Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 50

Sponsored Links

Mikewa Mumy tayi tana kallon Anty khadijah a mugun tsorace tace “Ciki kuma khadijah? Ciki fa??” Da kyar Anty khadijah ta juyo kai tana kallon Mumy, Aliyu ya juya ya fice daga ward din, mumy ta fashe da kuka tana kallonta tace “Ciki fa Khadijah, innalillahi wa inna ilai hi raji’un, turr da halin ki Khadijah, tsofe tsofe dake khadijah” Mumy ta xauna kan kujera ta dafe kai tana kukan abun kunyan da Anty khadijah ta dauko masu, Aliyu ko minti biyar bai kara a cikin asibitin ba ya bar ma saleem makullin motarsa ya hau motar haya xuwa Kaduna, don gaba daya hankalinsa na sudais, har ya isa gida kuma yana mamakin Anty khadijah, wai ciki… jiki a sanyaye ya wuce sama xuwa bedroom dinsa, har sannan baby na xaune dakin kusa da sudais dake bacci, tana ganinsa ta mike tace “Yayanmu ya jikin Anty khadijahn?” Ba tare da ya kalleta ba yace “Da sauki” daga haka ya kai hannu goshin sudais ya ji babu xafi kamar daxu da safe, ya kalli baby yace “Bai tashi ba tun daxu?” Ta girgixa kai tace “Bai tashi ba, amma yana ta kiran Anty cikin baccin” shiru yyi na d’an lkci sannan yace “Make him a cup of tea” juyawa tayi ta fita dakin, Aliyu ya xauna gefen gado, shi dai ya kasa cire mamakin da yake yi a ransa na Anty khadijah wai ciki…. Sosai Shureim ya sake jiki gidansu Khaleel cikin lkci kankani suka saba da yaran kanin khaleel mata da ke hutu a gidan, duk da kusan sun fi yin larabci, Ummun khaleel ma ta dinga jan sa jiki don yaron ya kwanta mata sosai. Yana tsaye ya jingina da mota idonsa a kan gate din gidan har ta fito, Hijab ne har kasa jikinta, ba tare da ta yarda sun hada ido ba ta karaso ta tsaya nesa da kusa da shi ta rungume hannayenta tace “Ina kwana” yana kallonta murya can kasa yace “Lafiya lau Amira, ya gidan?” Tace “Lafiya lau” yana shafa kai yace “Sorry ban xo ba jiya kuma ban kira ba, but we communicated with Dr Ayman ya gaya min komai, you don’t worry idan bai dawo da shi ba ko xuwa gobe I will personally meet his mum, kiyi hakuri kin ji, let just take everything easy because of the mother Amira, consider her generosity to you, kar ta ga baki mata kara ba” Ita dai Khadijah bata ce komai ba tana wasa da xoben hannunta, Ya d’an yi shiru kafin a hankali yace “ina shureim?” tace “Yana gidansu Dr Ayman” kallonta ya dinga yi yace “Me yake can?” Tace “Ya dai tafi da shi ne kawai” yace “Ohk that’s nyc” shiru ne ya biyo, “We need to talk Amira” abinda ya fadi kenan yana dubanta da kyau, a karo na farko tayi masa kallon cikin ido tace “About what?” Jikinta ne yyi sanyi tuna baya da tayi, their moment together lkcn tana laulayi, lkcn da ta fara samun sauki, lkcn da cikinta ya fito har xuwa lkcn da ta haihu, shi ma kallonta yake ko kiftawa babu, taji kamar ta fara hawaye a wajen, murmushi yyi ya dauke kai a hankali yace “Yanxu kin girma sosai, kilan kin fi karfina ko Amira, may be I am not ur class….” Sauke idonta tayi daga kallonsa cikin sanyin murya tace “Ban gane ba” openly yace “Xa ki iya auren mai mata?” Bata kallesa ba bata kuma ce komai ba amma sai da gabanta ya fad, wani murmushin ya kuma yi yace “That says it all, you are not interested” sai a sannan ta daga kai ta kallesa tayi murmushin karfin hali ita ma tace “I know marrying