Duk KarfinIzzata Book 2Hausa NovelsHausa Novels

Duk Karfin Izzata Book 2 Page 34

Sponsored Links

Page 34

Barci mai daɗi ne ya kwashe su dukkan su biyu suna manne da juna ya ƙanƙame ta kamar wani yace zai kwace masa ita.

3am dai dai ya farka tare da waro idon sa waje juyawa gefen sa yayi bata awajen cikin kasala ya miƙe zaune chan ya hangota saman dadduma ta idar da sallah tana karatun al Qur’ani mai girma,zuro kafafunsa kasa yayi kafin ya miƙe tsaye ya nufi toilet.

A gurguje yayi wanka tare da ɗauro alwala kafin ya fito ya wuce dressing room jim kaɗan ya fito sanye da jallabiya fara tas ganin ya nufo wajen tane ya sanya ta miƙe ta bashi daddumar ta koma saman sofa ta zauna tare da ɗan kwantar da kan ta jikin sofar tana karatu kasa kasa.

Nafila raka’a 4 yayi sanna yayi shafae da witiri yayi sallama tare da gyara zaman sa yana jero addu’oe.
Almost 30mins ya ɗauka yana addu’a kafin ya miƙe ya nufi saman sofar da take zaune,a nitse ya ansa Al Qur’ani hannun ta kasan cewar tayi barci zaune a wajen bayan ya mai da Al Qur’ani ma zaunin sa ne ya dawo ya ɗauke ta chak suka koma saman gado,kwanciya yayi tare da ita a jikin sa yana ɗan shafa bayan ta
Kasa kasa cikin muryan barci tace “yaya Prince addu’ar me kamin? Ko dai baka sani cikin addu’ar kane? kallon face nata yayi kafin ya ɗan kawar da kan sa gefe “ina saki mana duk wanda ma yake gidan nan ina sa shi a addu’a ta” “to amma yaya Prince wani irin addu’a kake min? Shiru yayi bai tanka taba hannu ta sanya saman dogon hancin sa tana faɗin “yaya Prince me ya sa baka son yi mini magana sosai? Bayan kuma kai kace na koya maka magana” shiru nan ma yayi kamar bai ji taɓa “yaya Prince dan Allah…bai bari ta karisa maganar ba ya ɗaura hannun sa saman lallausan lips nata yana faɗin “sarkin magana kiyi barci” kukan shagwaɓa ta saka masa tana faɗin “ni dai yaya Prince hira nake son muyi gaskiya” zuba mata ido yayi yana mamakinta idan tana irin wanna shagwaɓan ba karamin burge sa take ba “uhm uhm yaya Prince wai ba zaka yi magana bane?” da wata daddaɗar voice da bai san yana da ita ba ya fara magana sak yadda take “to me kike so ince miki?” mamaki ne ya sanya ta waro manya manyan ido ta wajen daman yaya Prince ma ya iya shagwaɓa ba karamin burge ta abun yayi ba,ganin ta tsare sa da ido takasa magana ne ya sanya ya hura mata iska mai sanyi a face nata tare da ɗaga mata gera ɗaya alamar yane, cool murmushi ta saki kafin tace “yaya Prince Allah kai ɗin kyakkyawa ne sosai” kallon gefen ido ya mata da sexy voice yace “ba za dai kiyi