Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 46

Sponsored Links

Haka suka cigaba da ƙulla mugunta kala-kala suna dariya.

Wunin yau Samha ba ta bi ta kan wayoyinta ba, sai yanzu ta nutsu, ta ɗau wayoyinta ta kunna, ta ajiye su a kan gado, ta shiga wanka. Daga shigarta wanka zuwa fitowar ta missed calls sun fi goma sha.

Mamaki ne ya kamata, tana shirin duba missed calls ɗin, kiran Fauziyya ya shigo wayarta. Ɗan ɓata fuska ta yi ta ce “Wai lafiya ake yi mini wannan kiran kamar mara gaskiya?”.

Fauziyya ta ce “Ke dalla can, idan ma wani rabon ne har ya wuce ki baki ɗaga waya ba, kawai kin wani kashe wayoyi”.

“Ke karki ɗaga mini hankali, hutu na zo yi dan me za a dameni? Ina jin ki”

Fauziyya ta ce “To, ai ni zancen ne ma ban san ta ina zan yi miki shi ba, abun farinciki zan ce miki, ko kuma tashin hankali da jimami, ko kuma abun ɗaure kai?”

Samha ta ɗan juya idonta ta ce “Fauzi, zan kashe wayata fa”.

“Katangar da ta daɗe da tsaye miki, ta hanaki cikar burinki ta rushe”.

“Kamar yaya kenan?”.

“Ƙanwarki ce ta mutu”

Miƙewa Samha ta yi, ji ta yi kamar ba ta ji dai-dai ba, wai ƙanwarta ta mutu.

“Ƙanwata wacce? Wace ƙanwar tawa?”

“Ahh, wacece ta sha gabanki ta hana cikar burinki na auren yayanmu, aisha ɗazu aka ce wai ta rasu a wurin haihuwa, a garin da ta je karatu, amma an dawo da jaririnta, amma dai kamar akwai wani abu da ake ɓoyewa ba a son a sani”.

Wata iska samha ta fesar ta ce “I hope ba ƙarya ki ke yi mini ba?”.

Samha ta ce “Ana ƙarya da mutuwa ne? Ki tambayi wanda ba sa yi miki ƙarya sai ki tabattar”.

“Am sorry, ba haka nake nufi ba, zan kiraki” ta kashe wayar ta cillata kan gadonta, ta hau sintiri a ɗakin.

To murna za ta yi ko kuwa jimami, wata zuciyar ta ce “Ke ina ki ka gata jimami, damar da ki ka daɗe ki na jira, Allah ya kawota a sama ki tsaya wani jimami? Yanzu hanya ta miƙe miki fetal, aiki kaɗan ya rage miki”.

Wayarta ta rarumo, sai dai ta rasa wa za ta kira ma, jefar da wayar ta yi, ta janyo akwatinta ta hau shirya kayanta, ko ba ta samu jirgi ba a mota zata koma gida gobe.

A daren ranar babu wanda ya runtsa a iyalin ammi, mussaman ita, da a kunnenta kishiyarta da facalolinta ke jifanta da miyagun maganganu.

Sabir kuwa tuni mama ta aike da shi gidan wata ‘yar garinsu da take aure a kano, matar kamar ƙanwa ce a wurin ammi, dan haka aka kai sabir can, duk surutun da aka din ga yi ba ta faɗi in da sabir yake ba.

Washegari ma haka aka ɗora zaman makokin aisha, samha kuwa tun da sassafe ta taho kano, sai dai ta rasa wani mood yakamata ta shiga, na farinciki ko akasin haka? Duk yadda ta so ta ji lamarin ya ratsata ta kasa, babban fatanta Allah yasa da gaske Aisha ba ta raye.