u is not even enough in biyaka abinda ka min a rayuwa barrister, but…” Ya katse ta da sauri yace “But what?” A hankali kuma a sanyaye tace “It looks as if you are afraid of ur wife, ba lallai ta bari ka kara aure ba…” lkci daya mood dinsa ya canxa yace “Says who Amira?” Ta sauke idonta kasa tace “Gashi nan saboda ita mun hadu after six years a super market amma kayi kamr baka taba sani na ba, kuma saboda ita ka kasa kirana jiya kana gida ka min common tambaya….” Ya dakatar da ita yace “Sai hakan ke nufin ina tsoronta kuma Amira, ba tsoro bane ina gudun fitina ne kawai, kema kin san it will look somehow in maki magana a mall ranan muna tare da ita kin san halin ku mata da kishi, a gida kuma it’s not proper in yi waya dake….” Khadijah tayi murmushi tace “Upon ur profession? Ta mance wa ta aura ne?” Shiru yyi yana kallonta, a hankali yace “Kawai dai ki ce baki ra’ayina Khadijah” Tana wasa da xobenta cikin sanyin murya tace “I didn’t say that Barrister, just that bayan duk wahalan da na sha a rayuwa bana son inyi aure kuma in kasa samun kwanciyar hankali, kasan lalurata, ina da ciwon xuciya, ni yanxu ko kadan bana son hayaniya…. Ban san me yasa ba” tana magana ne hawaye cike idonta, “Ban da haka bani da abinda xan iya biyanka da shi a duniya barrister da ya wuce in amince da auren ka a yanxu, but am afraid…” hawaye na sakko mata ta kai karshe, Lumshe ido yyi na few seconds kafin ya bude ya ga kallonsa take, da sauri ta sunkuyar da kanta yace “Kar ki damu da matata Amira, beside ba gida daya xa ku xauna ba” ita dai bata ce komai ba amma gaba daya hankalinta a lkcn ya tafi kan khaleel…, lkci daya jikinta yyi mugun sanyi, A hankali ta ji yace “Plss Amira…” Ta daga kai a sanyaye tana kallonsa. Mumy ce xaune tayi tagumi nesa da Anty khadijah dake ta ihu tana cewa xata mutu axaba ya isheta a cire mata kafafuwan ta huta damuwa ce sosai tare da Mumy tayi kukan takaici har ta gaji wannan wani irin bala’i ne, da ta tuna wai ciki gare Anty khadijah sai ta fashe da kuka sosai, da kyar ta tashi jin ring din wayarta dake ajiye cikin jaka ta bude ta fiddo wayar ta daga ta kai kunne hade da sallama, “Don Allah ina magana da Hajiya Fatima ne?” Mumy tace “Ni ce” matar tace “Alhmdlh, Hajiya Laure ce, dalilin kiranki yanxu shine tun jiya nake neman Hajiya Khadijah a waya bana samu, ga yar ta da ta bari nan kuraje sai ruwa suke suna fashewa, don Allah a turo a dauketa gaskiya, ni ban san wani irin ciwo take ba ni mai yara a gida, don Allah a xo a dauke ta gidana don ko tashi bata iya wa” Mumy ta kasa cewa komai jikinta ya kara mutuwa, cike da karfin hali tace “Toh xa a xo a dauketa, hatsari khadijahr tayi jiya” Hajiya Laure tace “Hatsari kuma? Toh Allah ya kiyaye, ni dai a xo a dauke yar nan gidana babu ruwana” daga haka ta katse wayarta, Mumy ta dinga goge hawayen idonta, bayan wani lkci ta kira Aliyu ta ji ko xai je dauko ikliman, yana dagawa cikin sanyin murya tace “Abuturrab,” yace “Na’am Mumy, ina yini” tace “Alhmdlh, ya jikin yaron?” Ya d’an yi shiru kafin yace “Muna Asibiti fa Mumy” tace “Asibiti kuma, jikin ya ki ne?” A hankali yace “Toh da sauki, but xa a duba kansa ynxu to check if everything is okay” Tace “Ikon Allah, to Allah ya basa lafiya” yace “Amin mum” daga haka ta katse wayar ba tare da tayi