Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 41

Sponsored Links

 

Ammi sai da ta ɗan yi jimm, sannan ta dubi rumaisa ta ce “Ita aishan ce ta saka masa wannan sunan?”

Ruma ta ce “A’a, ni na saka masa, sunan babana ne, ina son sunan sosai”

“Ba shi ne sunan da na yi niyyar sakawa ɗana ba, ba zan saka wannan sunan ba” Takawa yayi maganar cike da iko, sai da mama ta ɗan ji babu daɗi, ko da zai canza sunan bai kamata ya faɗa a gaban ruma haka ba, ba za ta ji daɗi ba.

“Ka ga ba fa ɗanka bane ba, tun da ni ta ce ta barwa shi, ɗana ne Mahmud na saka masa, kuma ba zan canza ba” ta yi maganar tana yi masa kallon banza.

Ammi ta ce “Madalla, suna mai girma da karama, Ubangiji Allah ya raya Mahmud, ta zauna maman baby, mun karɓi sunan” kallon da Ammi ta yi wa takawa ne ya sanya shi haɗiye maganar da yayi niyyar yi.

Ammi ta dubi ruma ta ce “Rumaisa, Haryanzu baki gaya mana ya ki ka baro aisha ba? akwai buƙatar ki bawa Adam haɗin kai wurin amsa tambayoyin da zai yi miki, tun da shi ma jami’in tsaro ne. Yaya Aisha take? Ya aka yi ki ka fito da ke da jaririn babu ita?”

Rumaisa ta ɗan yi shiru tana wasa da gefen bedsheet ɗin da take kai, hawaye ya taru a idonta, sai dai babu tsammani ta yi ƙara tana kare fuskarta da hannunta, da sauri mama ta ƙarasa wurinta tana tambayarta ko lafiya?.

Jikin ruma sai rawa yake yi, ta rungume mama tana ɓoye fuskarta.

Mama ta ce “Rumaisa ki yi magana mana, menene?”
Ruma ta ɗago a hankali tana duba jikinta ta ce “Sha tara ne ya harbe wani mutum jininsa ya ɓata mini jiki”.

Jiki a sanyaye mama ta ce “A asibiti fa ki ke a tare da mu, duba ki gani, jikinki babu komai babu jini” mama tayi maganar tana nuna mata rigarta, sai dai duk da haka ruma sai haki take kamar ta yi gudu.

Ammi ta ce “Haryanzu akwai sauran razani a tare da ita, dole ta razana tun da ki ka ga haka, Allah kaɗai ya san abubuwan da ta gani. Bari mu tafi ta samu ta huta, sai dai duk da ban san zuwa yaushe za a salleme ku ba da yaron nan, zan roƙi alfarmar ku, ya ɗan zauna a wurinku kan a sallami rumaisa, muna ƙoƙarin shawo kan wata matsala ne, kan mu kai shi gida kowa ya sani” abun ya ɗan ɗaurewa mama kai, wace irin matsala kenan? Amma ba ta tambaya ba ta ce “A’a babu damuwa, Ubangiji Allah ya raya mana shi a bisa tafarkin Annabi Sallallahu alaihi Wasallam”.

Ruma daga kwance ta ce “Ni fa ba wanda zan bawa ɗana, ɗana ne fa”.

Ammi ta ƙarasa gaban gadon ruma, ta shafi kanta ta ce “Dama naki ne, aro zaki bamu ai, Allah ya baki lafiya ya tsare gaba” ta yi maganar tana murmushi.

Ruma ta amsa da Amin, daga nan suka yi sallama suka tafi.

Suna tafe a hanya Ammi ta ce “Gaskiya akwai matsala, idan har yarinyar nan ba ta yi bayani ba, dole mu nemi yadda zamu yi”

Takawa ya ce “Ammi, ni fa na riga na gama shirin tarar kowane irin ƙalubale zan fuskanta, na san duk yadda muka kai ga ɓoye lamarin nan, nan kusa zai baiyyana, ko da a yanzu ma kalli a halin da nake ciki, kuma kar ki manta, da dogarai uku ki ka zo wurin nan, a gabansu aka faɗi komai, na san a kowane lokaci maganar nan zata watsu”.