Sai da ta isa gida ta tarar da tarin mutane, sannan ta tabattar da gaske aisha ta mutu, tun daga waje ta fashe da kukan ƙarya, dan kar a fuskanci wani abu, kai tsaye ta nufi cikin gidan tana kuka kamar gaske.
Nan yan makoki suka din ga rarrahinta suna yi mata nasiha a kan aisha addu’a take buƙata ba wannan kukan da take yi ba.
Abu kamar gaske, Samha ta din ga kuka tana tumami, ana rarrashinta da ƙyar ta yi shiru, ta tafi ɗakin mamanta ta kwanta ta samu bacci.

Sai bayan la’asar sannan Hajiya Asama’u ta shiga ɗakin ta tashi Samha.

Ta dubi Samha ta ce “Ke yanzu Samha dan aishar ta mutu ki ka zauna kina wannan uban kukan kamar ni na muty? Yarinyar da ta hanaku rawar gaban hantsi a wurin mahaifinku, har wani kukan mutuwarta zaki yi?”.

Samha ta ɗan duba bayan mama, ta ji babu almar wani zai shigo, sannan ta dubi mama ta ce “Mama na dole ne, ko ba kowa ba wasu san da cewa ina son Adam, idan har na nuna ban damu ba, wasu ma ai sai su ce ina murna da rasuwarta ne, nima na dole ne kukan, amma mama ya aka yi ta mutu wai? Sannan ina ɗan da ta haifa ɗin?”

Mama ta kwaɓe baki ta ce “Mhmm, su suka san me suka yi mata dai, wai can in da ta tafi karatun a can ta zo haihuwa ta rasu, jiya nan suka zo da jaririn, ammma sun ƙi fito da shi yanzu, tun jiya ake fama amma Giwa taƙi faɗar in da yaron yake sai ɓoye shi take sai ka ce ciwo”.

Samha ta jinjina kai ta ce “Taɓ a nan aka yi mata sutura kenan?”.

“To waye ya ga gawarta, wai a can london ɗin ta mutu aka binneta, haka suka ce fa, ni ko yaushe ta yi cikinma oho, na ga dai tana can tana karatu, to can ya bita yayi mata cikin? Ko kuwa da cikin ta tafi Allah masani, saboda wata lalacewa ma, ita ya turata karatu ƙasar waje, ya zo yana nema ya haikewa iman”.

Samha ta girgiza kai ta ce “Mama ba haka aka yi ba, batun iman wannan wani abu ne da Mummy ta shirya shi, amma yadda abubuwan ne suke wakana, akwai wani abu a ƙasa, amma dai bari na yi wanka na sauya kaya”.

Ta tashi ta ɗau wayarta ta shiga banɗaki, lambar Khalifa ta nemo, ta kira shi, sai da ta kusa katsewa sannan ya ɗauka.

Ba sallama ba komai ya ce “Ya akwai labari ne?”

“Eh kusan haka, Allah ya yi wa matar adam rasuwa ne”.

“Na ji labari” ya katseta.

“A ina ka ji?”.

“Kin manta fitacce ne shi? Labarin duk ya karaɗe dandanlin sada zumunta”.

Ta yi ajiyar zuciya ta ce “Haka ne, sai dai an ce a can london wai aka binneta, ba a kawo gawarta ba, sai jaririnta kawai”.

Da sauri khalifa ya ce “What? Jariri kuma? How a wace maƙabartar aka binneta a London ɗin? Suwaye suka halarci jana’izar ta a can?”

“I don’t know, nima abun da na zo na tarar kenan” ta bashi amsa.

Khalifa ya yi dariya ya ce “Shikenan, kin zo mini da labari mai daɗi, wannan ma wani abu ne na yaƙar adam”.

“Amma dai ina fatan ba cutar da shi zaku yi ba, sannan ina son cire hannuna a contract ɗin nan, tun da ma dai wadda ta hanani rawar gaban hantsin ta mutu, ina ga na samu chance”

Khalifa ya ce “Haka ki ke gani?”

“Eh mana, babu abun da yayi saura ai”

“Ba zai yiwu ki saɓa yarjejeniyar mu haka kanki tsaye ba, dole ki kammala mini aikina”.