masa maganar ikliman ba ma, Aliyu ya ajiye wayarsa yana kallon Sudais da aka cire ma oxygen a lkcn, Baby na share idonta a hankali tace “Yaya ko xaka kira mum dinsa, kaga ita yake ta kira fah” ya kalli kanwar tasa yace “I don’t have her contact” tace “Toh barristern nan da suka xo tare fa?” Shiru Aliyu yyi tunawa da yayi ya dau number khaleel a wayar Farouq ranan, daukar wayarsa yyi ya fiddo number yana kallo, da kamar xai yi dialing sai kuma ya fasa ya mike yace “I will go get her now” Da makullin motarsa ya fita xuwa parking lot, yana shiga motarsa ya nufi gidansu Khadijah, yana isa yyi parking ya fito ya nufi gate, a hankali ya tura ya ji ma a bude yake ya shiga, kamar bai son tafiyar yake yi har ya isa entrance din cikin parlorn, ya kai hannu ya danna bell, Khadijah dake kitchen tana girkin lunch ta fito kitchen din da sauri, bata damu da ta sa Hijab kan kananun kayan jikinta ba don a tunaninta Nanny ce ta dawo daga kasuwa, bude kofar tayi suka yi ido hudu da Aliyu, tayi still a wajen na yan sakwanni kamar an dasa ta, da sauri ta bar bakin kofar tayi hanyar daki ya bi ta da kallo, can ya sa kafa ya shiga parlon ya xauna kan kujera, kan gado Khadijah ta fada tana maida numfashi ga gabanta dake ta faduwa, Kar umma ta fito parlorn babu Hijab ya sa ta mike da sauri ta shiga dakin Umma, xaunawa tayi har ta gama waya kamar xata yi kuka tace “Umma kun ga abinda nake gudu kenan koh? Meye ya kawo Aliyu gidan nan yanxu, why will he come to this house kuma ba tare da yarona ba” Umma na kallonta da mamaki tace “Yana ina?” Fuska daure tace “Yana parlor mana” Umma tayi shiru, sai kuma tace “Toh ai sai ki tsaya ki ji me ya kawo sa koh” Khadijah ta kara hade rai sosai tace “Umma ni idan xan koma UK da yan biyun xan tafi gaba…” Shiru tayi a sanyaye tunawa da tayi ai a can ma ta fara jam da Aliyu, Umma tace “Ki tashi kije ki ji abinda ke tafe da shi, ni kar ki min fitsara” rai ba dadi Khadijah ta mike ta fita, labewa tayi da bango a corridor tana kallonsa, the mouth, the nose, the eyes, worst of all the face… Sosai jikinta yyi mugun sanyi, wayarsa kawai yake dannawa idonsa a kai, kamar ance ya waiga suka hada ido gabanta yayi mugun faduwa, tayi saurin dauke kai, shi ma hakan yayi, ta hade rai bbu yabo babu fallasa tace “Me ka xo yi gidan nan malam?” Ba tare da ya kalleta ba yace “Ur son, yana son ganin ki” Bata san lkcn da ta fito parlorn ba ta taho gabansa tace “Yana ina?” Ya mike bai kalleta ba yace “At the hospital” lkci daya hankalinta ya tashi tana kallonsa tace “Har yanxu jikin nasa?” Aliyu ya girgixa kai ba tare da ya kalleta ba still yace “Da sauki” daga haka ya nufi kofa yace “Ina jiran ki a waje” juyawa tayi da sauri ta koma dakin umma cike da damuwa tace “Umma wai asibiti xa mu je wajen Sudais” Umma tace “Asibiti kuma, an maida shi asibitin ne?” Gyada kai tayi kamar xata yi kuka tace “Ehh” Umma tayi shiru na d’an lokaci sannan tace “Toh ki je, Allah ya kiyaye, idan ba a sallamesa ba xuwa anjima sai in taho nima, ki tafi da wayar ki xa mu dinga magana” Khadijah tace “To” sannan ta koma dakinta ta dau waya ta fita, Aliyu na mota yana jiranta har ta fito, ta hade rai ta bude front seat din ta shiga ta rufe, shi dai bai ce komai ba ya tada motar yyi reverse suka bar anguwar, danne danne kawai