Ammi ta ɗan yi jimm sannan ta ce “Lokacin da Abokin ka bashir ya yi mini waya, babu halin in fita nikaɗai, kuma ban san kiran me yayi mini ba, wannan dalilin ne ya sanya na tafi da su, kuma jiya na ja musu kunne a kan su yi shiru da bakinsu”.

Ya girgiza kai ya ce “Ammi, kin manta gidan nan ne, lokacin da aka fitar da zancen ina shaye-shaye na yi yinƙurin yi wa iman fyaɗe, mutum nawa ne a wurn, wa zaki kama ki tuhuma ki ce shi ne? Haka wannan ɗin ma, dole zan matsa lamba yarinyar nan ta yi mini bayani, na san in da zan nemi mafita”

Ammi ta yi shiru, abubuwa sai sake cakuɗewa suke yi, ba a warware wannan ba wancan sai ya kunno kai.

“Ammi, meyasa ki ka amince da sakawa yaron nan Mahmud? Ni ba sunan da zan saka masa ba kenan, sunan Alhajinmu na so mayarwa, ni bana son sunan nan”

Ammai tayi murmushi mai ciwo ta ce “Haba babban mutum, ban ji daɗin jin wannan maganar daga bakinka ba, a bar wannan zancen dan Allah, ina roƙa mata alfarma, a bar mata wannan sunan tun da shi take so”.

Takawa ya ɗan duƙar da kai ya ce “Tuba nake”.

Bayan tafiyar su takawa kuwa Abdallah ne a ɗan hasale ya ce wa ruma “Dan ubanki ba a yi wa masu mulki magana yadda ki ke yi musu, gatse-gatse babu ɗa’a, wai ma ke kowa sa’anki ne da zaki din ga magana son ranki? Na fuskanci ba ki yi laushi ba haryanzu. To wallahi sai an basu ɗan su, ke gama rainonki aka yi da zaki janyo mana wani? Ki kuma cewa ɗanki ne ki ga yadda zan yi da ke” Jin Abdallah kawai take yi, amma gani take idan zasu mayar da ita ƙuli, babu wanda zai rabata da jaririn nan.

Washegari ‘yan Katsina su gwaggo da iya, da sassafe suka yi dirar mikiya a Kano, yayin da ‘yan uwa da abokan arziki, malaman islamiyya da makarantar bokonsu rumaisa, haka mutane daga lungu da saƙon unguwa, suka din ga zuwa dubiya gami da jajen abun da ya samu rumaisa, sai dai fa unguwarsu rumaisan ta ɗauka a kan jaririn da rumaisa ta dawo shi, nan da nan zantuka kala-kala suka hau zagaya cikin unguwa, masu daɗi da marasa daɗi a kan rumaisa.
Aliyu ya cika alƙawari, ya kawo Habiba har ɗakin da rumaisa take na jinya,ita da babarta, suka rungume juna suka din ga kukan farin ciki.

Gwaggo kuwa sai da ta yi kuka tana neman mama ta yafe mata da ta sanya a ka kai ruma aka ɓoye, ta ɗora alhakin faruwar komai a kan ta, har da su lawisa duk aka zo, rumaisa ta yi farincikin yadda mutane ke ta shiga suna fita duk saboda ita.

Sai dai duk rawar kan rumaisa taƙi sakin jiki ta basu labarin abun da ya faru a zamanta a hannun ‘yan ta’adda, ko zancen aka ɗauko sai ta haɗe rai ta hau kuka, gashi haryanzu lokaci zuwa lokaci tana razana, haka kurum tana zaune sai ta hau ihu, tana kiran sunayen ‘yan bindigar ta ce zasu yi mata wani abu, har sai da mai sunan Baba ya hana yi mata zancen gaba ɗaya.

