Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 69

Sponsored Links

A hankali Khadijah ta bude idanuwanta ta sauke kan Khaleel dake xaune gefenta Aliyu na tsaye daga gefensa, Umma ta taho gunta da sauri ganin xata mike xaune ta riketa da damuwa tace “Sannu Khadijah, how are you feeling now?” Kirjinta kawai ta nuna ma Umma hawaye na xubo mata, Umma tayi kasa da murya a sanyaye tace “Xai daina in sha Allah, be strong daughter” Baby dake tsaye gefe daya ta karaso ta xauna kusa da ita tana kallonta ta kamo hannunta, rasa abinda xata ce mata tayi, lkci daya ita ma hawaye ya kawo idonta, Khaleel ya mike ya fita ward din sai gashi sun dawo tare da likita, Juyawa Aliyu yayi ya fita, likitan ya gama dubata suka fita tare da Khaleel xuwa office din sa. A sanyaye Umma tace “Kin dai ji abinda likitan ya ce maki, Kar ki sake kukan nan don Allah saboda lalurar ki” Khadijah bata ce komai ba ta kai hannu tana share hawayen idonta, bude kofar ward din aka yi Sudais ya shigo, tsaye yayi nan bakin kofar yana kallonta, A hankali Umma ta dauke kai kanta daga kallon da take masa, Baby ta hade rai kamar bata taba dariya ba, Tun da Khadijah ta kallesa sau daya bata sake yarda ta dago ba hawaye ya dinga xuba idonta, ya iso har kusa da ita, da kyar yayi gathering courage yace “Amira….” ta fashe da kuka sosai tace “Am begging you ka rabu da ni pls Aliyu ka tafi, My heart is aching at the sight of you, kayi hakuri ka wuce… let me rest plssss” cikin matsanancin kuka ta kare maganar, Yana mata wani kallo yace “Amma in har maganganun da Jiddah ta fadi maki sun yi tasiri xuciyar ki ba ki min adalci ba Amira, for good two years na boye ma mahaifiyata na ajiye ki gidana ko da kuskure ban taba sanar da ita ba ban taba tona maki asiri ba, hatta frnds dina ban da Yusuf babu wanda yasan labarin ki, sai a yanxu kike tunanin xan fallasa sirrinki, Kuma in rasa warce xan fada ma sai matata da ko kadan ba dadin xama da ita nake ba, am I that daftt??” Ya girgixa kai cikin bacin rai yace “I never expect such from you Amira, I thought ke me fadi ma wasu cewar makirci ta xo tayi displaying gidan ku….but I was mistaken” kasa ci gaba yyi ya juya ya fice daga ward din, Khadijah ta hade kanta da gwiwa tana kuka kamar an aikota, Baby dai ta kasa cewa komai duk jikinta yayi sanyi sosai, Umma ta sauke ajiyar xuciya tana kallon baby tace “Hope kin ji maganata ya fito ko, Ni nasan makirci ne kawai na mace, I know baxai taba yin haka ba, baxai xaunar da ita yayi mata tsarin da ta xo tayi ba, she set him up kawai saboda kishi….” Umma na magana tana goge hawayen dake xuba idonta, ta ji tausayin Sudais sosai, “Khadijah idan kika ce kin fasa aurensa kamar yanda kika yi ikirari before passing out kin yi butulci, baki kyauta masa ba, Kuma kin nuna ta ci nasara kenan matar tasa” Khadijah ta dago cikin kuka tace “Wayyo Umma kashe ni xata yi a gidan, baxan iya auren mata miji ba ni dai, ku rufa min asiri, Umma kin ji yanda xuciyata ke min ciwo, na hakura da auren gaba daya I prefer dying a spinster” Rungume ta Umma tayi tace “Ba abinda xa a fasa daughter, kuma tayi kadan ta kashe ki, we will prove her wrong, ta xo tayi masa sharri duk don kice kin fasa to xa a nuna mata iyakarta in sha Allah sai kin aure sa, sai in Allah yayi shi din ba mijin ki bane dama, Amma babu abinda xa a fasa” Tun da Sudais ya fita ward din ya tafi kan wani kujera a waje ya xauna ya jinginar da kai ya lumshe ido, he was totally lost and sad, Bai taba tunanin makircin jiddah ya kai haka ba, ya rasa gane inda ta samu lbrin Khadijah, yasan Yusuf baxai fada mata ba, infact ta ina ma xa su yi communicating bayan bata da number sa