Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 44

Sponsored Links

Lumshe idonta ta yi, hawaye na tsiyaya daga idonta, mai sunan baba yana jin yadda zuciyarta ke bugawa da saurin gaske.

Duk wanda yake ɗakin sai da yayi sak, cikin ammi ya kaɗa yayi wani irin ƙugi, take ta fara fatan Allah ya sanya mafarki take ba gaske bane ba.

A hankali takawa ya tako cikin ɗakin, sai a lokacin suka lura da zuwansa, ya ƙarasa gaban gadon rumaisa, da take kwance a jikin mai sunan baba, hannunta ya kama ya yi wa wani irin mugun riƙo ya dubeta ya ce ‘Ki ka ce matata ta mutu, ta yaya? Ya za ayi ki ce aisha ta mutu? Ke kin san mutuwa kuwa”.

Ba riƙon da yayi mata ne ya sakata a cikin tashin hankali ba, abun da take gani a tattare da shi ne ya ɗaga mata hankali, sai dai alamu sun nuna babu wanda yake ganin abun da take gani sai ita kaɗai.

Mai sunan baba ne ya shiga ƙoƙarin ƙwace hannun rumaisa daga na Adam, amma ya kasa ruma kuwa ta ƙura masa ido tana wani irin kuka mai tsuma zuciya.

Ammi tamkar an dasata, ta ji maganar a bazata, ba ta taɓa tunanin abubuwa zasu cigaba da rikicewa haka ba.

Bashir ma ƙoƙarin ƙwace hannun rumaisa suke yi, amma riƙon da ya yi mata ba na wasa bane ba.

“Ki ka ce matata ta mutu? Ta mutu fa ki ka ce, ki tashi daga baccin da ki ke yi ki gaya mini gaskiya, ba Aisha ce ta mutu ba”.

Cikin kuka ta ce “Ka cikani kar ka ɓalla mini hannu, tun da na gaya maka abun da ka ke son ji” tayi maganar cikin kuka.

Bai iya cewa komai ba, sai ganinsa suka yi ya silale a ƙasa ya suma.

Sai a lokacin ammi ta samu hawayen idonta suka gangaro, mama da sauran mutanen wurin suka yi kan adam, sai dai ba ya motsi sam.

Da gudu Abubakar ya fita, sai gashi da likitoci sun biyo shi, suka yi umarni a kawo stretcher a ɗau adam a kai shi emmrgency.

Mai sunan baba kuwa bai motsa ba, sai ma rungume rumaisa da yayi yana shafa bayanta da sigar rarrashi, saboda kukan da take yi, ruma kuwa da ta ga an kawo stretcher an ɗora adam a rikice ta ce “Wai shi ma mutuwa ya yi? Haka anty aisha fa ta yi ta daina motsi bayan ta yi ta fitsarin jini, jininta ya ƙare”

Mai sunan baba ya sanya hannunsa ya rufe mata ido ya ce “Bai mutu ba in sha Allah, ki yi ta Addu’a”.

Gaba daya ta kasa nutsuwa, mutuwar aisha ce ta dawo mata sabuwa fil a idonta, duk masifar mai sunan baba, tausayin rumaisa ya mamaye shi, yarinya ƙarama tana ta gamuwa da iftila’in ƙaddara.

Ammi kuwa kuka ta din ga yi, kamar babu gobe ta yi iya ƙoƙarin ta amma ta kasa tawakalli ta jure, abu ka da mata abu na ‘ya’ya, mama na son ta rarrasheta amma ita ma ta ɓuge da kukan, daga baya suka bi bayan su Bashir, domin jin halin da Adam yake ciki, Yaya Abubakar ya tare su a hanya ya ce “Mama, ku je ku zauna in sha Allah babu wani abu, ga likitoci can sun rufu a kansa, ba za su bari ma ku shiga ba, ku yi haƙuri ku je ku zauna, ayi masa addu’a.
Yadda ammi take kuka zai tabattar maka da ba iya mutuwar ce ta dake ta ba, akwai tarin abubuwa cunkushe a zuciyarta.

