anwani kiraki kinbar aikin ki dake ciyar dasu kinje kauye? yanzu ma tukunna kwana nawa zakiyi idan kinje? Kan Ummi na kasa tace “sati daya ko biyu hala” Hadiza jitayi ranta yabaci datana da wani power da wlh saita hana tafiyan nan cus yaranta zasu shiga wani hali yazatayi dasu yanzu? Ga agency nan kokai requesting yan aiki unless akwai akasa shine zaka samu fast Inba hakaba sai an kawo, tsakin takaici takaraja tace “tashi kifita ki tabbatar dai goben kin shirya yaran nan sun tafi school kafin kibar gidan nan dan da sassafe zanje aiki yanda yau banje ba din nan” “to zanyi Anty, nagode” Ummi tafadi tana mikewa tafice daga dakin tawuce kasa yan karikechan ta tashiga hadawa bayan tagama taje tayi girki, yaran suka dawo ta shirya su bayan sunci abinci takaisu islamiyya dake nan cikin estate nasu itama takasa gayamusu zatai tafiya dan tasan kuka zasuyi sosai amman wlh zatayi kewansu sosai.

Wuraren 10 yashigo gidan zama yayi a dinning yaci abinci bura busko Ummi tamai da wani miyan veggies mai dadi abincin dayaci saida yabashi tsoro tass yagama yakalli dakinta yayi murmushi yawuce sama ga mamakinshi Hadiza yagani a falon sama kwance kan dogon kujera daga ita sai wani dan black short mai kaman pant yanada lace abakin wandon very sexy, tasaka half vest milk na silk material mai kyau shima, dan juyowa tayi suka hada ido itada Nuran sannan ta maida kanta kan throw pillow ta kwanta tana kallon tv, ita kanta bama tasan maisa tayi gayun nan tazo nan ta kwanta ba, deep down so kawai take ya kulata, dakin Aman Nura yashiga yadubashi yamai addu’a yafito ko kallon inda take baiyiba yashiga dakin Amal yamata addu’a yafito ta gefen ido Hadiza keta binshi da kallon ganin su Hajiya basu dawo tareda shi ba to ya komar dasu Kano ne? Ko yamaka musu hotel ne?.
Dakinshi yashiga bayi yafada direct yayi wanka fitowa yayi daure da towel a waist ga mamakinshi Hadiza yagani kan gadonshi ta kwanta tana kallonshi exactly irin kallon shima yamata yadauke kai yawuce gaban madubi ya shafa mai ya feffesa lafiyayyun turarenshi yaje gaban wardrobe yaciro pajamas nashi yakoma bayi yasaka yafito, ganin ya dumfaro gadon yasa Hadiza tasoma jin dadi aranta agaban gadon ya tsaya yasake kallonta ido cikin ido itama kallonshi take right in the eye amman bazata iya bude baki ta gaidashi kota cemai sannu ba taga shigowanshi gida tun dazu, dauke idanunshi yayi daga kanta, filon dake gefenta yasa hannu yadauka yayi wajen kofa yabude yafita yawuce dakin Aman kan gadon Aman yahau yana kashe wuta ya kwanta abinshi yana sauke ijiyan zuciya.

Bugo kofan Hadiza tayi tashigo ta kunna wuta dakin yayi haske takalli Nura tace “kanka akeji daman sabida Mama tamin fada ne nazo turakan ka amman jibi yanda ka wulakanta ni, ka shanyani agado kataho dakin danka zaka kwana anjima kahau cewa ban maka komi na aure, oya kajika gabanka aruwa kasha mana kasan ai ka iya biyo sahu idan jarabanka yataso maka ka lallabani nabaka, ina jiran ranan zakasha mamaki na nima wlh” tajuya fuuu tafice daga dakin ta bugomusu kofa saida Aman ya firgita cikin bacci dasauri yarike Aman yana patting head nashi, chan bayan yakoma bacci yatashi yakashe wuta yadawo ya kwanta yayi bacci abinshi.
**