take a wayarta, lkci daya tayi dialing number Khaleel ta kai wayar kunne, yana dagawa yace “Ya aka yi Ummu twins?” Ta sauke idonta kasa tace “Xan je clinic gun sudais ne yanxu” yace “Clinic, did they call you?” Ta gyada kai a hankali tace “Ehh” yace “Ohk toh Allah ya tsare, ke da waye?” A takaice tace “Driver!” yace “Ohk, text me the hospital name yanxu” tace “Toh” daga haka ta katse wayar, shi dai Aliyu driving dinsa kawai yake, bayan wani lkci fuska daure kamar ana tilastata tace “Wani asibitin ne?” Ba tare da ya kalleta ba yace “Ban sani ba” wani kallo ta dinga masa ganin ko waigo wa bai yi ba tayi tsaki, har suka isa asibitin babu wanda yace komai cikinsu, bayan yyi parking ya bude motar ya fita ya nufi entrance din clinic din, sosai ta ji ranta ya baci ta fito motar ta rufe tana hararansa, ba tare da ya juyo ba yyi locking motar da makullin hannunsa, sai da ta karanta sunan clinic din sannan ta bi bayansa tana turo baki, tuni ya shige ward kafin ta shigo reception, ta dinga kalle kalle ta rasa inda ya shiga, gaishe da nurses dake wajen tayi, wata nurse tace “Tare ku ke da Dr Aliyu?” Khadijah ta gyada mata kai, nurse din tace “Ohk ki je daki na biyar nan ya shiga” Khadijah ta mata godiya ta bi hanyar da ta nuna mata tana kirga wards din har ta xo na biyar, Aliyu na tsaye jikin window yana kallon result din scan da aka ma Sudais Khadijah ta shigo dakin, tsaye tayi bakin kofa tana kallon sudais dake kwance, Baby na ganin ta ta mike, a sanyaye Khadijah ta karaso ciki, baby na murmushi tace “Sannu da xuwa Iman” Khadijah ta mayar mata da murmushin tace “Ya su mumy?” Baby tace “Suna lafiya” tsayawa Khadijah tayi tana kallon Sudais dake bacci restlessly, har ya rame daga jiya xuwa yau, Baby tace “Jikin da sauki ma” Khadijah bata iya ta ce komai ba tana kokarin ganin hawaye bai zubo mata ba, Baby ta ja mata kujera tace “Ki xauna” kamar ta san da kyar take tsaye dama, Khadijah ta xauna tana ta kallon yaron nata, Aliyu ya juya ya fita daga dakin, text din sunan asibitin ta tura ma khaleel. Ba a dau lkci ba wani Dr ya shigo ward din Khadijah ta dinga kallonsa, allura biyu yyi ma Sudais, Khadijah ta mike da sauri jin ko bude ido bai yi ba, tana kallon likitan hankali tashe tace “Dr ban ji yyi kuka ba kuma yana kukan allura” yar dariya likitan yyi yace “Toh ai ba dole yyi kuka ba madam” daga haka ya juya ya fita, ta dinga kallon sudais xuciyarta na bugawa, ita kanta Baby mikewa tayi tana kallonsa, Khadijah ta kai hannu tana tashinsa, sai da ta jijjiga sa sosai ya bude idonsa a hankali, yana ganinta ya rike hannunta murya can kasa yace “Anty don’t leave me plss, where is shureim” Sosai ta ji hankalinta ya kwanta ta taba jikinsa ta ji bbu xafi, ta xauna kusa da shi cikin sanyin murya tace “Get well soon plss son” hawaye cike idonta ta kare maganar yace “Ohk, Anty shureim” ta kwantar da murya tace “Xai xo anjima ka ji” ya gyada mata kai, Aliyu ne ya shigo dakin, yana kallonsu yace “why did you wake him?” Ba tare da ta kallesa ba ta hade rai a takaice tace “Because he is my son” tsayawa yyi yana kallonta, Baby jikinta yyi sanyi ita ma, ta mike kawai ta fita daga ward din, Aliyu ya dau wayarsa ya fita shi ma, Mumy ya kira bayan ya gaisheta yace “Mumy ina jin fa dole xa a fita da yaron nan waje” cikin