“Innalillahi wa Innalillahi raji’un, la’ila ha illa la Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam” sune abubuwan da ammi ke ta nanatawa.

Mai sunan baba ya numfasa ya ce “A duk lokacin da muka rasa abu mai muhimmanci a rayuwarmu, sai mu tuna Allah ne ya bamu, kuma Allahn da ya bamu yafi mu son abun, kuma ya fi mu sanin muna son abun, dan haka addu’a zaki yi ki daina kuka” da ruma yake maganar, amma a zahiri ba iya ruma yake yi wa nasihar ba, har da ammi.

“Mai sunan baba” ruma ta kira sunansa.

“Na’am”

“Ka ga laifina da naƙi faɗa tun da farko? Ka ga shi ma zai mutu ya bar jaririn ko?”

“Ke da ki ka ce ba shi ne babansa ba, Meyasa ba kya so ya mutu?”

“Mai sunan baba” ta kuma kiran sunansa.

“Na’am” ya amsa mata.

“Idan sabir ya girma sai ya ji duk a gabana iyayensa suka mutu, idan ya tsane ni fa? bana son tunawa da mutuwar anty aisha, idan na tuna ji nake kamar na kashe kaina, da tsohon cikin nan fa dukanta suke yi, idan zasu dakeni ta hanasu, tun da suka taka mata cikinta take rashin lafiya, idan barde ya kawo mini abinci, tare muke ci, wataran ta ce in cinye ni ‘yar baby ce ita ta ci girma. Mai sunan baba na yi ta yi musu magiya su kai ta asibiti suka ƙi, kuma sun san ba ta da lafiya, na yi ta kuka ina roƙonsu ita kuma tana musu magiyar su karɓi kuɗin fansata a wurin mijinta su sakeni ni yarinya ce. A hannuna ta mutu bayan na bata ruwa, babu wani ɗan sanda da ya zo kuɓutar da mu, kuma sai yanzu zasu zo su dameni wai sai na gaya musu tana ina? Me za su yi a kai bayan ta bar duniyar, na tsani duk wani jami’in tsaro tunda har anty aisha ta mutu ba wanda ya kawo mana agaji, sai wasu ‘yan ta’addan ne suka ƙwace mu, wallahi duk wanda ya kuma tambayata wani abu ba zan faɗa ba, dan babu abun da za su iya yi a kai” tayi maganar cikin ƙunar zuciya tana rirriƙe hannun mai sunan baba.

A hankali ya kwantar da ita, ya toshe mata bakinta, saboda kamar nema take ta fita hayyacinta, adduoi ya din ga yi mata, har ya samu ta yi shiru, amma maganganunta sun ɗaga masa hankalin, shi daga nesa ma masu ciki tausayi suke bashi, saboda dakon cikin ma kawai ya ishe su, balle ace a taka mace da tsohon ciki, abun da ban tausayi.

Daga mama har ammi kowa sai goge hawaye take yi, sabir ne ya motsa ya fara kuka, mai sunan baba ya sanya hannu ya ɗauke shi ya fita da shi waje.
Ya ƙurawa yaron ido, sunan mahaifinsu rumaisa ta saka masa, ya tuna irin faɗi tashi da sadaukarwa da mama take yi a kansu, tun suna yara har zuwa yanzu da suka zama mutane ba ta daina ba, amma shi wannan ɗan bai san wannan ba, hasali ma tasa uwar tana kawo shi duniya ta mutu ta bar shi a dokar daji a hannun yarinyar da ita kanta ba ta san ciwon kanta ba, ta yi kwanaki tana gararanba da shi a daji babu ko wando a jikinsa ga ƙazantar haihuwa.
Wani irin tausayin yaron ya kama shi, ya rungume shi a ƙirjinsa yana shafa bayansa, wata irin ƙwallar tausayin yaron ta cika masa ido.