Washegari normal aikinta Ummi tayi Hadiza tasauko tai breakfast around 8 tawuce tafita abinta ko biyar bata bawa Ummi ba dan ba son tafiyan takeba, saukowa Nura yayi yana sanye da wata farar shadda yayi kyau bana wasa ba har gaban dakin Ummi yaje yayi knocking bude kofa tayi chak numfashin shi ya tsaya ganin Ummi tana sanye da sabon black dogon rigan daya saya mata, ta tsife kanta jiya da daddare ta wanke da sabulun wankanta abinta ta taje tayi Parking batada cikan gashi at all dan kanta ma small head gareta amman wani kalan coily blonde-black hair gareta dan gashinta ba baki sidik bane irin jajajan nan ne orange orange baki baki, fari fari irin gashin agwai haka gashinta yake ta yana gyale akai daya dan ja baya tasa kwalli a idanunta, rigan yamata chass ajiki ganinshi dan tun jiya sai yanzu suka hadu yasa ta juya dasauri zata koma cikin daki karaf yakamo hannunta dasauri tajuyo suka hada ido ta zubamai fararen idanunta dasuka sha kwalli ta diga kwalli in between giranta guda biyu tayi wani kalan unexplainable kyau, ahankali yasaki hannunta dayaji yamai taushin gaske kaman yarike hannun Amal sai kawai yajuya dasauri yayi dinning dan rabon dayaji wani abu yatadamai da sha’awa harya manta, ganin Ummi da dan kama hannunta dayayi just awaken libido nashi zama yayi a dinning yayi crossing leg da sauri batare daya juyoba yace “kin gama hada komi ina gama breakfast zamu wuce” daga chan ta dakinta tace “eh nagama” itama komawa daki tayi dasauri yanda taji hannun Alhaji cikin nata sai taji tana fitar da numfashi kashi kashi.

