Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 74

Sponsored Links

A hankali khadijah ta koma ta kwanta, bata kara minti biyar ba bacci ya dauketa. Da asuba tana jin fitansu tare da Shureim xa su masallaci, ita ma ta mike ta shiga bayi, tana xaune kan darduma tana azkar taji shigowarsu gidan, bude kofar dakinta Aliyu yyi suka shigo tare da Shureim, kallo daya tayi masu ta dauke kai, ya xauna gefen gado Shureim ya nufe ta ya durkusa gabanta yace “Anty ina kwana?” Tana kallonsa tace “How was ur nyt?” Ya wara ido yace “It was cool Anty” Bata ce komai ba ta saci kallon Aliyu suka hada ido, d’an murmushi yayi a hankali yace “Good morning Iman” sunkuyar da kanta tayi bata ce komai ba, ya mike ya nufi kofa Shureim ya bi bayansa da sauri ta bi su da ido har suka fita, ta fi minti ashirin xaune ganin gari ya fara washewa ta mike, tana sane jiya babu abinda tayi a gidan, yau kam ta sauka parlor ta share ko ina ta goge, ta shiga kitchen ma ta gyara ta goge, tana kokarin sa turaren wuta a burner aka danna bell, mikewa tayi tana kallon kofar, ta wuce sama da sauri don dauko hijab ta dawo ta bude, Baby ce tsaye da breakfast, Khadijah ta langwabar da kai tace “Don Allah daga yanxu kar ki sake kawo abinci xan yi girki muna ba Mumy wahala…” Baby ta wara ido sai kuma tayi dariya tace “Xa dai ki girka abinda xa ki ci, tunda nasan ba bama yayana xa ki yi ba, yaron ki kam nasan shi ma xa ki basa, Abbansa dai ne baxa a bai ma ba” tabe baki khadijah tayi ta bata hanya ta shigo ta ajiye abincin nan parlor tace “Da fatan kun tashi lafiya, yau naga har da su gyare gyaren gida meye sirrin Iman?” Tana murmushi da tsigar tsokana ta kare maganar, khadijah ta hade rai tace “Wani irin sirri?” yar dariya Baby tayi tace “Oho, ni dai xan wuce, a gaida min yayana” Daga haka ta nufi kofa khadijah ta bi ta da kallo har ta fita sannan ta tabe baki, ta koma ta ci gaba da abinda take, dinning ta kai breakfast din ta ajiye sannan ta wuce sama ta shiga daki, nan ma ta gyara gadonta tayi goge goge kafin ta shiga wanka, tana xaune gaban mirror bayan ta fito wanka tana shafe shafe aka bude kofar bedroom din, xaro ido tayi tana gyara towel din jikinta, ganin Shureim ne ya shigo ta sauke ajiyar xuciya, ya iso kusa da ita yace “Anty am hungry” tace “Me ya hana uncle din baka breakfast” Ya buda hannu yace “He told me I shud come to you ki bani” Tana shafa mai a kafarta tace “Shi me yake yi?” Shureim ya matso cream din xai shafa mata ta 6alla masa harara tace “Ina wasa da kai koh?” Ya mike yace “Anty taya ki xan yi” toes dinta ta mika masa tace “Toh shafa a nan” ya durkusa yana shafa mata tace “Tambayar ka nayi me uncle din yake?” Ya kalleta yace “He is lying down” shiru tayi bata ce komai ba, a hankali yace “Anty yace min he is not feeling fine” Kamar baxa ta ce komai ba sai kuma tace “What’s wrong with him” Yace “I don’t know” Tace “Je parlor ka jira ni in sa kaya sai in xo in baka breakfast” yace “Toh” sanann ya fita dakin, mikewa tayi ta dau atamfar da xata sa na riga da skirt, sosai dinkin yayi mata kyau tayi simple dauri na dankwali ta sa eye pencil a idonta sai chapette ah two colored lips dinta, sosai tayi kyau, ta fesa turare daga karshe ta fita dakin, har xata sauka stairs sai kuma ta tsaya, ta fi minti biyu tsaye kafin ta karasa kofar dakinsa a hankali ta bude, kwance ta gansa ya rufa da duvet har kansa, ta sauke idonta kasa ta karasa dakin kamar mai counting steps dinta, tana ta tsaye kusa da gadon tana kallonsa, a hankali ta durkusa dab da shi ta cire duvet din fuskarsa, idanuwansa a lumshe suke, ta kai hannu forehead dinsa, lkci daya ya bude idonsa tayi saurin dauke