Abubakar kuwa tamkar wani daga cikin ‘yan uwansa ne suka suma aka kwantar da su, sai kai wa yake yi yana komowa, sai da ya ga lokaci na neman ƙure masa sannan ya ɗau jakarsa ya tafi.

Ko da su Usman suka zo mamaki ne ya kama su, ganin halin da su mama suke ciki, fuskokinsu ɗauke da damuwa, idon mama yayi ja saboda kuka, ammi kuwa har a lokacin kuka take yi.
Aliyu ne ya fara maganatuwa ya ce “Mama lafiya kuwa? Meyafaru ne?”

Mama ta girgiza masa kai ta ce “Lafiya ƙalau, ya kuka baro gidan an gama komai?”.

Usman ya ce “Mama, ya zamu ga kuna kuka kuma ku ce lafiya ƙalau, meyafaru?”

“Baban yaron nan ne babu lafiya, ashe mahaifiyar sabir da ake ta fama da rumaisa a kan ta yi bayani taƙi, ashe rasuwa ta yi, a hannun’yan bindigar ta rasu”.

Dafe ƙirji Aliyu ya yi yana Innalillahi wa Innalillahi raji’un, usman kuwa sak yayi duk da bai san matar ba, amma tausayinta ya kama shi.

“Mama rumaisa kuwa na da hankali, kuma shine ake ta fama da ita ta yi mursisi taƙi faɗa, saboda tsabar rashin kan gado”

“To ka san halinta da baƙin taurin kai, yanzun ma babana ne ya sakaya a gaba ya zare mata ido, amma yan sandan da suka zo suma ƙin kula su ta yi”.

Cikin damuwa usman ya kalli Ammi ya ce “Dan Allah ku yi haƙuri, wallahi yarinyar nan haka take sai a hankali wasu lokutan, bai kamata ta ɓoye abu mai girma irin wannan ba, ku yi haƙuri Allah ya jiƙanta da rahama ya sanya ta huta”.

Ammi ta ce “Amin, ku daina ganin laifinta a kan gaskiyarta take, yanzu ihu ake bayan hari, kamata yayi a kai musu ɗauki tun suna hannun ‘yan bindigar. Ba ta yi mini komai ba, babu abun da zan ce wa rumaisa sai fatan Allah ya rayata, ya shiryata ya tsareta na gode sosai da sosai”. Ta kai maganar tana kuka.

Usman cikin damuwa yake duban Ammi ya ce “Ki yi haƙuri, sai a gode Allah da ya kuɓutar da ɗan ta, ko ba komai za a kalla ace ga ɗan Aisha, kuɓutar yaron nan kawai ya ishi a godewa Allah, duk da ya karɓi uwarsa, komai yayi daidai ne, ki yi haƙuri, ki yi haƙuri Allah ya yafe mata, ya kula mana da jaririnta, ku yi haƙuri dan Allah kuka ba mafita bane, duk da dole ne jin zafi a duk lokacin da muka rasa makusanta mu da muke so, amma ayi haƙuri, duk jarrabawar da Allah ya yi wa bawa dai-dai ce”.

Duk da ba wasu shekaru ne da usaman ba, amma ammi har cikin zuciyarta ta ji daɗin yadda suka nuna damuwa a kan ta. Ta ce “Na gode Allah ya yi albarka”

Ƙasan zuciyar ammi kuwa, tashin hankali ne mai yawan gaske, dan al’umar sun yi dagulewar da ba ta san ta ina zata kamo bakin zaren ba.

Sai wajen azahar rumaisa ta farka, ji take kamar ba a gaske ta faɗa musu mutuwar Aisha ba, mai sunan baba ta gani zaune a gefen gadonta, yana juya Sabir yana murmushi gefen baki, mai sunan baba da kan ka ga dariyar sa aiki ne ja, ruma za ta iya cewa tun da ta buɗi ido a duniya ba ta taɓa ganin mai sunan baba ya ɗauki ɗan wani ba, wani irin daɗi ta ji da ta gan shi ɗauke da Sabir.
Ya dubi ruma ya ce “Sannu kin tashi?”
Ta jinjina masa kai alamar eh.

