Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 10

Sponsored Links

10

 

Ɗan tsayawa ruma ta yi tana kallon mama, cikin sangarta ta ce “Mama wai me na yi to?”

“Ban sani ba fitar mini daga ɗaki, mara kan gado, ni ba dan a gida na haifeki ba, cewa zan yi an canza mini ‘ya, idan an yi gabas sai ki arta ki yi arewa, me ake da wani wari ban da rashin kan gado irin naki?”
Tsayawa ruma tayi tana kallon mama tana wasa da gashin kanta.
“Ba zaki fita ki bar mini ɗaki ba, sai na taso kan ki?”
Fitar ta tsakar gida yayi dai-dai da shigowar Yasir, da shi da Huzaifa.

Yasir ya aika mata da wani irin mugun kallo ya ce “Me na ce miki game da zuwa Ajinmu?”

Ta murguɗa baki ta ce “Ni wurinka na zo, ai ba wurinka na zo ba, ni da malam Habibu muka zo”

“To uban me ya hana ki je ajin su Huzaifa?”

Huzaifa ya yi caraf ya ce “Wallahi ta zo mana aji, sai na mata dukan tsiya, ta zo ɗin ta gani”

Hararsu ta dinga yi, tana cewa wallahi sai ta je.

Bayan Huzaifa ya canza kaya, ya shiga ɗakin mama ya ɗau jakarta.
Ruma ta ɗaga murya ta ce “Mama, ga Huzaifa nan ya ɗaukar miki jaka”

Ya ce “To munafuka”

“Wallahi ni ba munafuka ba ce, mama Huzaifa zai satar miki kuɗi”

Huzaifa ya ce “Mama aron naira ɗari zan ɗauka”

Mama ta ce “Ajiye mini jakata, ba zan baka aron ba, idan ka ɗaukar mini kuɗi ba bani ka ke ba”

“Dan Allah mama ki bani, zan baki wallahi”

Daga kitchen mama ta ce “Ba zaka ajiye mini jaka ba sai na zo ɗakin nan?”

“Mama wallahi bai ajiye miki ba”

A fusace Huzaifa ya ajiye jakara, yana yiwa ruma kallon banza, kamar ya kai mata duka haka ya fice.

Ruma ta ce “Dana sani na bar shi ya ɗauka, nawa nake bin mama ba biyana take ba”

***

Yau za a rufe makarantar su ruma a tafi hutu, yau za ayi spelling B da aka bawa su ruma.
Sai bin malaminsu take tana ce masa ita fa sai an sakata a cikin masu spelling B.
Malamin ya ce “Ki kwantar da hankalinki, zamu san yadda za ayi”.

Azabar nacin ruma sai da ya sanya aka sakata a cikin masu spelling B, amma aka ce kar ta yi magana.

Ƙarshe dai ruma ce ta taimaki ‘yan ajinsu, gaba ɗaya kalmomin nan babu wanda ba ta haddace ba, ruma ta bawa malaman makarantar su da ɗaliabai mamaki, dan ko bata takardar da aka yi, tsabar naci ne ya sanya a ka bata.

Ai kuwa ruma ta samu kyaututtuka sosai, karo na biyu a rayuwarta, da ta samu wani abun arziki a saboda harkar karatu.
Aka bata litattafai kaya guda, da kayan koyon karatu.

Ruma baki har kunne ta je gida, mama ta ganta da kaya niƙi-niƙi.

“Ke wannan kayan na menene?”

Ruma ta zubewa mama kayan ta ce “Mama, duk nawa ne a makaranta aka bani”

“Meyasa aka baki?”

“Wannan takardar da aka bani ce a makaranta, kowa ya ƙi koya mini, na je na yi ta yi da kaina, shine fa aka yi yau na samu wannan kyautar”

Mama ta ce “Hmm, ai shikenan”

“Mama wai na ga kamar ba ki yadda da bayanin da na yi miki bane?”

“Eh to kusan hakan, dan abin da kamar wuya gurguwa da auren nesa”

Cikin rashin fahimta ruma ta ce “Mama wace gurguwar kuma?”

Cikin gajiya da halin ruma mama ta ce “Ki tashi ki cire uniform ki yi wanka”
Ruma ta tashi ta cire kayanta, ta ɗebi ruwa ta shiga wanka. Ta na tsaka da wankan, ta jiyo muryar Usman ya shigo, daga banɗakin ta buɗe murya ta ce “Yaya Usyy Albishirin ka”

“Ruma ban hanaki surutu a banɗaki ba?”

Ta ce ‘yi haƙuri mama”

Ba dan ta gama wankan ba, cikin zumuɗi ta fito daga wankan ‘Yaya usman, bari na nuna maka wani abun mamaki”

Ba ta san a ya ta fito daga banɗakin ba, sai da mama ta daka mata tsawa, daga ita sai pant ta fito. Ta koma ta ɗauko zani, sannan ta kwaso kyaututtukanta ta nunawa Usman.