Tun da aka rubutawa rumaisa hoto, mama ta aika Abubakar ya tambayo kuɗin hoton, aka ce masa dubu arba’in da uku, mama ta ɗan shiga damuwa, domin kuɗin da yawa, ba ta son yawan ɗorawa yaran ɗawainiya, dan ma kuɗin asibiti da na magani ba biya suke yi ba, an riga an ɗau nauyin lafiyar rumaisa a aljihun takawa, dan tun da bashir ya ji yaron nan na Adam ne, ya sanya aka canza musu asibiti zuwa babban asibitin kuɗi, domin samun kulawa ta musamman tun da ya san adam yana da kuɗin biya, ko magani likita ya rubutawa ruma, sai dai kawai a ɗauko a kawo musu, sai dai wanda babu su je waje su saya.

***
Tana zaune a kan katafaren gadonta, sai shirya mata kayanta mai aiki take a cikin akwati, dan ta ƙallafa ranta a kan tafiyarta Abuja nan, sai ba wa mai aikin umarni take cikin isa da kuma gadara gami da wulaƙanci.
Samha kenan akwai gayu da ƙwalisa, sai dai babu hali mai kyau, ɗaya daga cikin wayoyinta ta duba ba ta gani ba, ta js ɗan gajeren tsaki, ta fita ta tafi ɗakin mama.
Mama ta tarar tana ta ƙananan surutai tana mita. “Mama na bar Samsung ɗina a ɗakin nan ne?”.

“Ke ni rabu da ni da wata wayarki, turaki ya ɓata mini rai”.

Samha ta ce “Too ikon Allah, mai Baban kuma yayi miki?”

“Manta kawai, jirgin ƙarfe nawa zaki bi?”

Samha ta ɗan yi ajiyar zuciya ta ce “Ƙarfe biyar na yamma, amma ki din ga haƙuri mama, kin san tsufa yana taka muhimmiyar rawa a kansa yanzu, idan ki ka matsa zaki yi ta damuwa ne ranki yana ɓaci”.

Ɗan shiru mama tayi sannan ta ce “Abun nasa dai ba tsufa bane, ba wani tsufa kawai halinsa ne, ina yi masa maganar wani abun daban, amma yana nuna mini maganata ba ta da muhimmanci yana kawo mini nasa zancen da bai shafeni ba”.

Samha ta yi murmushi ta ɗau wayarta ta ce “Na san tatsuniyar gizo ba ta wuce ƙoƙi, yakamata ace zuwa yanzu kin saba mama, ki yi haƙuri, bari na je na cigaba da shirina” daga haka ta fice ta koma ɗakinta.

***
Abubuwa suka cakuɗewa Adam gaba ɗaya, kallo ɗaya zaka yi masa ka san a cikin tashin hankali yake da matsananciyar damuwa, Ammi ta ce sam ba ta yarda ya je gidansa ya zauna shikaɗai ba, don tun da ya shiga damuwar nan take cikin fargaba, kar ciwonsa ya tashi abu ya ƙara haɗe musu.
Yau da safe Ammi da kanta ta je ta saka Adam a gaba a kan ya ci abinci amma ya kasa ci, sai da ya ga ta matsa sosai da sosai sannan ya ɗan cakali kaɗan ya bar shi.

Ammi ta dube shi a tsanake sannan ta ce “Takawa” ya ɗaga kai ya dubeta.

“Yanzu meye abun yi ne? Me ka yanke a kan lamarin nan, kuma ya ake ciki game da binciken?”

Ya ɗan yi jimm sannan ya ce “Dama Bashir ne incharge ɗin da case ɗin yake a hannunsa, sannan police ɗin da case ɗin yake hannunsu suna ta ƙoƙari, ina ga in anjima za su je asibitin da kansu, su yi mata tambayoyi”.
Ammi ta ɗan sauke numfashi sannan ta ce “Bana son a cigaba da yawan matsawa yarinyar ne a kan maganar, na ga haryanzu tana cikin razani, dole a bita a hankali”.