barci ba kuma ba zaki kyale ni nayi ba ko?” Turo ɗan karamin bakin ta tayi cikin shagwaɓa ta fara magana “uhm uhm ni bana jin barcin ne ai kuma ban son kayi barci ka kyleni ni kaɗai” hannu ya ɗaura saman ɗan karamin bakin ta yana kewaye ɗan bakin yana faɗin “ba zaka ga baki ba sai magana at the first time idan mutun ya kalle ki zai ganki like you’re not talk” ya tsan nasa ta tura cikin bakin ta tana tsotsa kamar sweet,wani zirr zirr yake ji a jikin sa kamar ana masa allura cikin sauri ya zame yatsan nashi daga bakin nata dan bai san wata fitina yanzun nan “uhm uhm yaya Prince ni ka bani sweet na” girgiza kai yayi kafin yace “uhm uhm hannu nane sweet nakin? Baki ɓuɗe take kallon sa yadda ya kwaikwayi maganar nata ba karamin bata mamaki yayi ba amma yadda yayi maganar ya burgeta sosai da sosai,ganin alamar kamar ta tafi duniyar tunani ne ya sanya ya shafa fuskar ta da sauri ta ɗago ido ta ɗan kalle san kasa kasa tace “yaya Prince ai ya tsanka yafi sweet daɗi ni dai ka bani na cigaba da sha” “waya koya miki magana haka? turo baki ta daɗa yi tana faɗin “ni yaya Prince ba wanda ya koyamin ni da kai na na iya” “to why ban ta ɓa jin kinyi magana haka ba sai yau? gyara kwanciyar ta tayi da kyau a jikin sa kafin tace “ai daman mijina ne kawai yakamata na rinƙa yiwa magana haka ba wasu ba bai ma kamata wasu maza suji voice na ba idan ba miji na ba shi ya sanya bana magana sosai da wasu koda su diyana ne,voice na dan miji na kawai akayi shi” bakaramin daɗin kalaman ta yaji ba har ran shi lallai yarinyar nan tana da hankali da ilimi da sanin yakamata sosai kuma tana aiki da ilimin da take da shi ɗin
ganin alamar ya ji daɗin maganar tane ya sanya tace “yaya Prince amma in tambaye ka mana? zuba mata ido yayi ba tare da yayi magana ba cigaba da magana tayi “yaya Prince me ya sa baka so na? Shiru yayi na yan mintoci kafin yace “ni nace miki bana son ki? girza masa kai tayi alamar a’a “kafin kuzo gidan nan sister mace ɗaya nake da shi Auta ina matikar kaunar ta fiye da kai na daga baya kukazo kamar yadda na ɗauki auta a raina haka kuma na ɗauke ku so dukkan ku ina kaunar ku” ajiyar zuciya ta sauke ba tare da tayi magana ba “lfy? Kike sauke ajiyar zuciya haka?” “Yaya Prince ban taɓa tunanin akoi kaunar mu ni da yan uwana a ranka ko kaɗan ba shi ya sanya da naji kace kana kaunar mu kamar yadda kake son Aunty Zahra sai naji daɗi sosai har rai na” shiru yayi tare da lunshe ido bai sake magana ba kankame sa tayi tana jin farinciki har ran ta da haka barci ya ɗauke su manne da juna.