hannunta ta koma baya, kasa tashi tayi kuma bata yarda sun kara hada ido ba ta fara kame kame, kallonta kawai yake, ta dago daga karshe tana kallonsa a hankali tace “Are you sick?” Ya mike xaune yace “No…. am alright” shiru tayi tana kallonsa, ya sauka daga kan gadon ya nufi bayi ta bi sa da kallo don kana ganinsa kasan karfin hali yake yi, Mikewa tayi a hankali ta nufi kofa ta fita dakin, kwance ta ga Shureim ya kunna cartoon yana kallo parlorn yana ganin ta yyi saurin kashe tvn da remote din hannunsa, ta tsaya tana kallonsa tace “Who asked you to switch on the tv?” Shiru yyi yana kallonta, ta wuce dining ta hada masa shayi a cup ta debar masa dankali da kwai da plantain, sannan ta yankar masa bread karami ta daura gefen plate din Irish din, tace “Zo ka xauna nan Shureim” ya taso ta ja masa kujerar dinning din ya xauna ta ajiye masa abincin a gabansa sannan ta koma kitchen ta dauko wani cup din ta dawo ta hada wani shayin, ta debi Irish da kwai a plate, ta dauko wani bowl ta xuba pepper soup na kayan ciki, gaba daya ta daura su kan tray ta dauka ta wuce sama, a hankali ta tura kofar dakin nasa, xaune ta gansa gefen gado ya rike kansa, jin an bude kofa ya dago yana kallonta, kanta a kasa ta iso har kusa da shi ta ajiye tray din ba tare da ta kallesa ba ta mike ta fita dakin. Dining ta koma gun Shureim ta xauna kujerar kusa da na shi ita ma ta hada shayin, a hankali take sha har ta gama, tuni Shureim ma ya gama ya mike pleadingly yace “Anty plss in kunna tv?” Kai ta gyada masa ya juya ya wuce parlor, ta kwashe duk abinda suka bata ta kai kitchen ta wanke sannan ta fito, sama ta wuce ta bude bedroom din Aliyu, kwance ta gansa ya kara rufa da duvet, ta karasa tana kallon breakfast da ta ajiye masa, Bata san lkcn da ta xauna gefen gadon ta yaye duvet din tana kallonsa da damuwa tace “Baka yi breakfast din ba? What’s wrong with you?” Ganin bai bude ido ba kuma bai ce komai ba ta kamo hannun sa da damuwa tace “Talk to me plss” bude ido yyi ya mike xaune, ta dauko cup din shayin da ta rufe ta bude tana mika masa tace “Gashi ka sha sai ka sha magani” karba yyi xata dauko plate na irish ya dakatar da ita “Noo I will take this first” da kyar yyi maganar, ta dago tana kallonsa ya kai shayin baki kamar wanda xai sha magani, kadan ya kurba ya cire a bakinsa, tace “Da zafi ne?” yana girgixa kai ya mika mata, ta hade rai tace “Me xan yi da shi?” Xai ajiye kasa tayi saurin cewa “Kar ka ajiye shi, u better force ur self to drink it…” Bai saurareta ba ya ajiye ya mike ya nufi bayi da sauri, a sanyaye ta mike bi sa da kallo, tana ta tsaye ita dai bata ji yana amai ba kamar ynda tayi tunani, can dai ta bi bayansa, jingina tayi da kofa tana kallonsa ganin aman yyi har ya wanke wajen, ya juyo xai fita bayin ta rikesa a hankali tace “Let me make you water sai kayi wanka” yana gyada kai yace “Finish first” daga haka ya fita, ta hada masa ruwan ta fito, kwance ta samesa ya kara rufe kansa, ta cire duvet din da damuwa tace “Kayi wankan sae mu je asibiti” da kyar ta samu ya mike xaune, tana ta kallonsa ganin har rama yyi, sauka yyi daga kan gadon ya cire jallabiyar jikinsa ta amsa ta ajiye sannan ya wuce bathroom, sai a sannan ta fita dakin a sanyaye. zaunawa tayi gefen gadonta tayi tagumi bayan kusan minti talatin ta tashi ta koma dakinsa, dai dai lkcn ya fito wanka daure da towel, tayi saurin juyawa kamar mai neman abu sai kuma ta fita dakin, turo baki tayi ta sauka downstairs ta tadda Shureim yana ta kallo ta xauna kusa da shi. Jin alamar Aliyu na sakkowa stairs ta kalli direction din, kananun kaya ne jikinsa yana rike da makullin mota ya iso parlorn, ta mike tana kallonsa