Adam a ransa ya ce “Babu wani razani, tsagwaron iskanci ne, kuma da ni take zancenta, ba zan lamunci iskancinta a kan rayuwar matata ba’

Amma a zahiri ya ce “Amma Ammi dole ta yi magana domin gaggauta ceto Aisha”.

“Eh haka ne, amma ita ma ‘ya ce, kuma yakamta a bita a sannu, saboda lafiyar ƙwaƙwalwarta, kana kallona gabanka jiya take ihu wai an harbe wani” Ammi ta dafe goshi ta ce “Innalillahi wa Innalillahi raji’un, Allah ya shiga tsakanin na gari da mugu, dole yarinyar nan ta shiga ruɗu, ayi kisan kai a gaban yarinya ƙarama kamar wannan”

Shiru Adam yayi, yana ta addu’a Allah ya sa Aisha tana lafiya.

Ya kalli ammi ya miƙe tsaye ya ce “Ammi, bari na je asibitin nan da kaina”.

“A’a kar fa ka je ka nuna musu zafin zuciya da zafin kai, ka bi komai a hankali”.

Ya girgiza kai ya ce “Ba wani abun zan yi ba, kin san yau za’a kai ta x-ray, so nake na je na ga yaron, in kuma jarrabawa ko zata yi magana”.

“To shikenan, ka gaishe su, ni sai zuwa dare in Allah ya kaimu na je” ya jinjina wa ammi kai ya fice.

Likita ne a tsaye a kan rumaisa da take ta bacci, tun bayan da mama ta yi mata wanka, ta yi wa jaririn, ta kwantar da shi a kusa da rumaisa suke ta bacci, haka nan mama ma yaron ya shiga ranta, ga yaron da matuƙar haƙuri, idan yayi kuka ko dai ya gaji da kwanciya ko kuma yana jin yunwa, daga bacci sai cin hannu kawai yake yi, mama ba ta taɓa jin ta gaji da ɗawainiyar da take da ɗan da bata da alaƙa da shi ba, ji take yi hakkinta ne na uwa ta kula da shi, gefe guda kuma tana matsanancin jin tausayinsa tare da fatan Allah ya kuɓutar da mahaifiyar sa, ita kanta da ta ɗaukowa rumaisa zancen uwar yaron, sai ta hau zabure-zabure.

Likita yana duba file ɗin ruma yana kallonta, mama ta ce “Likita babu dai matsala ko?”.

Ya ce “Eh babu, duk wasu gwaje-gwaje da yakamata ayi mata mun yi mata, babu wani mummunan ciwo a tare da ita, sai dai zan rubuta wata allaura a sayo ayi mata, saboda ciwon haƙarƙarin da take kuka da shi, kan ku yo hoton”.

“Eh, in anjima za aje yin hoton in Allah ya yarda, dan sai daf da asuba ta samu bacci, da gari ya waye na tasheta, tana ta kuka da wurin”.

Ya ce “In sha Allah idan aka yi allurar, za ta samu releif, kan muga sakamakon”.

Mama ta ɗan nisa sannan ta ce “Amma likita ba su yi mata wani abu ba dai ko? Basu taɓa ta ba kun duba?”.

Ya jinjinawa mama kai ya ce “Ki kwantar da hankalinki, akwai report da police suka bamu, tun daga asibitin farko da aka kaita, da na biyu zuwa nan, muma da namu binciken, komai lafiya ƙalau”.

Mama so take ya bata amsa ƙarara, amma kamar bai fahimci me take nufi ba, ba ta son ya ga kamar ta matsa masa, dan haka ta ƙyale shi”.

Ganin yadda rumaisa ke kuka da ciwon haƙarƙarin nan ya sanya ta ce bari ta yi sauri ta je ta sayo allurar, gashi da wuri Abdallah ya tafi, yau yana da jarrabawa a makaranta, gwaggo kuma daga ita har iya suna fama da jikin girma, suma mama cewa tayi su tafi gida su huta, dan haka ganin ruman na barci ya sanya ya fito nursing station ta ce musu dan Allah ga rumaisa nan, za ta je sayo allura.