Ya kalli ruma sannan ya kalli kayan ya ce “Ruma ban yarda da ke ba”

Ta ce “Saboda me?”

“Ina ki ka ga kwanyar da zaki yi wani abun arziki ke?” Tsuke fuska ta yi tana kallonsa ta ce “To me ka ke nufi?”

“Ɗauko takardar da aka baki, na yi miki tambayoyi” ta miƙe ta je ta ɗauko masa takardar ta miƙa masa.

Ga mamakinsa duk abin da ya tambayi ruma, sai ta bashi amsa daidai ko gyaranta ba ya ci.
Ya ajiye takardar, ya kalli ruma ya ce “Ni fa haryanzu mamaki nake, matar da take zuwa ta kusa da ta ƙarshen aji, ita ta yi wannan ƙoƙarin”

Ruma ta yi murmushi sannan ta ce “Ikon Allah kenan, baku san haushin da nake ji idan aka ce mini daƙiƙiya ba, shi ya sa na dage na je na iya”

“Congratulations, ina ma zaki cigaba da dagewa da kin ga cigaba a rayuwarki”

Ta taɓe baki ta ce “A’a da wahala gaskiya, ka san baƙar wahalar da na sha kan na iya wannan abun, dan a dai na ce mini daƙiƙiya daga wannan ba zan kuma ɗaukar dala ba gammo ba”

Usman ya yi murmushi ya dafa kafaɗarta ya ce “Haba ƘANWAR MAZA, rayuwa ce fa, kuma idan da rai da lafiya yanzu aka fara, kar ki sake ɗarsawa ranki cewa akwai wani abu da zai gagareki komai wahalar sa, rayuwa sai da gwagwarmaya da faɗi tashi, musamman ga ɗan talaka. Kar wani abu ya ƙara razana ki, ko ki yadda ke daƙiƙiya ce zaki iya komai kema”
Ta yi ajiyar zuciya sannan ta ce “Dan Allah da gaske Yaya Ussy?”

Ya jinjina mata kai ya ce “Sosai makuwa, ki dubi rayuwarmu a cikin gidan nan, tun baki da wayo, har zuwa yanzu a cikin gwagwarmaya muke, farincikinmu kawai ki ke gani, amma kowa akwai kalar ƙalubalen da yake fuskanta, ki kalli mama ba ta yi karatu mai zurfi ba, amma ta cancanci a kirata jarumar uwa, ba lallai ki fuskanci me nake nufi ba a yanzu, amma ki saka maganganun nan a ranki akwai ranar da za su yi miki amfani. Amma ki tsaya a kan ƙafafuwanki, ki fuskanci abin da yake baki tsoro, ke fa jaruma ce, bai kamata sunan daƙiƙiya ya biki ba”

Ruma ta ɗan yi shiru sannan ta kalli Usman ta ce “Yaya Usy, in sha Allah zan dinga mayar da hankali na yi karatu sosai na daina wasa”

“Yauwwa ko ke fa, ai hakan ya fi deluwa”

“Kuma zan cigaba da ƙoƙari, in zama mai ƙarfi sosai, duk wanda ya tsokane ni, in yi masa dukan tsiya in farfasa masa baki da hanci, in kakkarya mutum”

Mama da take jin su ta ce “Ke kuma ba kya fatan ki girma ki yi hankali, sai rashin hankali ke ba kya fatan Allah ya shiryeki ki daina faɗace-faɗacen banzan man a matsayinki na mace, faɗa ba na ‘ya mace bane”

Ruma ta ce “A’a mama, gara ki bar ni na koyi ƙarfi sosai”

“Sai kuma ki yi ai”.

Usman ya kuma murmusawa ya ce “Ba irin wannan ƙarfin ake magana ba, ƙarfin zuciya da kaifin basira wurin sarrafa duk wata Matsala da za ta tinkaro ki, kar ki bari matsalolin ki su razana ki, ko sau ɗaya kar ki bada wannan damar, ki turje ki dake ƙalubale duk girmansa, ki yi gaba da gaba da shi”

Ruma ta ce “Mhmm, gashi dai hausa ka ke yi, amma bana gane me ka ke faɗa, sai na ji kamar ma wani yaren ka ke daban, ban wani gane me ka ke nufi ba”

“Ni ma na san ba zaki gane a yanzu ba shekarunki da hankalinki babu lallai ya kai, saboda ke a yanzu ba ki sa wata damuwa ko matsala. Tashi ki zubo mana Abinci mu ci” Ruma ta miƙe ta tafi kitchen.