tashin hankali Mumy tace “A fita da shi kuma? Jikin ya ki ne har yanxu Abuturrab” yace “Akwai matsala ne scan da aka yi masa, just pray for him mumy” Mumy ta kasa cewa komai Aliyu ya katse wayar, Khadijah sai kallon sudais take da ya kara rufe ido kamar mai bacci, ta dau waya ta kira khaleel, bugu biyu ya dauka, tace “Plss ka d’an xo da Shureim” yace “Ohk, let me go back to pick him” Cikin minti sha biyar khaleel ya kirata yana asibiti, Khadijah ta mike ta fita don shigowa da shi, da gudu Shureim ya taho ganinta da yayi tun daga nisa ta bude hannunta ta rungume sa, “Anty plss I want to see sudais now” ta shafa kansa tace “You wil see him sweetheart” daga haka ta mike tana rike da hannunsa ta kalli Khaleel dake kallonsu, ta d’an yi murmushi ta sauke kanta kasa tace “Ina yini” yace “Lafiya lau ya mai jikin?” Tace “Da sauki, ya ma koma bacci yanxu” daga haka ta fara tafiya rike da shureim ya bi bayan su har suka isa ward din, tun da Khaleel ya shiga yake kallon sudais har ya karasa kusa da shi, ya juya yana kallon Khadijah yace “Yaushe aka kawo sa asibiti?” Ta bude hannu alamar bata sani ba, yace “Wa ya kawo sa?” Ta turo baki tace “Shi ya kawo sa” khaleel yace “Ina yake?” Tace “Kilan yana office” juyawa yayi ya fita ta bi sa da ido, can ta mayar da dubanta kan sudais, shureim na kusa da shi kan gadon da damuwa yake cewa “Sudais are you still sick? Plss get well soon so that we can play together, I am missing you” Kallon sa kawai Sudais yake bai ce komai ba, hawaye ya cika idon Khadijah ta karasa kusa da shi ta kamo hannunsa tace “Sudais talk to ur brother he is missing you” Sudais ya gyada mata kai amma bai ce komai ba, ta xauna kujera hawaye na sakko mata tace “Plss get well son, I want to see u hale and hearty once more” Aliyu na rubuce rubuce yana duke gaban table dinsa khaleel ya shigo, kallon kallo suka tsaya yi, can khaleel ya karasa cikin office din yace “What exactly is the little boys problem now?” Ba tare da Aliyu ya sake kallonsa ba ya dau takardan scan da aka yi ya mika masa, Khaleel ya karba yana dubawa, shiru yyi na yan dakiku kafin ya kalli Aliyu yace “So what next?” Mikewa Aliyu yyi yace “We will be going to India tomorrow” kallon khaleel yyi yana kwasan takardun da ya gama rubutu a kai yace “Don’t tell her anything about it….” Kallonsa kawai khaleel yake bai ce komai ba, can ya juya ya fita daga ward din ya koma reception ya xauna, kai kana ganinsa kasan he is disturbed, Khadijah tayi ta jiran dawowan khaleel amma shiru, taji duk hankalinta ya tashi, kallon Shureim dake ta damun sudais din da magana ta yi xata ce ya daina damunsa taji muryar sudais a hankali yace “Anty tell him to let me I want to rest” idonsa a rufe yake maganar, Ta kalli shureim da damuwa tace “Leave him plss shureim ka ga ba shi da lafiya” Shureim ya bata fuska yace “Then I will rest with him too” ita dai bata ce komai ba, wasu likita biyu da nurse daya suka shigo ward din, daya ya sauke Shureim kasa daga kan gadon, wasu alluran likitan ya kara masa guda biyu, daya likitan yace “Xa a canxa masa daki yanxu madam….” Juyawa Khadijah tayi ta fice daga dakin xuciyarta na bugawa, Khaleel na xaune har sannan a reception, bai jira ta karaso ba ya mike ya fita kamar bai ganta ba, sama ta wuce ta bude office din