Tass yayi lafiyayyan breakfast sannan yazo wajen kofan yace “kawo kayanki mutafi” bude kofa tayi rike da ghanamasgo dinta akunyace kallon Ghanamasgon yayi sai kawai yajuya yace “ina zuwa” sama yakoma yadauko babban suitcase nashi yakawo har gaban dakinta ya duka yabude ya karbi Ghanamasgon baiji kunya ko kyama ba da kanshi yabude yashiga jera mata komi a suitcase din, yarinyar nada tsafta dudda kayanta sun mutu but komi awanke alinke ga dan black leather dayakai hannunshi zai taba dasauri Ummi ta duka tarigashi dauka hakan yasa ya kalleta sai kawai yayi murmushi dan yasan menene turawa tayi akasan akwatin nan da nan yagama hadawa suka kulle yaja akwatin waje Ummi na biye dashi har mota gaba yau yabude mata yana kallonta shiga tayi ahankali ta zauna yakallulle yadawo gaba shima yatada mota har Gwarimpa bakaramin addu’a Hajiya tamusu ba sannan Meena da Baffan shi da ita suka tafi airport ga mamamkin Ummi abokanshi tagani a airport already suna jiransu da Musa da engineer sunci manyan kaya sai kallo Ummi suke munafukai saijin dadi suke, jirgi suke shiga kalan tsoron da Ummi taji a ko tadauka mutuwa zatayi haka sukakai Yola motoci taga suna jiransu guda daya daya security personnel sauran nasu nan aka dauki hanyar kauyensu though sun tsaya a hanya anyi sayyaya na ban mamaki kayan abinci shopping da sauransu.
Tunda Ummi taga sun dauki hanyar kauyensu gabanta ke faduwa hannunta suka fara rawa komi nadawo mata sabi fill
Hannunta Meena tarike tace “ga dukanmu, ga mopol yan sandan chan babu abinda wani katon dan daban kauye ya isa yamiki” tafiyan awa daya da rabi yakaisu kauyensu, kauye ne da yamayi developing ga government work akwai government school, burtsatsai, primary health care da sauransu sai kallon ko’ina take komi ya chanza ta dade rabonta da garin har gidansu wanda yake babban gida ginin kasa irin na da din nan.
Wata tsohuwa sosai haka na zaune a tsakar gida tana mulmula hura taji ihuuu hayaniya a waje tace “Allah yasa ba shaidanin yaron nan ne yazo dawani bala’in ba yau” da gudu wata yarinyar mai kama da Ummi yar karama da bazata wuce 13yrs ba tashigo tana hakki. “Gwaggo Gwaggooo Ummi, Umm…..” kafi takarasa magana Ummi tashigo gidan tareda Meena, mikewa tsaye Gwaggo tayi saikuma tasa zani ta murje idanunta tasake kallon Ummi data tsaya tana kallon Gwaggo, Gwaggo tace “Kodai mutuwa ce tazomini yasa nike ganin kaman Ummi achan tsaye dawata balarabiya” dawani kalan gudu Ummi tazo tafada jikin Gwaggo sai kuka ga kanwar Ummi ta biyun itama tashigo sai kawai dukansu sukahau kuka dagota Gwaggo tayi tace “Ummi kene binni ya karba haka kin ganki kuwa ya akayi kikazo? Banace kada kizo ba duk sati sai Mudi yazo gid…..” fuska Ummi ta share tace “Gwaggo akwai baki maza awaje dauko tabarma Aisha ki shimfida wajenki zukazo” dasauri Gwaggo tace “bakin yan uwan baturiya nan ne, yaki yarinya gaki fara kaman madara” murmushi Meeena tayi tazo ta gaida Gwaggo, Gwaggo ta aika Aisha ashigo dasu nan da nan aka shigo dasu wai bakin Gwaggo yaki rufuwa taga manyan dattijawa ansha shadda fura tashiga hada musu kowanne a kwarya mai kyau su Aisha harda Ummi dama Meena natayasu har Baffa saida yasha huran sun dade basu sami aslin ingantaccen fura irin wannan ba sukai salla.
Daukan nasu huran sukayi su Ummi duk suka tafi daki saida aka gama Baffa ya gabatar da zancen daya kawosu wai Gwaggo kasa boye farin cikinta tayi nan ta sanar dasu komi game da Ummi da aurenta ada tace zancen aurenta kuma maigari ne mai bada yaran aure Dan haka atafi wajenshi nan akanshigo da komi aka shiga mota aka tafi wajen mai gari shima yayi naaam babu wani wahala Dan Auren bazawara ba wahala and tanada right Ummi tafito da mijinta yanzu tunda nabiyu ne kuma itane takawoshi har kauyensubnan da nan su Musa suka ijiyema abokinsu sadaki dubu dari uku aka daura aure tsakanin Nura da Zainabu Ummi akan sadaki 300k mutane dayawa sun shaida aka kawo su goro cingam menene menene aka rarraba wai Nura sai murmushi yake he just can’t believe it duk suna wajen Aisha tazo da gudu tace “Gwaggo ga Mudi chan yazo amman yan sandan nan sunmai duka” tashi Nura yayi da sauransu Maugari yace “dan Allah kukai yaron nan gidan yaro ya addabi mutanen Hm kauyen nan” komawa sukayi akai arresting Mudi nan fa Gwaggo tayi throwing small party itadai Ummi taja makale adaki taki fitowa Meena ko tafito sai video take yanda matan kauye ke rawa Musa yakawo bakinshi saitin kunnen Nura yace “kai mutumina bura’uban chan haka kauye keda tsala tsalan mata bazanyi wuff dawata ba kuwa anan kai jibidai kirjin wanchan dake rawa” tureshi Nura yayi yace “dan iska” dariya Musa yayi yana kallon yammatan, Musa yataba engineer yace “kaga yara amman Allah yamusu kindirmo a kirji” Nura yayi kaman baijishi ba aranshi yace “na Matata Ummi tamafi kowa nan kindirmo” yadan lashe lips yana kallon agogo, Aisha ne tazo tace “Gwaggo tace kazo” binta yayi zuwa falon Gwaggo tana zaune ga Ummi agefe kanta akasa zama yayi ahankali Gwaggo tace “Nura na yaba da hankalinka ne saisa nabaka Auren jikata dan mutumin kwarai ne zaisa diyarka a mota da yan uwanshi azo har kauyenku a nemi aurenta dan haka nabaka ita amana kagansu nan su hudu ne dukansu marayun Allah ne ba uwa ba uba kaji tsoron Allah bamu da kowa a binni dazance je gidan Ummi dobamin ita, tana hannunka ka kulamin da ita na yarda da tarbiyan dana bama yaran nan sunada kunya natsuwa amana da girmama na gaba dasu Ummi bazata taba cutarda kai ba Ummi matace karike ta amana sai kuma inaso nadan roki alfarma ka barta tadanyi ko sati guda ne anan wajena a danyi mata gyaran amare” abu Nura yaji ya tsayamai awuya Gwaggo tace “kayarda”? Ahankali yace “ba matsala” Gwaggo tace “yauwa tunda an kama shegen yaron nan banda sauran tashin hankali na gode Nura bari nafita nabaku guri kuyi sallama” Gwaggo ta tashi tafice.