tace “Where are you going to?” Bai ce komai ba, ya nufi kofa, ta isa gabansa ta hade rai tace “Nace ina xa ka?” Ya ki kallonta yace “To get drugs” kwace makullin hannunsa tayi tace “Let me do the driving” Daga haka ta nufi stairs ya bi ta da kallon gefen ido, mayafi karami ta dauko a daki ta rataya a wuya ya dinga kallonta, ganin ta nufi kofa yace “Iman!!!” juyowa tayi tana kallonsa, yana nuna mayafin kanta yace “Haka xa ki fita?” Kallon kanta tayi daga sama har kasa tana masa wani kallo tace “So?” Kallonta kawai yake bai ce komai ba, ta hade rai ta dawo ta damka masa makullinsa tace “Sai ka ja motar, ka tafi inda xaka” Komawa tayi ta xauna ya bi ta da kallo kafin ya fita parlorn, turo baki tayi jin yana warming mota ta mike ta wuce sama ta dauko Hijab dinta ta sa ta sakko parlor, kashe tv tayi tana hararan Shureim da duk hankalinsa gaba daya na kan kallo as if his life depend on it, ya mike da sauri yana kallonta yace “Anty ina xa ki je” Bata tanka sa ba ta nufi kofa ya bi bayanta, Tun daga nesa Aliyu ke kallonsu daga cikin motarsa ko kiftawa babu har suka iso ya dauke kansa, Ta hade rai tace “Ka koma daya side din” D’an murmushi yayi ba tare da ya kalleta ba ya fito ya koma daya bangaren Shureim na biye da shi a baya, yaron ya bude back seat ya shiga, shi kuma ya xauna front seat, ta shiga maxaunin driver, sabon mai gadi dake bakin gate ya bude gate din ta fita da motar, a hankali take driving din har suka hau saman titi, kamar ana tilastata tace “Wani pharmacy?” Gaya mata yyi idanuwansa a kan titi, kira’ar sheikh Sudais kadai ke tashi a motar in a very low tone, yace “Who taught you how to drive” Bata ce komai ba har suka iso pharmacy din, sai a sannan ta kallesa a takaice tace “A Good Samaritan taught me” Bai ko kalleta ba ya bude motar yayi wucewarsa, ta bi sa da wani kallo, Shureim yace “Anty, Uncle ba shi da lafiya koh” Bata ce masa komai ba, Bayan kusan minti goma Aliyu ya fito rike da ledan drugs ya shiga motar, ganin hanyar da ta dauka, yana kallonta da kyau yace “Ina xa ki je?” Ba tare da ta kallesa ba tace “Xan je gida in dauko ma Shureim wears dinsa” “Noo, mu wuce gida, xan je da kaina in amso masa ba sai kin je ba” A hankali take ta tafiya da motar shi dai bai kara ce mata komai ba, can ta turo baki ta dau hanyar gida… Tana gama parking ya bude motar ya fita ya bude back seat ya fiddo Shureim suka wuce ciki ta bi su da kallo, Babu kowa parlorn da ta shigo, ta ajiye makullin hannunta ta wuce kitchen, Cup din tea ta hada ta fito ta haura sama, bude kofar dakinsa tayi ta gansa xaune yana ballar drugs shureim sai surutu yake masa, ta ajiye masa shayin gabansa ta fita, dakinta ta shiga ta kwanta, Bata san lkcn da bacci ya dauketa ba kawai taji hannu a fuskarta ta bude ido a hankali, lkci daya ta mike xaune tana komawa baya tana kallonsa tace “What?” yace “Kin yi baki downstairs” Ta d’an buda ido tace “Su wa?” Ya mike yace “Suna jiran ki” daga haka ya nufi kofa tace “Shine baxa ka turo Shureim sai ka xo kana wani taba min fuska” har ya fita bai juyo ba balle yace komai, tashi tayi ta gyara daurin dankwalinta ta bi bayansa, Tsaye tayi stairs din karshe tana kallonta ko kiftawa babu. Suka hada ido da Khaleel dake jujjuya makullin motar hannunsa, saurin sunkuyar da kanta tayi, ta karasa shigowa parlorn kanta a kasa, haka kawai taji wani mugun kunyarsa take ji, ta xauna kan kujera taki kallon Jawahir, Khaleel yace “Good afternoon khadijah” Ba ta dago ba tace “Ina yini” ya d’an yi murmushi yace “Lafiya lau, how are you” Bata ce komai ba, Jawahir tace “Ya gidan khadijah” sai a sannan khadijah ta kalleta, Jawahir ta sauke idonta a