bashi da nata, Babu abinda ya kara sanyaya masa jiki sai yanda Khadijah of all people ta yarda da abinda jiddah taje ta fada, ai Ita mai ce ma mutane sharri jiddah ke masa, but she is among the believers, Khaleel dake jingine da motarsa yana ta kallonsa, tausayi ya basa sosai, and he knows what he is feeling, khaleel ya fi minti biyar yana jinjina kwarewar matar Sudais a fannin hypocritical action, she is just perfect, a hankali ya taka ya isa har inda yake ya xauna gefensa, Sudais ya bude ido a hankali jin mutum gefensa, Khaleel ya cire glasses din idanuwansa in a low voice yace “Sure it hurts…” Sudais na kallonsa da idanuwansa da suka sauya launi cikin sanyin murya yace “Can I confide in you Dr Ayman?” Khaleel na kallonsa ya gyada kai yace “Sure” Gyara xama Sudais yyi yana dubansa ya fara magana cikin sanyi…. Umma ce ta fito haraban hospital din bayan kusan minti sha biyar, duk iya kalle kallenta bata hango ko wannensu a nan ba hakan yasa ta koma ciki don dauko wayarta, Sudais ya dinga kallon Khaleel da yayi shiru idonsa a kasa, Sudais yace “Don’t forget I asked you before letting out my mind to you doctor, ka gaya min gaskiyar abinda ke ranka” Sai a sannan Khaleel ya dago yana kallonsa, d’an murmushin karfin hali yayi yace “Sure” bayan few seconds a hankali yace “Yea Barrister, May be it’s the right decision” Sudais na kallonsa yace “May be?” Khaleel ya shafa kansa yace “It’s just the right decision” a sanyaye ya kare maganr, Sudais ya kalli wayarsa dake ring ya ga Umma ce ke kiransa dauka yayi, ya kai kunne yayi sallama, Umma tace “Kana ji na Barrister, Babu abinda fa xa a fasa, don’t let anything spoil ur mind pls, idan har kana son Khadijah da gaske ka tafi, it’s almost time for prayer ana saukowa a daura auren ba abinda aka fasa in sha Allah” a hankali yace “Toh Umma nagode sosai Allah ya kara girma” tace “Ameen” katse wayar yayi yana kallon Khaleel dake kallonsa shima don duk ya ji me Umma ta ce, a tare suka mike Sudais na kallon agogon wrist din sa. Tun da aka sauko masallaci gaban Sudais ke faduwa, is he really making the right decision, Khaleel dake gefensa na lura da shi, a hankali ya matsa kusa da shi sosai yace “It’s not only the right decision but the best…. For many reasons” Sudais ya kallesa yayi murmushi bai dai ce komai ba, can ya kalli Khaleel yace “Kana da Number Dr Aliyu kuwa? I didn’t see him…” Katse sa Khaleel yyi yana yar dariya yace “Sheer jealousy, did you expect to see him here….” Murmushi kawai Barrister yayi, Khaleel ya fiddo wayarsa ya nemo masa number Aliyu ya mika masa, Dialing number Sudais yyi ya kai kunne ba a dau lkci ba aka dauka Sudais yace “It’s Barrister Aliyu, ban gan ka masallaci ba, or don’t you want to witness the nikka?” Aliyu yyi murmushi yace “It’s not a must I stay near you Barrister, though I can sight you from where I am, I am not what you might have thought of me, idan abun farin ciki ya samu d’an uwana musulmi ina taya sa murna, idan kuma otherwise….” Hangosa Sudais yyi tsaye not too far away from them tare da Salim da wasu frnds, Sudais ya katse wayarsa yana murmushi, Aliyu ya Karaso ya basa hannu Sudais ya mika masa nasa, sannan Aliyu ya mika ma Khaleel ma, Khaleel ya cire glass din idanuwansa ya basa nasa hannun. A can asibiti kuwa bayan an ma Khadijah allurai aka bata drugs aka sallamosu suka koma gida, har sannan hawaye ya ki tsaya mata, Babu abinda aka fasa na biki a gidan kamar yanda Umma tace don kamar ma ba ayi komai ba sai dai Amarya da bata da lafiya, Shayi Umma ta sa baby ta bata ta sha ta kwanta nan da nan bacci me nauyi ya dauketa….

Breakfast, just light😎

Back to top button