Juyoda kanshi yayi yakalli Ummi da kanta ke kasa tana jikin bango kaman ruwa ya hadiyeta mikewa tsaye yayi yana duba agogon dake daure da writs nashi sannan yakalleta yace “tashi ki rakani Amarya zan tafi” akunyace Ummi tadaura duka hannayenta kan fuskanta tarasa inda zatasaka kanta sabida kunya, he loves yanda takemai yarinta yarintar nan kunya kunyan nan, gently ya duka agabanta dab da ita yana kallon dogayen yatsunta masu fararen kumba dake kan fuskanta daya rufe yayi shiru, kamshin da Ummi taji na shiga hancinta yasa tadan ware two of her right fingers kaman munafuka tadan bude idanunta dan so take taga ina yake dan yanda takejin kamshin turaren nan nashi karaf suka hada ido ya leko fuskanta ta spice na yatsun ahaukace ta yunkura zata tashi karaf yariketa hannunshi daya yakai ta waist nata yarikota dasauri taboye kanta akirjinshi sosai takejin kunyanshi, yanda yaji fuskanta akirjinshi yasa ahankali yasaki hannunta yakai dayan hannunshi daman bayanta yaturata tashiga kirjinshi gabaki daya sannan yacire hannunshi daga waist nata yasa dukansu abayanta ya rungumeta da kyau tareda sauke ijiyan zuciya ataushashe yace “Assalamu Alaykum Matata Zainab” wani irin sanyin kunya Ummi taji tanaji takasa yarda jikin Alhaji take arungume haka, wlh kirjinshi bala’in taushi ga fadi kaman wani katifa, tun tanajin kunya taki sakin jiki hartai lamo tadaina motsi tanaji yanda kirjinshi ke beating ahankali, wayanshi ne yahau ringing batare daya saketa ba yazare hannunshi daya yaciro wayan yakai kunne Ummi bataji akace ba, amman da muryanshi dataji harya chanza launi yace “bari nagama sallama da iyalina nafito” yana maganan yacire wayan daga kunnenshi yamaida aljihu kafin ahankali yakai hannunshi daya yadago kanta daga kirjinshi maida kanta tayi da sauri, murmushi yayi cikin whispering yace “ina sonki Ummi, amman banji amsan soyayyata aranki ba aka daura mana aure kina sona”? Noke kanta tayi akafadanshi kaman yanama yarinya magana yace “kunyana kikeji?” Gyadamai kai tayi, ahankali yace “nazama mijinki yanzu babu ragowan kunya, yaushe zaki bani amsa?” Kanta yasake dagowa for the second time wannan karan batai musu ba ahankali ya manna mata peck agoshi batare daya cire bakinshi akan goshinta ba yace “zanbar miki Meena da some mopol anan ranan itiyau zan dawo na dauke, banda yawo, idan kinason wani abu ki kirani ki sanar dani kinji”? Gyadamai kai tayi ahankali yasa hannunshi a aljihu yakamo soft hannunta yasa bandir na 500 aciki yace “ki ijiye kudin nan tare dake kome kikeso kiyi dashi kinji”? Gyadamai kai tayi, har lokacin bakinshi nakan goshinta lips dinta ya kalla tanada a bit chubby soft bottom lips sai na saman is slightly thin a bit pinkish a bit dark he seriously wanna kiss her like right now but then yanason tazama comfortable dashi dan ijiyan zuciya yasauke kadan kafin ahankali yasaketa yace “zan tafi” dan komawa baya kadan tayi kaman kada tafita daga jikinshi tana sussunnar dakai tace “Allah maidaku gida lpy nagode da abubuwan daka kawoma su Gwaggo Allah kara budi mai albarka” Ameen yafadi yayi wajen kofa dan juyowa yayi yakalleta kaman yadauketa yakeji yadai daure yadaga labule yafita daga dakin.