“Babu wata matsala dai ko?”

“Eh babu, baban mama kana son mai sunan babanmu ko?” Ya jinjina mata kai, a lokacin da yake gyarawa sabir kwanciyar sa a hannunsa, duk da ba wani ƙwarewa yayi a iya ɗaukar yara ba.

“Mai sunan baba dan Allah kar ku bari a rabani da shi, wallahi mamansa ta ce ta bar mini shi, da gaske nake ba wasa ba” kallonta kawai ya yi bai ce mata komai ba.

Ammi kuma na kan dadduma tana jin su, amma ba ta tanka ba.

Su Iman sun kira wayar ammi har sun gaji, dan ƙarshe ma kashe wayarta ta yi ma gaba ɗaya, dan ba ta san me za ta ce musu ba.
Adam kuwa ya shafe awanni a emergency ana fama, domin a ceto ransa, sam zuciyarsa ta ƙi bugawa yadda yakamata, bpn sa ma an kasa picking ɗin sa, ga numfashin sa ma yayi ƙasa fiye da yadda ake so, su kansu likitocin sun fara fidda rai, da ƙyar da taimakon Allah ya farfaɗo ya samu bacci, sai da ya yi baccin ne sannan aka fito da shi a ka bashi ɗaki.

Wunin ranar da su Aliyu aka yi ta sintiri a kan Adam, in an jima usman ya zauna ya yi ta yi wa ammi nasiha yana ba ta haƙuri. Sai da aka fito da shi, sannan aka ce ammi ta je ta ganshi.

Aka yi mata jagora har ɗakin da yake, dan har ta fara fitar da rai a kan sa, jin shiru-shiru ba a fito da shi ba, ta zaci ko shi ma ya rasun ne.

Ta tsaya tana ƙare masa kallo, ga robar ruwa nan a saƙale, shi kuma idonsa a rufe yana bacci.

Ta kama hannunsa a cikin nata, ta saka hannunta ɗaya tana shafa kansa ta ce “Na sani akwai wahala, amma ka ƙara jurewa, tun da na haifeka a kullum akwai fejin ƙaddara da kake buɗewa babi babi, da an wuce wannan sai wannan, na sani da wahala amma ka ƙara jurewa addu’a ta tana tare da kai yarona. Allah ya shiga lamarinka Adam, Allah ya cigaba da dafa maka ya baka ikon cin jarrabawa” tayi maganar tana rushewa da kuka.

Bashir ya ce “Ammi, addu’a nan dai, ita zaki cigaba, kar jininki ya hau fa, kuma yanzu mun gano bakin zaren, tun da ta tabatta ta rasu, sai mu san abun yi na gaba, Allah ya yi mata rahama”.

Aka din ga rarrashin ammi ana bata baki, daga bisani Bashir ya sallami direbanta, bayan magariba bashir ya ce zai mayar da ita gida, ya dawo ya zauna da Adam.

Mama ta ce “A’a, ita zata kwana a wurinsa”

Aliyu ya ce “Haba dai, saboda rashin kara ka wuni kana kaiwa da komowa, ita ma ta wuni a nan kuma ace ku kwana, ai ba wani abu, ko ni sai na zauna na kwana da shi”.

Ammi ta ce “Kar a ɗora muku ɗawainiya”

“Wallahi ba wata ɗawainiya, Allah ya bashi lafiya kawai”.

Daga gida har wurin adam kowanne tana son ta zauna, amma ya zama dole ta zaɓi tafiya gida, domin kuwa ba ta son kowa ya farga da abun da ya faru kan su sanar da kansu, ta san rashin zamanta a gidan, kan iya jefa zargi a wurin masu son ganin bayanta, dan haka a dole ta yarda Bashir ya ɗauketa ya mayar da ita gida.