Washe gari misalin 7 suka gama shirin su na zuwa Maiduguri a tare suka jera zuwa part ɗin Ammi zaune suka same Ammi da yanmatan ta a palo har da diyana da ko tafiya bata iya yi sai dai a ɗaga ta.
Tana ganin yaya Aryan ta sunkuyar da kan ta kasa dan bata son haɗa ido ta shi
Gefe da gefen Ammi suka zauna suka sata a tsakiya kasan cewar tana zaune ne a saman sofa mai mazaunin mutun 3 cikin girmamawa su Zahra suka fara ɗaga musu gaisuwa Aryan ne kawai ya ansa gaisuwar bayan su Zahra sun gama gai da su su kuma suka gaida Ammi

“Ina zaku je naga kunyi shiri haka?” basu bawa Ammi amsa ba dan basu so su faɗa wa koma batun rashin lfy Aunty farida dan kar su ɗagawa kowa hankali
bgs ne yayi saurin cewe “Ammi na gama bincike na akan yaran nan dana sa aka kawo jiya,zasu zauna a gidan nan kafin mu koma Abdol zai je ya musu komai na school su fara karatu” waro ido waje Aryan yayi kafin yace “wasu yara kuma? Aina suke? Aina kuma ka samo su? Ammi ce tace “yarinyar ma tana ɗaki har yanzu bata saki jiki da muba bata son shiga cikin su Zahra da alama tsoron su take ji” “amma Ammi me ya sanya za’a kawo wasu kuma gidan nan wayan da bamu san su ba ko dai yan uwan mune? Chewar Aryan hararar wasa bgs ya wurga masa kafin yace “nayi binchike akan yaran suna da zuciya mai kyau wadda idan aka taimake su suma zasu iya taimaka wa wata al’umma nan gaba duk da sun taso cikin tsanani da wahala hakan baya hana su bautar Allah da dagewa wajen ganin sunci halak nasu duk da cewa iya face mark suke sayarwa suci abinci danace yaron ya bamu kyauta ya banu bai damu da cewa iya kan jarin su kenan ba bai damu da cewa idan ya bada sadaka shi zai rasa ba,duk ta laucin da suke ciki hakan baya hana su sadaka shiya sanya idan zakayi kyauta kar ka duba abun da zaka bayar ka duba ladar da zaka samu hakanne zai baka kwarin guiwar cigaba da kyautatawa na kasa da kai kullun ku kasan ce masu hangen ladan ku kar ku duba idan kun baya kazan ku zai ragu” murmushi Aryan yayi yana mamaki wai waya koyawa bgs magana mai tsawo haka mutumin da cewa okey ma wahala take masa ko da yake yanzu wa’azi yake wa su auta dan su rinƙa taimako.

Ajiyar zuciya Ammi ta sauke kafin tace “gaskiya ne nima ɗan zaman da nayi da yarinyar na fahimci tana da hankali da son taimakon mutane yanzu dai ina zaku je kukayi wanna shiri haka? Miƙewa bgs yayi ya dubi hiyana dake zaune ta sunkuyar da kai kasa yace “ke ki same ni a part na” yana kai karshen maganar ya fice daga palon
kallon diyana dake ta faman kunbure kumbure Aryan yayi cikin sanyi murya yace “my jidda ba gaisuwa? To ni bari na gaishe ki ya jiki? Kin rashi lfy?” Miƙewa Ammi tayi ta basu wajen a tare su Zahra suka miƙe hiyana ta fice daga palon ta nufi part ɗin bgs su kuma su Zahra suka wuce ɗakin su.

Kamar jira Aryan yake Ammi ta fice tana fita ya dawo kusa da jiddan sa tare da riko hannun ta duka biyu cikin muryan rarrashi ya fara magana “I’m so so sorry my jidda kin ji ko? Ayiwa yaya Aryan afuwa da ran gwami ba zan kara ba” hararar sa tayi ta kasar ido ba tare da ta ɗago ta kalle sa ba kasa kasa ta fara magana “ni ai nace na yafa maka tun da Ammi ta sa baki amma ni bana son ka ba zan zauna da kai ba amayar dani gidan Aunty farida na” shafa kansa yayi tare da kara matsowa kusa da ita yace “ok ɗago idonki ki kalli cikin ido na kice bakya so na idan kikayi hakan i promise u that zan mai daki wajen Aunty farida” “ni ba sai na kalle ka ba kawai ka mai da ni can dan ni ba zan zauna da kai ba” dukar da kan sa yayi ya leko fuskar ta yana faɗin “eyaeeee my jidda da kan ta kefa tawace ba mai rabani da ke mrs Aryan” duka ta kai masa a baya tana faɗin “Allah yaya Aryan kabari bana so ni da gaske nake bana son ka”dariya yayi tare da jawota jikin sa yana faɗin “eyeeeee mrs Aryan yanzu kam kin tuna sunana kenan ba a hospital kin manta sunana ɗin ba har da cewa ban son kallon wanna mutumin” ya kai karshen yana kwaikwayar yadda tayi maganar,kokarin kwace jikin ta tayi daga nashi tana faɗin “ni ka kyale ni ba wasa nake maka ba Allah ba…bai bari ta idasa maganar ba ya rufe mata baki tare da raba jikin su dan bai san ya jata da magana ta cigaba da cewa bata son shi yasan wacece diyana ita mutunce da idan ka ja magana ta kafe akan abu tofa ko mai wuya bata sauyawa.