Bin dakin Ummi tayi da kallo ganin littafai da byro akan wani dan table yasa taje wajen ta bude tsakiyan book yafalllontahsiga rubutu, dasauri take rubutun cikin 2min tagama tadaga takara karantawa sannan tashiga linke paper wani kalan linki tama paper kaman flower wow yarinyar is creative fitowa tayi daga dakin da sauri Aishan su tagani tabata tace “imaza kaima mijina Shatu maza kafin su tafi” da gudu Aisha ta fanfala sai alokacin Ummi tadaura hannunta kan bakinta jin tace mijinta, Aiaha nafita suna tafiya haba tabi motan da gudu tana ihu yaran anguwa suka bita suna tayata ihu ana. “Mota ku tsaya ku tsaya” abunku da yaran kauye, Musa yafara hangosu dasauri yace “Nura wanchan ba kanwar Ummi bace ke biyomu da gudu da tawaganta” lekawa Nura yayi ganin yanda yara ke gudu ana ku tsaya yacema driver ya tsaya parking sukayi da gudu su Aisha sukazo wajen dasauri yabude kofa dan daga Nura sai shi sai engineer Baffa na dayan motan, ana bude kofan Aisha da karfin muryanta tana haki tace “Yaya Ummi tace nabawa mijinta wasikar nan” tamikama Musa wasikar juyawa Musa yayi yakalli engineer dake murmushi sannan Nura daya hade rai Musa yamika hannu yace “to sannu da aiki Shatu kawo” hannu yasa zai amsa saiga hannun Nura ya fizge ya sa a aljihun gaban riga yabama yaran wasu kudi daya ciro daga aljihu yace “nagode” yaran suka kwasa aguje Musa yarufe kofa yace “jamuje direba” yakalli Nura yace “wowww Ango wlh soyayyan kauye tayi ne jibi wani wasika da aka aiko maka an mata wata kinmin fulawa kaga engineer billahillazi a kauyen nan zanzo nima na nemi amarya inaaa kai kaga yaransu ne sunsha kindirmo tun suna jarirai yanzu duk yakoma kirjinsu” dariya duk sukayi Engineer yace “kaidai kwarto ne Musa shegen gari, kai ranan kasa na kusan kashe madam wannan maganin basir ai bala’i ne” dariya Musa yayi suka cigaba da hira ganin haka yasa Nura yaciro wasikar yana yaban design da magic na maida sheet of paper into flower shape da Ummi tayi ya warware ahankali.

 

“Assalamu Alaykum Baban Amalily, wanda yazama mijina ayau rana uku ga watan maris.
Amsan tambayan kace awannan sakon”
Gyara zama Nura yayi yacigaba da karatu.
“Acikin wani bakin dare mai duhun duhu daban taba tunanin zanga haske awannan daren ba wani haske ya gauraye inda zuciyan Zainabu Ummi take, kasan haske nada zafi a ido dakuma fata sai wannan hasken ya kasance mara zafi, mai taushi ce dakuma da tsantsa kyawu, kyawu irin wanda bantaba sanin akwaishi ba awannan duniyan sunan hasken nan NOOR wato NURA! Ana haka wata kalan guguwa mai karfi ya taso dake dauke da kifiyoyi guda uku masu zafin rabasheshen dalman wutan kauna ce ke tashi daga jikinsu, suna zuwa chak! Chak!! Chak!!! Suka sossoki zuciyata, kifiyoyin nan guda uku na dauke da kalma guda uku ne na farkon yace I nabiyun yace LOBE na ukun yace YOU!!!, I lobe you My Noor Baban Amalily” Yihuhuuuu!!! Nura yabuga ihu kaman dan daba dayasa su Musa duka suka juyo suka kalleshi yace “wlh Yarinyar nan ta tashi kaina, billahillazi dauko matata zanyi, kai dereba juya kan motan nan kaga ku kusauka ku shiga dayan motan, ba’a taba gayama Nura irin wannan kalaman soyayyan ba, wayyoo zuciyata nima kifiyoyin dalman soyaya sun chakeni” tsayawa duk sukayi suna kallon Nura kaman kanshi ya kwance.

Hahahahah Guys rate sakon soyayyan yan kauyen M shakur naku, I crafted this on my own chaiii yayi making sense kuwa???

Ummi fa zata haukata mana Nura Hadiza sorry for you, just look at how Ummi ke feeding mijinki soyayyan kauye, soyayyan uneducated girl.
[9/18, 9:17 PM] +234 706 542 1229: MATAN?? Ko MAZAN??

✍M SHAKUR

 

Back to top button