Mama ta ce “Kai ma banda abinka, wannan zaka zaunar ka na wani gayawa wannan bayanan, me zata gane a ciki? Ita ban da wautarta da tambayoyin ta na rashin kan gado me ta sani?”

Usman ya ɗan yi shiru sannan ya ce “Haka kurum mama ina jin tausayin yarinyar nan, jikina na bani za ta yi gwagwarmaya a rayuwa, gwagwarmaya a bugiren da ba zamu iya tsaya mata ba, ko yi mata wani taimako ba, gwagwarmayar da take buƙatar ta tsaya da ƙafarta ta cimma nasara”
Mama ta ce “Tooo ikon Allah, to koma dai menene, ni dai addu’a kullum cikin yi muku ita nake, ba ku kaɗai ba, dukkan ‘ya’yan muslmai baki daya, Ubangiji Allah ya shiga lamarinku, ya tsare gabanku da bayanku, ya kula da rayuwar ku”

“Amin mama, Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana uwa ma bada mama”

“Amin ya rabb”

A ranar duk wanda ya shigo, sai ruma ta nuna masa kyaututtukan da aka bata, har a waya sai da aka kira mata yaya Abubakar ta gaya masa, tun ana tayata murna da Allah ya sanya albarka har ta fara ƙular da mutanen gidan. Dan hatta maƙwabta sai da ta shiga ta gaya musu ai tayi ƙoƙari a makaranta an bata kyauta.
Da ta je Islamiyya kuwa, har ofishin shugaban makaranta ta je, shi ma ta gaya masa, ya tayata murna tare da sanya mata albarka, ta ƙarasa staff room bayan sun gaisa da malaman suma ta gaya musu ai a makarantar boko tayi ƙoƙari an bata kyaututtuka. Nan suka yi ta mata fatan alkhairi, ji take a duniya yau ta ƙure daɗi tayi abin da ba ta taɓa ba.
“Malam to idan an idar da salla dan Allah a sanar”

Wani malami ya kalleta ya ce “A sanar da me?”

“Na yi ƙoƙari a makarantar boko mana, har na ciyo kyauta, word kusan ɗari biyu da hamsin fa na haddace yadda ake spelling ɗin su”

“To amma ai nan ba makarantar boko ba ce ba, ki bari idan ki ka yi bajinta a nan ma, sai a sanar wa ɗalibai”

Ruma ta ce “A’a malam gara ai a sanar, saboda masu ce mini daƙiƙiya su san ƙwaƙwalwata na aiki, wataran zan bayar da mamaki”.

Malam Habibu ya yi caraf ya ce “Ƙwarai kuwa, dole a sanar da ɗalibai wannan namijin ƙoƙari da ki ka yi, nima ba rannan na yi ƙari kin iya ba, duk za a sanar kar ki damu” cikin jin daɗi ruma ta ce “Yauwwa malam na gode”

Bayan tafiyarta ya yi dariya ya ce “Yanzu idan ba ku yi yadda take so ba, Allah kaɗai ya san wace tijarar zata yu, amma yanzu idan aka faɗa ɗin, za ta ji daɗi da ƙara samun ƙwarin gwiwa”.

Ruma da ta ga an idar da salla, ana neman a watse ba a sanar ba, ta tafi ƙofar masallacin maza, ta leƙa ta ce “Malam Habibu kar ka manta fa, na ji ba a faɗa ba”.

Malam Habibu ya ce “To bari a sanar, ai yakamata wannan abin arziki haka”

Haka malam Habibu ya tashi ya ce “‘yan uwa ɗalibai da malamai, a taya ‘yar uwa murna, wato ‘ya ta rumaisa, bisa nasara da ta yi a wata gasa da aka shirya a makarantar bokon su, har ta samu kyaututtuka dan Allah ayi mata Addu’a, Allah ya ƙaro nasarori”

Daɗi kamar ya kashe ruma, masu dariya na yi, masu jin haushi na yi.

Huzaifa da suka yi salla sahu ɗaya da Yasir ya ce “Ka ji abin da wannan mara kan gadon ta yi ko?”

“Bar motsatsiya, suma malaman da suka biye mata, idan ba tayi wasa ba sai na ƙona banzayen litattafan da aka bata, kowa ma ya huta”.

Cike da annashuwa ruma ta tafi gida, ta je ta bawa mama labarin yau har a wurin salla, aka sanar da ta ci kyauta a makarantar boko. Tana shiga gidan ta tarar da Yaya Abubakar ya zo hutu, da kuma waa dattijuwar mata a zaune a tsakar gida.
Da sauri ruma ta nufi dattijuwar ta faɗa jikinta ta ce “Gwaggo Atine, yaushe rabon da na ganki?”

Dattijuwar ta washe baki ta ce “Dama ina zaki ganni, nayi-nayi da babarki ta din ga kai mini ke ina ganinki, amma ta ƙi saboda ina ƙauye”.