Miƙewa tsaye yayi cikin sanyi murya yace “my jidda zan tafi Maiduguri amin addu’a” sai lokacin ta ɗago da sauri karaf suka haɗa ido kawar da idon ta tayi gefe kafin ta fara magana “dan Allah yaya Aryan ka tafi da ni sai ka barni wajen Aunty farida” dukowa yayi ba tare da yayi magana ba yayi kissing na goshin ta ya juya ya nufi kofar fita yana faɗin “ina kewar lallausan lips ɗin my jidda ta Allah ya baki lfy idan kin samu sauki zamuje tare” cikin sauri ya fice dan bai san jin kukan ta kuma yasan ba makawa sai tayi kuka haka ko akayi yana fita tasa kuka kamar wata yar baby ita ala dole sai an tafi da ita

A ɓangaren hiyana kuwa tana shiga bedroom nashi zaune ta samesa a bakin gado da alama ita yake jira gaban sa tazo tana kokarin tsugunnawa ya jawota jikin sa cikin kunnen ta ya raɗa mata “waye ce ki gudu ɗazun?” Murmushin tayi tana mai jin daɗin sauyawar da yaya Prince yayi daga jiya zuwa yau abun ba karamin kayatar da ita yake ba duk da cewa yace shi ba son ta yake ba har da wani cewa ta samo miji ya mata aure to da alama dai maganar yaya Aryan ne gaskiya

Hannu ya ɗaura saman wuyar ta yana shafawa “zanyi tafiya zuwa Maiduguri yanzu i need your prayer” buɗe baki tayi tana kokarin yin magana yayi sauri rufe mata baki yana faɗin “ni ba a nan nace ki min addu’a ba time ya tafi kamata yayi mu isa Maiduguri tun 7 amma yanzu almost 8:5 bamuma tafiba yanzu dai tashi min ajiki na bari mu wuce shagwaɓe fuska tayi kamar zatayi kuka tace “yaya Prince ayya zan bika” girgiza mata kai yayi tare da miƙa wa da ita tsaye ya nufi hanyar fita.

Sai da suka fita palo ya sauke ta a tsakiyar palon ya manna mata kiss a goshi sannan ya wuce ya fice daga palon,zuba masa ido tayi har ya fice sanna ta koma ɗakin sa tafara gyara masa,bayan ta kammala ta cire kayan jikin ta tare da cire ɗan karamin nauran da ya bata ta ɗaura saman mirror ta shiga wanka.

45mins ta ɗauka kafin ta fito ɗaure da towel a kirji ta ɗauki hijabin ta ta sanya ta fice daga ɗakin ta nufi part ɗin Ammi
har zata shiga part ɗin Ammi sai ta tuna ta bar na’uran da ya bata a saman mirror sa girgiza kai kawai ta wuce cikin part ɗin Ammi tana faɗin “zan dawo na ɗauka anjima”

tana shiga palon Ammi ta samu yaya Khalid yaya Fahad yaya Yusuf suna zaune ga matan su zaune kusa da su suna hira
har kasa ta tsugunna ta gaida su cikin girmamawa sanna ta wuce ɗaki ta shirya cikin doguwar riga pink colour ta sanya hijabi har kasa sanna ta fito palo ta zauna kusa da diyana sai hira su Zahra suke

“Yaya Khalid dan Allah ka kai ni gyaran gashi pls”chewar Zahra tayi maganar a shagwaɓe Khalid ya buɗe baki zai yi magana hiyana ta rigasa da cewa “Ni ma yaya Khalid muje tare dan nima gashi na yana son gyara” murmushi Khalid yayi kafin yace “ok to ku shirya muje” kallon su amrat Zahra tayi tace “amrat lamrat ku fa zaku je ne? Har suna haɗa baki wajen cewa “aa ba zamu je ba” yar dariya Khalid yayi kafin yace “oh sister’s hadda saurin haɗa baki haka to shikenan yanzu dai auta dake da sister ku shirya muje” da sauri diyana tace “nima ina son zuwa” girgiza kai Khalid yayi yana faɗin “aa jidda ki bari sai kin samu sauki sai na kai ki ko kuma Aryan ya kai ki” shiru tayi bata sake magana ba dan bata son yawan magana da su Khalid,mikewa Zahra tayi ta kama hannun hiyana tana faɗin “muje mu shirya idan munyi sallar azahar sai yaya Khalid ya kai mu,tana kai karshen maganar suka wuce ɗaki.

