Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 77

Sponsored Links

Ya kwantar da murya a hankali yace “Haba my Ummu Shureim…” turo baki tayi ta dauke kai tana goge idonta, ya juya yana kallon shureim, murmushi yayi yace “Toh kaga tayi shiru kai ma kayi shiru” Kai ya gyada masa yana kallon mum dinsa, ya dawo kusa da ita a hankali yace “Anty kiyi hakuri” kallonsa tayi, tayi d’an murmushi tace “Toh na yi” komawa yayi ya xauna, Aliyu ya tada motar ya ci gaba da driving, murya can kasa yace “Mu bari next time sai mu je duba iklima, coz i really don’t have the energy to start consoling you again” tace “Ni ka kai ni yanxu, ba wani next time, I will be going back to schl soon” murmushi yayi yace “Ohk then” hanyar family house din su iklima Aliyu ya dauka, bayan minti kusan sha biyar suka isa babban gidan, yayi parking a waje suka shiga, yan gidan basu wani tarbe su ba, hakan bai wani dame Aliyu ba, ita dai khadijah jikinta yayi sanyi, autar su mahaifin Iklima ta nuna masu wani kofa tace “Tana can” Aliyu ya mike yana kallon khadijah ita ma ta mike, Shureim xai tashi ya duka ya dafa shoulder dinsa a hankali yace “You wait for us here sweetheart ka ji?” Kai Shureim ya gyada masa ya koma ya xauna, Aliyu ya nufi kofar dakin khadijah ta bi bayansa gabanta na faduwa, ita kadai ce kwance dakin mai dauke da yar katifa ko leda babu, katifar ma babu xanin gado, da ganin dakin babu me shiga ciki, Ga cup da plate da spoon dinta nan gefen gadon, da kadan iklima ta fi skeleton kwance a kan gadon, khadijah ta kasa karasawa cikin dakin tana iya kokarin ganin bata fashe da kuka ba ta toshe bakinta, Aliyu ya karasa ciki yana kallonta shi ma a sanyaye, Durkusawa yayi kusa da ita a hankali yace “Sannu iklima” maimakon ta amsa masa sai hawaye, duk jikinsa yayi sanyi ya kasa cewa komai lkci daya shi ma idonsa ya kada, khadijah ta fashe da kuka sosai ta juya ta fice daga dakin, Da kyar Iklima ta iya bude baki tace “Kace ta yafe min don Allah” Ya sauke idanuwansa kasa a hankali yace “Kina shan magani iklima?” Girgixa masa kai tayi hawaye na xuba idonta, ya fi minti biyu durkushe gabanta bai iya yace komai ba, can ya dago da kyar yace “Wa ke kula da ke?” Nan ma ta girgixa masa kai, cikin sanyi yace “Yaushe rabon ku je asibiti?” Kallonsa kawai take alamar maganar ma baxata iya ba, mikewa yayi a hankali ya fita dakin, ya kalli khadijah da ta hade kai da kujera tana kuka Shureim na kusa da ita shi ma yana kukan yana kallonta, Babu wanda yace masu komai, kowa na harkan gabansa a babban gidan, gun yayar mahaifin iklima da ya sani ya nufa a waje, tana xaune su kusan uku suna hira, ya d’an duka ya gaishe ta, ta amsa tana tambayarsa yaushe ya xo, yace “Ba mu jima ba, mama nace iklima na xuwa asibiti kuwa?” Matar tace “An kwan biyu ba aje ba tunda uban nata bai turo kudi ba kilan ya gaji shi ma, mu kuma ya bar mu da wahala” Shiru Aliyu yayi yana kallonta, can ya mike yace “Toh bari mu je yanxu” tace “Kar ma ka bata lokacin ka ko tashi bata iya yi, idan ba likitan xaka je ka gayyato a asibiti ba” Bai ce komai ba ya koma parlorn sannan ya shiga dakin da iklima take, Kallonta kawai yake yana kokarin gano stage din da cutar nata yake, bayan wani lokaci ya juya ya fita, gun khadijah ya nufa yace “Tashi mu je” Ta mike da kyar har lokacin kuka kawai take, Aliyu ya dau shureim ya rungumesa suka fita, bank ya fara tsayawa, ya kalli khadijah kafin ya bude motar ya fita xuwa gun automated teller machine, ba a dau lkci ba ya dawo ya shiga motar, wani babban pharmacy dake area din ya tafi, yana kallon khadijah da taki daina kuka yayi kasa da murya yace “Am begging you ki daina kukan nan Iman, baki kyauta ma yaron nan, even for his sake kiyi hakuri ki daina kukan” Juyawa tayi tana kallon Shureim da ke kuka bakin rai shi ma, hadiye kukanta tayi xuciyarta na mata xafi, Aliyu ya bude motar ya fita, bayan kusan minti goma ya dawo rike da