Mama na fita takawa ya iso asibitin, dan direba ya saka ya kawo shi, shi ba zai iya tuƙin ba.

Yana daf da shiga ɗakin da rumaisa take, likita ya fito daga ɗakin kusa da nata, suka tsaya suna gaisawa.

Takawa ya tambayi likitan ya jikin jaririnsa?.

Likita ya ce “Baby yana nan lafiya Alhamdilillah, shi ya samu sauƙi sosai Alhamdilillah, mamansa ce dai iya rigima haryanzu muna fama ba ta warware ba, muna jiran sakamakon hoton da zamu turata mu san abun yi na gaba”.

Adam ya ce “Haryanzu ta ƙi magana a kan in da mahaifiyar yaron nan take, da an yi maganar sai ta hau ihu, dan Allah hakan yana da nasaba da razani ko kuma iskanci ne kawai”

Sai da doctor yayi dariya ya ce “To kowanne ma zai iya kasancewa, amma razani kam tabbas tana cikinsa haryanzu, wasu lokutan tunanin ya kan ƙwace mata ta zaci tana hannunsu haryanzu, amma abi komai a hankali, sannan dan Allah idan ku ka tashi karɓar yaron nan, ku bita a hankali ta shaƙu da shi sosai, kar ku rabata da shi lokaci ɗaya”.

Bayanin likitan na yanzu ya shiga ta kunnen Adam na dama, ya fita na hangu, dan bai ji zai iya saurarawa ko ɗaga ƙafa wurin karɓar ɗansa ba, yanzu ma don yana cikin tashin hankali ne, da damuwa da son sanin in da matarsa take, ba dan haka ba, da tuni ya ɗauk ɗan sa.

“Thank you very much” ya faɗa a taƙaice ya shiga ɗakin rumaisa.

Sai dai yayi mamakin ganin babu kowa, baccinta take hankali a kwance, gefenta ga jaririn shi ma yana barci, kai ka ce uwarsa ce.

Ya ƙarasa gaban gadon ya tsaya ya ƙare mata kallo, a haka tana bacci looking so innocent, amma a zahiri halinta idan ba ka kai ziciyarka nesa ba, sai ta sa zuciyar mutum ta buga.

Ya kalli ƙafarta da aka rage bandejin da ake saka mata, saboda raunukan da suke ƙafar, ga wani yanka a ƙwaurinta, kai da gani ka san faɗuwa ta yi, ga tabo a gefen goshinta, kai ba sai an gaya maka iya wannan ya isa ya tabbatar wa mutum da ruma ta azabtu kan ta kuɓuta.

Hannunsa biyu ya saka a kan gadon, ya ƙurawa yaronsa ido da yake daga lungu, ya tuna irin yadda suka shirya rayuwa da shi da Aisha idan Allah ya sauketa lafiya, da irin budurin da suka shirya yi, da yadda take nanata masa sai dai su bawa mutane mamaki, ba wanda ya san da cikin sai dai su ce wa mutane ga babynsu, yau ga baby amma ita ba ta nan.

“Aisha why, meyasa a karon farko ki ka tsallake umarnina abun da baki taɓa yi ba, gashi kin sanya mu a wani hali” ya furta lokacin da hawayensa ya gangaro ya zuba a hannun rumaisa.

Juyi tayi zata gyara kwanciyarta, ya ga tana nema ta danne masa ɗa, dan haka cikin azama ya miƙa hannu zai ɗauke yaron. Caraf rumaisa ta riƙe hannunsa ta buɗe ido ta kalleshi.

“Wayyo Allah zai sace mini ɗa, mama kina ina” ta ware murya iya ƙarfinta tana ihu.

Ayshercool.

*₦500 ne, via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143*

https://chat.whatsapp.com/G9XU8tDJMjq02zlZMHurZ5
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI’IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA’A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA’IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA’IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni’ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

Back to top button