Miƙewa Yusuf yay ya riko hannun lamrat yana faɗin “muje mu gaida Ummi” “to” kawai tace kafin ta miƙe su fice daga ɗakin miƙewa Khalid ma yayi ya fice
satar kallon diyana ta kasan ido Fahad yayi kafin ya dawo da kallon sa kan amrat dake kusa da shi “amri tashi muje ko” kallon diyana tayi itama kafin tace “yaya Fahad zan zauna a nan nayi hira da Aunty diyana” tun bata gama rufe baki ba diyana tace “ni ban ce ki zauna ki dame ni ba ato kiyi tafiyar ki ban son surutu” murmushi Fahad yayi a ransa yace diyana uwar rigima ita dai idan bata son abu bata jin kunyan faɗin bata so haka kuma idan tana so abu a gaban kowa take faɗin abun da ke ranta. sunkuyar da kai kasa amrat tayi dan har ga Allah bata son bin yaya Fahad gashi diyana ta sa dole ta bishi,kumbura kumatu tayi a ranta tana faɗin “shi yaya Fahad ɗin nan sai yayi ta matse mutun baya gajiya ko kaɗan” ta shagala da tunanin sai jin sa tayi ya sureta sama ya saɓa ta a kafaɗa ya fice da ita
suna fita diyana ta gyara kwanciyar ta saman kujera tana faɗin “haka kawai zaki dameni ni kam Allah ma ya sa yaya Fahad ɗin nan ya miki abun da yaya Aryan yamin kila kyayi hankali, rumtse idon tayi kamar mai barci.

To masu karatu sai muleka yola muga me suke ai katawa

Yola

Yaya bello kamar zai yi kuka haka suka fito shi da hasana riƙe da bakkon kayan su su inna suna biye da su a baya har wajen motar da Ammi ta aiko akan a ɗauko su sukaje gaba ɗaya jama’ar kauye sun fito yimusu sallama kuka hasana take sosai dan ita gani take kamar idan taje birni ba zata dawo ba.

gidan baya na motar yaya bello ya shiga hasana kuwa tana tsaye tana kuka,dafa kafaɗar ta innar bello tayi tana faɗin “ba komai In Sha Allah ki shiga ku tafi” juyowa tayi ta rungumi inna cikin shesshekar kuka tace “inna dan Allah ki sa baki a bani hajjo mu tafi da ita” kallon maman hasana dake tsaye rike da hannun hajjo innar bello tayi kafin tace “inna wuro dan Allah ki bata kanwar tan nan mana tun jiya aketa ta rokon ki amma kinki ba abun da zai faru tun da kika iya barin hasana ta tafi itama hajjo zaki iya bada ita” shiru maman hasana ta ɗanyi kafin ta saki hannun hajjo tana faɗin “to kije Allah ya tsare min ku” da murna hasana ta rungumi hajjo yarinya yar shekara 14 suna ta farinciki suka shiga mota. gaba ɗaya jama’ar kauye sai addu’a da fatan alkhari suke musu,sai da motar ta kurewa ganin su sanna su inna suka koma cikin gida.

Maiduguri

Koda suka isa gidan Aunty farida kwance suka sameta saman katafaren gadon ta idon ta buɗe tana kallon sama ko motsi bata yi kallo ɗaya bgs ya mata ya fahimci irin ciwon Ahmad ne kallon dadyn Junior dake zaune gefenta yayi calmly ya fara magana “Aryan zai cire mata ruwan nan da aka sa mata zamu wuce da ita kano anjima yanzu dai ina zuwa”yana kai karshen maganar ya fice da ga ɗakin
miƙewa Aryan yayi ya cire mata ruwan dake jikinta suka fito palo shi da dadyn Junior.