A fusace samha ta ce “Kai saurara, ba fa ‘yar ka ba ce ni, ka daina yi mini magana da isa kana bani umarni, ka kiyayeni” da haka ta kashe wayarta tana tsaki.

Kwanaki uku aka yi aka watse daga makokin aisha, sai dai adam sam baya hayyacinsa, kana kallonsa ka san a tashin hankali yake, ko abinci baya iya ci, haka yake tafiya gidansa, ya zauna ya saka kayan aisha a gaba yana kallonsu.
Ranar da suka rabu ya tuna, da zai yi tafiya, lokacin kwananta biyu da dawowa tana yi masa magiyar ya barta ta yi tafiya, ya din ga jan kumatunta yana yi mata dariya ya ce “Cikin nan naki ya sanya kumatunki ƙara cika, kuma sun fi daɗin wasa a haka” kwaɓe fuska ta yi za tayi masa kuka ta ce “Dan Allah ka mayar da maganata serious please ka bari na je”.

“Ki bari idan na dawo da kaina zan kai ki, kin ji fulanina”.

Kamar ƙaramar yarinya ta shiga turza ƙafarta za ta yi kuka ta ce “Dan Allah kar ta mutu ban je na dubata ba”.

Ya ɗan tsuke fuska ya ce “Bana son rigima fa, ke ba ki ga yadda cikinki ya tsufa ba, kin san hatsarine ki fita a san kin dawo, a sirri fa na bari ki ka dawo, tun da kin kasa riƙe kanki, sai kin dawo wurin mijinki”

Buɗe baki ta yi ta ce “Ni haka nace maka?”

Dariya yayi mata ya ce “Idan ma baki ce ba, yanayinki ya nuna ai, tun da ki ka dawo ko waje ban leƙa ba, soyayya kala-kala kawai nake sha, ki yi haƙuri jibi zan dawo in sha Allah sai na kai ki”

Idonta ne ya cika da hawaye, amam ya mayar da abun jokes, ya cigaba da ja mata kumatu yana kashe mata ido.

Da ya zo nan a tunaninsa ya durƙushe a kan gwiwoyinsa, yana kallon kujerar dressing mirror da ta zauna, suka yi wannan abu, da washegari ya ga message ɗin ta na ban haƙuri, a kan ba zata iya jiran dawowoarsa ba jikin kakarta ya tsananta da yawa.

Ya dinga zubar da hawaye yana surutai a hankali, wata irin kewarta tana ratsa shi.
Wani abu ne mai kama da bacci ya ɗauke shi, kawai sai ganin rumaisa ya yi a kan kujerar, tana zaune tana ta yi masa dariya, ‘Sarki mai koriyar alkyabba, ka ɗananiba dokinka” tayi  masa maganar tana murmushi, daga bisani ta taso ta nufo shi, tare da miƙa masa hannu, ya miƙa hannunsa zai riƙo nata, kawai yayi firgigit ya farka yana kalle-kalle. Ɗan tsuke fuska ya yi, ya tuna yadda ya din ga fama rumaisa tana yi masa gizo a baya, da ƙyar ya daina ganinta, kwatsam yanzu ma ta cigaba da yi masa gizon, ba dan ya ganta tare da ‘yan gidansu ba, to da babu shakka zai gazgata cewar aljana ce ita.

Kusan kwanaki ukun nan, rumaisa ta ƙi sakin jikinta, kusan kullum cikin kuka take a kan a dawo mata da jaririnta, tun mama tana ta tata har ta gaji ta ƙyaleta, abinci ma sai an yi kamar za a zaneta sannan take ci. ‘yan islamiyyarsu tawaga guda suka yo, har da malamansu suka sake zuwa dubata, amma mirsisi taƙi kulasu, taƙi magana.