ledan magani masu yawa da tsada, murmushi yayi ganin yanda Shureim yayi shiru yana kallon khadijah dake ta kukan xuci, Bata taba tunanin ganin Iklima a yanda ta ganta ba, ta ji duniyar ba bakin komai yake ba, wani store Aliyu yayi parking ya fita ya siya cartons of malts da Madara masu yawa, sai locozade boost, a booth aka xuba abubuwan da ya siya, ya shiga motar ya kalli khadijah da ta jinginar da kanta jikin kujera ta fada duniyar tunani, kamo hannunta yayi ta juya a hankali tana kallonsa, murmushi ya sakar mata yace “Kowa da irin kaddararsa, su irin tasu kenan, so you just have to pray for them, Allah ya sa mu cika da imani” wasu sabbin hawayen suka sakko idonta, ya tada motar suka bar wajen, shi kadai ya shiga dakin iklima ya ajiye magungunan gefenta yaran gidan suka dinga shigowa da abubuwan da ya siyo, Yana kallon iklima ya fiddo magungunan gaba daya ya shiga nuna mata yanda xata sha, kallonsa kawai take bata ce komai ba, bayan ya nuna mata yace “Idan kin ji kina jin yunwa sai ki daure ki tashi ki sha malt ko madara, idan lokacin shan maganin ki yayi ba a baki abinci ba sai ki sha malt ki sha drugs din kin ji?” a hankali ta gyada masa kai, ya fiddo dubu talatin a aljihunsa ya daga gefen katifar ya ajiye mata yace “Ki dinga aika yaran gidan su siyo maki fruits sai ki basu ko dari biyu don su dinga xuwa kin ji?” Nan ma ta gyada masa kai, ya d’an yi murmushi yace “Allah ya sauwake lil sis, idan kina son ki samu lafiya sai kin yi ta shan drugs din ki” Nan ma dai ta gyada masa kai, yace “Xan dinga xuwa duba ki always, idan kika fara samun sauki xan kai ki gun Mumy dama Abbanki ne yace a kawo ki nan” kallonsa kawai take, jikinsa yayi sanyi ganin hawayen dake sauka idonta, da kyar yace “I will be back soon” daga haka ya mike ya fita dakin ta bi sa da ido, Har suka shigo kaduna, Daga khadijah har Aliyu duk jikinsu a sanyaye yake, tuni Shureim yayi bacci bayan motar, Aliyu na gama parking ya juya yana kallon khadijah da ta bude motar ta fita, fitowa yayi shi ma ya bude back seat ya fiddo Shureim, ya rufe motar ya bi bayanta, bedroom dinsa ya shigar da Shureim ya kwantar da shi, ya fita ya shiga dakin khadijah, kwance ya sameta tayi lamo jikin pillow, ya xauna gefenta yana kallonta, ita dai bata yarda ta kallesa ba, kamo fingers dinta yayi yace “You need not to worry this much Iman, kin san condition din ki fa” Bata san lkcn da ta fashe da kuka ba ya dagota ya rungume ta, ta kwantar da kanta kirjinsa tana shesshekar kuka, murya can kasa yace “Kiyi addu’ar Allah ya basu lafiya Iman” Sun fi minti biyar a haka, Ya dago kanta a hankali yana kallonta, rufe idonta tayi, yyi murmushi yana kallon cute lips dinta, kamar tasan me yake yi ta kwace kanta ta mike ta koma can karshen gado ta kwanta, shafa kansa yyi yace “Ki tashi kiyi sllh” daga haka ya mike ya nufi kofa ta bi sa da ido har ya fita, throughout ranan haka khadijah ta kasa samun natsuwa, Aliyu yayi lallashin har ya gaji, duk ta 6ata mood din little Shureim ma, Bayan magrib ya dawo masallaci ya shiga bedroom dinsa dai dai lkcn da wayarsa ya katse, karasawa yayi ya dauka yaga Mumy ce ta kirasa, ya xauna gefen gado ya shiga kiranta, tana dagawa yayi mata sallama, jin yanayin muryarta a hankali yace “Mumy baki da lafiya ne?” Mikewa yayi yace “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un” lkci daya ya ajiye wayar ya koma ya xauna ya rike kansa, bai san lkcn da hawaye ya dinga xuba idonsa ba, ya fi minti biyar a haka kafin ya mike da kyar ya share idonsa ya dau makullin motarsa ya fita daki, yana ta tsaye corridor kafin ya bude dakin khadijah xaune ya ganta kan darduma ta jinginar da kanta da gado, Shureim na xaune kusa da ita, kasa karasawa cikin dakin yayi yana daga bakin kofar yace “Iman xa mu je can gida yanxu” ta kallesa kafin tace komai har ya juya ya wuce, a tunaninta gaida Mumyn xa su je su yi, ta mike ta linke pray mat din ta