Aikuwa a falo ta tarar da su Nusaiba a zazzaune fuskokinsu duk babu daɗi.

Nusai ce ta fara cewa “Ammi akwai matsala ne, tun safe mun kira wayarki ba kya ɗagawa hankalinmu duk ya tashi, yanzu uncle Jamil ya bar gidan nan yana nema ya ɗaga mana hankali wai ina takawa yake?”

Gaban Ammi ne ya faɗi, kar dai ya san wani abun ne, ta buɗe baki da ƙyar ta ce “Ya ce muku wani abun ne?”

“A’a kawai dai yana tambayar mu wai ina yake, baya samunsa a waya, ya je gidansa ma baya nan”

“Babu wani abu, ban zaci zan kai haka ba nima, amma ai gani na dawo”

Buutt baba uwani ta fito cikin girmamawa ta ce “Allah ya ja zamaninki, haƙiƙa yau mun wuni cikin zulumi da tashin hankali, mussaman da baki wuni a gida ba na tambayi su auta, sun ce ba su san in da ki ka tafi ba, ga wayarki ba ta shiga duk sun shiga damuwa kamar marayu”.

Ammi ta ce “Gani na dawo, uzuri ne ya riƙe ni, zan shiga in huta, kar wanda ya shigo mini”.

Iman ta ce “Ammina abinci fa?”.

“Na ci” ta faɗa a taƙaice ta wuce sashinta.

Nusaiba ta ja hannun iman, ta yi ƙasa da muryarta ta ce “Anya kuwa babu matsala?”.

Jiki a sanyaye Iman ta ce “Nima haka nake tunani, amma ta ce kar wanda ya je in da take balle mu ji”.

Nusaiba ta yi ajiyar zuciya ta ce “Bari mu jira zuwa Allah ya kaimu da safe mu gani”

Iman ta amsa da “Allah ya kaimu ya sa lafiya”

Tafiyar Ammi babu daɗewa Adam ya farka, Aliyu ya yi masa sannu, ya ɗan jinjina masa kai.
Ya yinƙura zai tashi, Aliyu ya taimaka masa ya tashi zaune, ya bashi ruwa ya sha.

Aliyu ya ce “Zaka ci wani abun ne?” Adam ya girgiza kai ya ce “Salla zan yi”.

Aliyu ya taimaka masa ya kai shi banɗaki yayi alwala, ya dawo da shi ya shimfiɗa masa abun salla, ya jero sallolin da suke kansa, sai dai bai tambayi Aliyu komai ba, can kamar an mintsine shi ya ce “Da gaske ƙanwarka take matata ta mutu ko?”

Jiki a sanyaye Aliyu ya ce “Haka ne, amma dan Allah ka karɓi ƙaddara ka yi haƙuri, ka ga da ƙyar likitoci suka ceto ranka, mahaifiyarka na cikin damuwa, kar ka sake sawa hankalinta ya tashi”.

Hawaye ne ya taru a idon Adam, ya haɗiye wani abu mai ɗaci, da sai da adams apple na maƙogwaronsa ya motsa sosai, cikin rawar murya ya ce “Jikina ya daɗe yana bani ta rasu, amma zuciyata ta ƙi aminta da hakan, ina jin zan sake ganinta, zan sake kallon fuskarta, ashe bankwana na yi da ita, na san ko gawarta bani da ikon gani, balle in binneta da hannuna ina yi mata addu’a da tuna biyayyarta da soyayarta, wayasani ma ko yar da gawarta suka yi ta lalace a haka, sun tozarta ni, sun tozarta iyalina. Amma ni musulmi ne, muslmi ne ni tabbas, dole na yi imani da ƙaddara. Ku rarrashi ƙanwarku, amma a gobe in Allah ya kaimu zan karɓi ɗana, zan je gaban sirikina, kuma uba a wurina, in sanar masa komai, ya ɗauki duk matakin da yake ganin ya dace da ni”.

AYSHERCOOL.
08081012143

*paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*b

Back to top button