Kwanaki huɗu da sallamar su, mama ta ce wa usman yakamata su je gida su yi wa ammi gaisuwar rasuwar aisha.
Mai sunan baba na jin jaka ya ce bai yadda ba, kar su zata wani abun suke nema a wurnsu, tun da sun yi musu gaisuwar a asibiti ya isa.

Mama ta ce “Kai ka san ba zamu je wurinsu domin neman wani abu ba, amma dai-dai gwargwado sun yi ɗawainiya da ƙanwarku, kuma babu laifi dan an bisu gida an kuma yi musu gaisuwa, shi ne abun da yakamata ai, tun da rashi suka yi. Shi dai mai sunan baba ba haka ya so ba, amma babu yadda ya iya haka ya haƙura ya ƙyalesu.

Mama ya shirya ya saka rumaisa ta shirya, ta ce usman da Aliyu suka raka su, ruma sai murna take ko ba komai, zata ga Sabir, sai jin daɗi take yi, ta shirya cikin riga da hijjabi, sannan ta kawo face mask ta saka.
Usman ya ce “Meye kuma na rufe fuska?”.

“Bana son a din ga kallona duk in da na je”

Ya ce “Ko kuma baki da gaskiya ba, ko kin yi wa wani laifi”

“Haba yaya usy, yaushe na dawo da zan nemi maganar ma”.

Yayi murmushi ya ce “Ashe kina sane ki ke neman maganar”

Gyara zaman hijjabinta ta yi, ba tare da ta sake magana ba suka tafi.

Gidan galadima kuwa, ammi ta karɓo sabir, su iman sun kewayeshi suna kallonsa, yaron haƙurinsa har yayi yawa, ba ya kuka sai ya ga dama, sai dai yayi ta bacci.
Babu in da ya bar adam, kamarsa ɗaya sak da adam, an yi masa wanka an shirya shi, nusaiba tana bashi madara a feeder.

Iman ta ce “Allah sarki rayuwa, Allah ya yi wa anty aisha rahama, mun ci buri sosai a kan haihuwar nan, duk da yadda ake ɓoyewa ba a son a san da cikin, amma tayi buri a kan cikin, kusan kullum sai ta turo mini hoton siyayyar da ta yi wa baby”.
Ammi ta ce “Rayuwar duniyar kenan, amma ba zan taɓa manta yadda aisha ta mutu ba, Allah ka kawo mana tsaro a ƙasarmu, ka ƙara kiyaye al’ummar musulmi” suka amsa da amin.

Adam ne ya yi sallama, suka amsa gaba ɗaya, su iman suka shiga gaishe shi, bai iya amsa musu ba sai jinjina musu kai kawai da yake yi.

Ya durƙusa ya gaida ammi. Ammi ta amsa masa tare da tambayarsa ya haƙuri.
Muryarsa a raunane ya ce “Alhamdilillah”

“Allah ya yi mata rahama, Sannan a cigaba da haƙuri duk mai rai mamaci ne”. Ya jinjinawa ammi kai, tare da zura hannunsa a aljihunsa, Saboda vibrating da wayarsa ta fara.

Bai san mai lambar ba, amma ya ɗaga tare da yin sallama.

Aliyu amsa sannan ya ce “Aliyu ne yayan rumaisa, mun zo mu yi maka gaisuwa ne, mun shigo cikin gidan bamu san ina zamu bi ba, a wurin bashir na karɓi lambarka”.

Adam ya ce “Ok babu damuwa, bari na zo gani nan” ya miƙe ya ce “Ammi ina zuwa”.

Rumaisa kuwa riƙe ƙugu tayi tana ƙarewa harabar gidan su takawa kallo, ga motoci gefe guda kuma ga burgar dawakai, ko ina sai manyan bishiyu da ƙanana, sai kalle-kalle take kamar ‘yar ƙauye, ga dogarai suna ta shiga suna fita, suna kaiwa da komowa a harabar.