hankali, Khadijah tace “Alhmdllh” Khaleel yace “Ta ce in kawo ta ku gaisa….” Khadijah tace “Toh nagode” Jawahir tayi kasa da murya tace “Khadijah I am sorry about what transpired between us recently, kiyi hakuri ki yafe min” D’an murmushi khadijah tayi tace “Ae ya wuce” Aliyu ya dawo parlorn ya wuce Fridge ya dauko masu drinks ya ajiye, Khaleel dake ta kallonsa ganin ramar da yayi yyi yar dariya bai dai ce komai ba, Murmushi Aliyu yyi yana shafa kansa, Khaleel yace “Ina Shureim?” Aliyu ya xauna kujera yace “He slept off minutes ago” Khaleel yace “Alryt then, dama madam na kawo, I think we will be on our way now, but before then Ina son xa muyi magana da kai…” Aliyu ya mike yace “Alright” a tare suka fita parlorn, Jawahir ta dawo kusa da khadijah tace “Da gaske kin hakura khadijah?” Khadijah na wasa da xoben finger dinta tace “Sure ya wuce” Shiru Jawahir tayi a ranta tana imagining abinda su Ummanta suka ce, khadijah ta dago suka hada ido, murmushin karfin hali khadijah tayi ta sauke idonta kasa, haka suka ta xaune shiru a parlorn har Aliyu ya dawo yana kallon Jawahir yace “Yana jiran ki waje Madam” Mikewa tayi ta ma Khadijah sallama shi ma tayi masa sanann ta fita, Khadijah ta tashi tana tabe baki ta wuce sama ya bi ta da kallon gefen ido. Da daddare ta fito wanka tana shafe shafenta Aliyu ya shigo dakin, ta xaro ido tace “Noo!! you can’t just come in without….” Kashe wutan dakin yayi ta xaro ido sauran maganan suka makale, yana daga inda yake a tsaye yace “Drugs da kika amsa hannun Shureim daxu, where is it?” Tace “Ka tafi xan kawo maka” a d’an fusace tayi maganan, yayi murmushi ya tako a nutse har inda take, duk da duhun dakin hakan bai hanata ganinsa ba ta dinga komawa baya a tsorace tace “Aliyu meye haka…” Xata gudu ya rikota sai jin ta tayi jikinsa, lkci daya jikinta ya dau rawa ta dinga kokarin kwace kanta amma yaki saketa, Babu abinda ke mata yawo a memory dinta sai incident din Shekaru bakwai da suka wuce, lumshe ido yyi jin yanda ko ina na jikinta ke rawa, murya can kasa yace “Ki gaya min abinda ke xuciyar ki game da ni Iman…. Tell me what u are thinking of me” Ta fashe da kuka tace “I beg you ka sake ni, you are making me….” Bai bari ta kai karshe ba ya hade bakinsu….. Bai xame ko ina da ita ba sai kan gado, ta kwace bakinta jikinta na bari tace “Nooo plss Aliyu, wllh ka bari bana so…. Kana son xuciya na ya fara min ciwo ko” Murya can kasa yace “I will cure it…” Toshe bakinta yayi jin xata fara masa ihu, Sallamar Shureim bakin kofar dakin ya sa shi saketa da sauri, da ta samu ta sauka kan gadon bata xarce ko Ina ba sai bayi ta rufe kofar jikinta na 6ari, Aliyu ya mike tsaye yana kallon kofar ya kunna wutan dakin sannan ya bude, Wayarsa Shureim ya mika masa yace “Uncle Mumy tana kiran ka tun daxu” Ya amshi wayar yace “Are you done with the game?” Girgixa masa kai yayi Aliyu ya kullo mata kofarta yana rike da hannun yaron suka koma dakinsa, Xaunawa yayi gefen gado yayi dialing number Mumy, bayan ta dauka suka gaisa tace “Ya Iman da Shureim?” Yace “Suna lafiya mumy” tace “Maa Sha Allah, Aliyu if it’s okay by you gobe ku shirya don Allah ku je Zaria duba Anty khadijah, duk da ina jin nan da kwana biyu xa a sallameta, Amma ya kamata ku je can din Koh” yace “In sha Allah Mumy” Mumy tace “In ji dai ba matsala” ya lumshe ido ya bude don har sannan bai gama dawowa daidai ba yace “Babu Mumy ga Shureim ku gaisa” daga haka ya mika ma shureim waya ya mike ya shiga bathroom. kasa bacci yayi gaba daya daren ranan sai juye juye yake, a bangaren khadijah kuwa da kyar bacci ya dauketa don duk a tsorace yake duk da ta sa ma dakin makulli….

Back to top button