ajiye, ta kama hannun Shureim suka fita bayan ta kashe wutan dakin, ganin yanayin Aliyu ta kallesa da damuwa tace “Ko dai wani abu ya faru ne?” Yana driving idonsa kan titi yace “Nothing” har suka isa gida bata sake cewa komai ba, yayi parking ya fito ita ma ta fito tana rike da shureim suka bi bayansa, sosai gabanta ya fadi ganin mutane a parlorn, Aliyu ya isa gun Mumy ya durkusa gabanta, khadijah ta kasa karasawa xuciyarta na bugawa, upstairs ta wuce xuwa dakin baby da sauri, baby na ganinta ta fashe da kuka sosai, cike da karfin hali khadijah ta durkusa gabanta tace “Me ya faru baby” Baby tace “Iklima…” Hawaye ya shiga sakko ma khadijah ta hade kanta da gado tana salati a ranta. Daren ranan a gidan suka kwana gaba daya, mutuwar Iklima ya girgixa kowa barin khadijah da Baby, da ta tuna yanayin da suka sameta daxu da rana sai taji hawaye ya ki tsaya mata ashe mutuwa xata yi, gashi ko magana bata samu ta mata ba saboda tashin hankali, babu wanda ya wani rintsa a gidan har asuba. Washegari da safe Umma suka xo gidan da Nanny don yi ma Mumy gaisuwa, da Umma ta tashi tafiya Shureim yace xai bi ta, haka Umma ta wuce da shi don har da kukan sa, sai bayan da aka yi sadakan uku Khadijah da Aliyu suka koma gida da daddare, har sannan shock din bai bar ta ba, har ranta taji ta yafe ma Iklima don ita a iya tunanin ta ma bata mata komai, ajiye abincin da Mumy ta basu su tafi da shi tayi a nan tsakiyar parlor ta wuce sama Aliyu da ya bi ta da kallo yace “Iman” juyowa tayi tana kallonsa, yace “Baxa ki ci abincin ba” ta girgixa masa kai, yace “Ba fa ki ci komai tun daxu ba” Bata ce komai ba ta haura sama, kitchen ya shiga ya dau plate ya wanke sannan ya dawo parlorn ya bude abincin ya dibar mata ya rufe sauran ya wuce sama, kayanta ya sameta tana cirewa, tana ganinsa ta durkushe kasa da sauri kamar xata yi kuka tace “Baka iya sallama ba ne” d’an murmushi yayi ya sauke idonsa daga kallonta yace “Yi hakuri” ta turo baki tace “Ka ajiye ka tafi” Ajiye mata abincin yayi ba tare da ya kalleta ba ya juya ya fita, zani ta dauka ta daura ta xauna kusa da shinkafa da miyar da ya ajiye mata ta dau spoon din ta fara ci a hankali, Bata wani ci da yawa ba don har sannan bata da appetite ta mike ta shiga bathroom, sai da ta wanke bakinta sannan tayi wanka ta fito, Hijab ta sa ta dau sauran abincin da ta rage ta fita da shi ta dawo dakin, ta dau lkci xaune gaban madubi tana shafe shafenta ya bude kofar, xaro ido tayi ta duka, ya koma da sauri yace “Ohh sorry, Assalamu alaikum…” Tayi saurin daukan hijab dinta ta sa ganin har ya sake shigowa ta hade rai tace “Bana son haka Aliyu, ba sai an amsa ake shigowa ba” dariya ta basa sai dai bai yi ba, ya mika mata wayar hannunsa yana kallonta yace “Gashi Dr Ayman xai maki gaisuwa” ta hararesa ta karba wayar tace “Toh ni ka fita” juyawa yayi ya fita dakin, ta kai wayar kunne, muryar Khaleel taji yace “Uhm lallai, ya fita koh?” Murmushi tayi murya can kasa tace “Ina yini Doctor” yace “Lafiya lau khadijah, ya gida?” Tace “Alhmdllh, ya jawahir” yace “She’s fyn, ya karin hakuri?” A sanyaye tace “Mun gode Allah” yace “Allah ya mata rahama” tace “Ameen mun gode” yace “Maa sha Allah, good nyt” tace “Alryt, my regards to jawahir” yace “In sha Allah” daga haka ya katse wayar, ta ajiye gaban madubin ta mike ta cire hijab dinta ta dau kayan baccin da ta fiddo ta saka, ta linke Hijab dinta ta ajiye sannan ta kashe wutan dakin ta kwanta, har bacci ya fara daukanta taji an bude kofar dakin ta bude ido da sauri, tana ji ya rufe kofar, Bai kunna wutan ba yana tsaye daga inda yake a hankali yace “Iman, wayana fa?” Shiru tayi bata ce komai ba, ya fi minti daya tsaye kafin ya juya ya fita a hankali ya rufo mata kofar, sai a sannan ta mike xaune, tana ta xaune kan gadon kafin ta sauko ta tafi gun mirror ta dau wayarsa ta saka hijab ta fita, a hankali ta bude kofar dakinsa ta shiga.

Back to top button