Rumaisa ce ta fara hango adam ya nufo su, ya rame sai uban wuya, da dogon hanci, idon nan nasa jawur ya ƙaraso in da suke yana yi musu sannu da zuwa.
Risunawa ya yi ya ce “Mama sannu da zuwa, ya gida?”.

Cikin kulawa mama ta ce “Lafiya lau, ya ƙarin haƙuri?”

“Alhamdilillah”

Haka ya bi su usman duk suka gaisa, amma bai kula ruma ba, ita ma ba ya kula shi ba.
Ya ce “mu shiga daga ciki”

Rumaisa dama tun da ya zo yana fara magana, ta wani juya ƙeya, irin ba ta ma san yana wurin ba, sai dai kamar yadda ta ga ya rame, haka shima ya ga tayi rama, ta fi cikowa kwanaki uku baya da aka sallameta daga asibiti.

Yayi musu jagora zuwa ciki, rumaisa ta gwalala ido, ganin kayan alatun da ke falon ammi, ya wuce da su babban falon, ya ratsa da su zuwa falon ammi, wanda bai kai wanda suka baro ba.

Yayi musu iznin su zauna, ya kira ɗaya daga cikin barorin ammi, ya ce a karɓi su rumaisa. Ya ce “Bari na yi wa ammin magana”.

“To ina ɗana yake?” Ta yi maganar ba tare da ita kanta ta yi niyyar maganar ba.

Banza yayi mata bai kulata ba, sai da ya juya zai bar falon, sannan ya ce “Na kai shi koyo yadda ake gaida mutane”

Aliyu ya ce “Ai da abun duka ka samu ka zaneta wallahi, mara kunya kawai”.

Adam yana barin falon, rumaisa ta miƙe tsaye, ta sake zama a kan kujerar ta ce “Wayyo laushi, Innalillahi kujerar nan ta ji katifa yasin, kujerar masu kuɗi daban take, har na tuna wata kujera da na gani a gidansu wata ‘yar ajinmu, kujerar nan duk ƙashi, sai soso duk a waje, na ƙusa ta kusa tsarge mini mazaunai”

Usman ne ya talle mata ƙeya ya ce “Gaisuwa fa muka zo, ki ke yi mana surtu, shashasha” shiru ta yi ta sunkuyar da kanta ƙasa kamar ta Allah.

Mama ta ce “Rumaisa yaushe ki canza halaye zuwa na banza ne? Dama haka na koya miki rashin gaida mutane ko?”

Ta girgiza kai ta ce “A’a ki yi haƙuri”

Aka zo aka din ga jere musu kayan abinci kala-kala, da na sha, ita dai rumaisa burinta ta ga Sabir.

Adam ya je ya tarar da ammi ta aiki su Nusaiba, daga ita sai sabir a ɗakin, ya ce “Ammi kin yi baƙi”.

Ammi ta ce “Suwaye, na ce duk wanda yayi gaisuwa ya tafi ina son hutawa ne”.

Rasa mai zai cewa ammi yayi, dan ko sunan rumaisa ba ya son kamawa, ya ce “Yarinyar nan ce, da mamanta da yayyenta suka zo yi mana gaisuwa”.

Cikin rashin fahimta ammi ta ce “Wace yarinyar kenan?”

“Wannan yarinyar da ta zo da Sabir” Sabir ɗin ma da ya faɗa ji yake kamar ya kwafsa, kasancewar rumaisa ce ta sanya masa sunan.

Cikin fara’a ammi ta miƙe tana faɗin Allah sarki.

Adam ya karɓi Sabir a hannun ammi, da niyyar ya gwanyawa rumaisa, suka fito falon.

Ko ammi ba ta kalla ba, ta miƙe tsaye tana jiran Adam ya ƙaraso ta karɓi Sabir, amma ya canza hanya ya yi wani wurin. Ai ba su ankara ba rumaisa ta bi bayansa da gudu tana “Ka tsaya in ɗauke shi, ka zo ka bani ɗana”.

Back to top button