To kunji halin da Aunty farida ke ciki mu waiya kano kuma muga wani waina su hiyana ke toyawa

Kano

Zahra hiyan Sun gama shirin su tsab yaya Khalid da kan sa ya ja su a cikin motar sa suna tafiya suna yar hira Zahra a gaba mota hiyana a baya “yaya Khalid ayya zaka kai mu wajen lallema idan mun gama gyaran gashin?” chewar hiyana kallon ta yayi ta cikin mirror motar kafin yace “yanzu haka addu’a nake Allah ya sanya kar bgs ya nemiki har muje mu dawo nayi gangancin fita da ke ba tare da izinin sa ba sai yanzu ma nake nadamar yin hakan” “to ai yaya Prince bay…bata karisa maganar ba tayi shiru kasan cewar ta tuna tun da yaya Prince bai sanar da yaya Khalid akan tafiyar su ba to tafiyar sirri ce bai kamata ta sanar wa kowa ba amma ta sha ruwan mamaki ya akayi yaya Prince bai sanar da yaya Khalid ba ya sanar min?
tayi nisa cikin tunani Khalid ya taka wata wawan birki wadda ya sanya sai da kanta ya bugu da jikin kujerar gabar motar.
A zafafe ta ɗago kai dan taga me ya sanya yaya Khalid taka irin wanna birki haka,wata mota ta gani kirar siyasa baka mai bakin glass ne ta sha gabar su kan kace me jibga jibgan bakaken mutane sanye da bakin kaya sun rufe fuskar su baka iya ganin komai sai ido ne suka fito daga cikin motar
Khalid na kokarin ɗaukan wayar sa babban cikin su ya buɗe kofar motar nasu ya damko Khalid ya fitar waje ba tare da ɓata lokaci ba suka tura Khalid cikin motar su sanna suka fito da hiyana da Zahra nan fa suka ruɗe sun rasa wacece ogan su yace su kawo dan Zahra da hiyana da bgs duk kamannin su ɗaya sak kamannin Ammi suka ɗauko. Fito da wani hoton ogan nasu yayi da wata murya mara daɗin ji ya dubi su Zahra ya nuna musu hoton yana faɗin “wacece wanna a cikin ku? Murya na rawa hiyana tace “ni ce” da sauri Zahra tace “ba ita bace ni ce” tsawa ya daka musu tare da fito da bindiga ya saita su yace “idan baku faɗa min wacece ba sai na harbe ku dukkan ku biyu!!” “wlh karya Aunty Zahra take ni ce ba ita bace” chewar hiyana damko wuyar hiyana yayi ya turata cikin mota suka shiga suka tada motar da gudun gaske suka bar wajen

durkushewa kasa Zahra tayi ta saki kuka mai ban tausayi tana faɗin “me yasa zaki ce kece Aunty Hiyana? why ba zaki bari su tafi da ni ba tun da yaya Khalid na hannun su ni nasan yaya Prince ya fara son ki yanzu idan suka kashe ki shike nan ba zai sake son wata mace ba” tana kuka tana surutai kamar mahaukaciya.

Sai da tayi kukan ta mai isar ta san nan ta miƙe ta koma cikin motar su cikin sauri ta ɗauko wayar ta tafara kiran layin Bgs sau uku tana kiran sa bai ɗaga ba kiran layin Aryan tayi shima har sau uku bai ɗaga ba juyawa tayi gabas da yamma hanyar shiru babu motsin kowa lokacin guda mugun tsoro ya dira a ranta gashi ita bata san haryan komawa gida ba dan ba fita take ba ko school kai ta ake kuma a ɗauko ta chan wani dabara ya faɗo mata akan ta kira layin Abba
cikin sauri ta fara kiran layin Abba shima bai ɗaga ba ihu ta saki tare da yin wurgi da wayar gefen titi dan bakin ciki
tarwatsewa kaca kaxa wayar yayi,sai bayan da ta fasa wayar ne kuma ta fara nadama yanzu dame zata nemo gida akan azo a ɗauke ta fita tayi daga cikin motar ta fara tafiya da kafa tana tafiya bata ma san in da ta nufa ba tanayi tana kuka kamar zararriya.

To masu karatu sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu to masoyan yaya Khalid masoyiyan hiyana masoyan Zahra aikin tsayuwar dare ya ganku fa amusu addu’a gashi zaku nan gidan Abba basanan suna Maiduguri akoi chakwakiya fa hmmmm

 

Back to top button