Aliyu, tsaye ta gansa jikin window ya juyo suka hada ido, ta isa kusa da shi hawaye cike idonta tace “Tell me what’s wrong with my son Aliyu, ka gaya min plss” ta fashe da matsanancin kuka tana kallonsa, ya dauke kai yace “He will get better soon, it’s just a minor illness” ta tsayar da kukan da take cikin sanyin murya tace “Are you assuring me??” Yana kallon kwayar idonta yace “Sure, Allah xai basa lafiya” juyawa tayi ta nufi kofa ya bi ta da kallo. Karfe Biyar na yamma Umma ta xo clinic din, hankalinta ya tashi sosai ganin Sudais ita ma, Khadijah dake xaune cikin sanyin murya tace “Umma kawai xaxxabi ne, Allah xai basa lafiya” ita dai umma bata ce komai ba, abincin da ta kawo ma bai ci ba, khaleel yace ta bar sa anjima xai ci ana basa abinci a drip, Da ladabi Aliyu ya shigo ward din ya gaida umma ya fita, har aka yi isha suna clinic din, Aliyu ya samu khaleel dake xaune waje yace “You tell her to go home it’s getting late” Khaleel bai kallesa ba yace “Allow her to be with her son, kuma it’s better ka gaya mata matsalar yaran sai ta bi ku xuwa India gobe” Aliyu bai ce komai ba na kusan minti daya, can ya juya ya bar wajen, tara saura umma ta wuce, babu yanda Khadijah bata yi da shureim ya bi ta ba amma ya ki, haka umma ta tafi ta bar sa. Khadijah na xaune ta jingina da gadon da sudais yake misalin goma saura wayarta ya fara ring, dagowa tayi tana kallon wayar, ta dauka a hankali ganin sudais ke kiranta ta daga ta kai kunne cikin sanyin muryarta tayi sallama, muryar mace taji tace “Amira koh?” Khadijah tayi shiru tana saurarenta, tace “Toh jiddah ce, matar Barrister Aliyu, ina son sanin meye hadin ki da mijina tun da girma da arxiki” mamaki ya cika Khadijah, jiddah tace “Ohh shiru xa ki min kina ji na?” Khadijah tace “Toh uwata ce ke da baxan yi shiru ba, why not ki tambayi shi mijin naki meye tsakaninmu xa ki kirani, ko kin mance profession din mijin naki” wani tsawa jiddah tayi tace “Kee maxa kalmashe kalamanki, kinsan wacece ni, na fi ki sanin aikin mijina malama, sannan mijina baya kiran client dinsa baya kuma saving numbers dinsu sai dai su kira sa suyi introducing kansu ke ko gashi duk shi ke kiran ki kuma ku dau mintuna masu yawa kuna magana, halan baki san yana da aure bane, baki san mijin aure bane?” Tsaki Khadijah ta ja tace “Kan ki ake ji, wannan kuma sai ki je ki samu mijin naki ki tambayesa” daga haka ta kashe wayarta, jiddah ta kirata ya fi sau hudu bata daga ba lkci daya taji xuciyarta ya fara mata xafi duk da ba wai hayaniya tayi da ita ba, taji ranta yyi mugun baci. Wata nurse ce ta shigo ta nuna mata wani spare gado dake ward din tace ta kwanta, khadijah ta mike tana kallon Sudais duk da bata son barin sa, ta kai hannu goshinsa still taji ba xafi temperature dinsa is normal, ya bude idonsa a hankali, har ranta ta ji dadin hakan don har umma ta xo ta tafi bai bude idonsa ba, xata yi magana ya riga ta yace “Anty ina Shureim?” Tace “Yana waje tare da uncle” ya bata fuska yace “Me yasa ya tafi?” Ta kwantar da murya tace “You said he shud allow you to rest, shine ya tafi da uncle” a hankali yace “Anty kice ya xo plss, I want to tell him am sorry” jikinta yayi sanyi tace “Toh xan kira sa yanxu” daga haka ta nufi kofa tana waigo yaran da ya bi ta da ido,

Back to top button