Mama ta ce “Haba Yaya Atine, wallahi ba haka bane ba, kin san yanayin makaranta kuma ruma ba ta ji idan aka kai miki ita sai ta gallabe ku”

Ruma ta haye kan cinyar matar cikin jin daɗi ta zauna.

Matar ta ɗora da cewa “Ba wani rashin ji, a kawo mini ita a hakan ina son ta, duk rashin jin ta. Ɗan uwana ya ƙallafa rai a kan ta yana son ta, nima ina matuƙar ƙaunarta da na ganta shi nake tunawa amma ba za a kawo mini ita ba, sai wannan ƙartin ne kawai suke zuwa in da nake” ta yi maganar tana fashewa da kuka.

Mama cewa take “Allah ya baki haƙuri, in Allah ya yarda za a dinga kawota”.

Ruma kuwa ta kalli Gwaggo ta ƙyal-ƙyale da dariya ta ce “Dan Allah Gwaggo ki daina wannan kukan, ni wallahi fuskarki dariya take bani idan ki na yi, kin ga yadda ki ke yamutsa kuwa?”

Yaya Aliyu ya ce “Ai gara ta fara gwada miki halin”

Gwaggo ta tsaya da kukan ta ce “Rumaisatu, kukan nawa ne yake baki dariya?”

Ruma ta ce “Eh mana, amma ki daina ce mini wata rumaisatu, sai ka ce wata masara, kowa aka saka masa suna mai daɗi a gidan nan, amma aka saka mini wata Rumaisa kamar masa”

Gwaggo ta jinjina kai ta ce “Ikon Allah”
“Gwaggo wai ina wannan ‘yar ta ki, mai kamar ni ɗin nan?”

Jin ruma ta tambayi ‘yar autarta ya sanya Gwaggo yin murmushi ta ce “Au Lawisa tana nan ƙalau, ta na ta a gaishe ki, ita ana biki sun tafi da tuni tare zamu zo”

Ruma ta yi dariya ta ce “Wai Lawisa, ai har gara nawa sunan ma da nata, wata lawisa kamar za ace lawashi, ta fini girma yanzu?”

“A’a zaku yi tsayi ɗaya da ita”

Ruma ta yi murmushi tana kaɗa ƙafa.

Abubakar ya ce “Ruma ɗaga mata ƙafa mana”

“A’a ƙyaleta, ai haryanzu yarinya ce, Allah dai ya kai ni auranku ke da Lawisa”

Ruma ta ce “Amin, ki yi mini Addu’a, Allah ya sa na yi tsawo na isa aure, kuma Allah ya sa na auri kyakykyawa mai kuɗi sosai”

Mama ta riƙe haɓa ta ce “Ruma, ƙanƙanuwarki da ke, har kin san wani miji mai kyau mai kuɗi?”.

Gwaggo ta ce wa mama “Wai ke ina ruwanki da mu ne, muna hira kina saka mana baki” ta mayar da hankali kan ruma ta ce “Amin ‘yar albarka, Allah ya kai ki in da zaki huta, mu ci mu sha mu yi wadaƙa”.

“Amin, kuma Allah ya sa na auri me kyau”.

Aliyu ya ce”Da wannan shegen hancin naki kamar na aladae zaki auri me kyau?”

Gwaggo ta ce “Ƙarya ka ke dan ubanka, wallahi kamar ta ɗaya da babanku, kuma hanci ne da shi har baka, in Allah ya yarda sirikina kyakykyawa ne kuma mai abin hannu, tun da ‘ya ta ba daga nan ba”

“Gwaggo kin san wa nake so na aura?”

“A’a sai kin faɗa”

“Kina kallon wrestling?”

Gwaggo ta ce”A’a ni ban san shi ba”

‘To ball fa?”

“Ni ina zan ga wannan shirmen”

Ruma ta ce “Da kina kallo, da na gaya miki wanda zan aura a cikin su”.

Cikin son katse surutun da ruma ke yi ba kunya ba tsoro mama ta ce “Ruma tashi ki canza kaya, zan aike ki” ruma ta miƙe daga cinyar Gwaggo ta tafi sauya uniform.

Tun da Allah ya sa Gwaggo ta zo gidan nan, ruma taɓara ta ƙaru, don ko me ruma za ta yi ba zata bari a yi mata faɗa ba, gashi kullum cikin faɗa take da mai sunan Baba, dan kome za ta yi idan ruma tayi laifi hukunta ta yake yi.

“Wannan yaro da fuska kamar bajimin sa, ba ka da imani, wannan ‘yar tatsitsiyar yarinyar guda nawa take, da zaka dinga azabtar da ita wallahi Hauwa wannan ɗan naki mugu ne”
Gaba ɗaya ruma da Gwaggo suka gallabi gidan nan, ruma kuwa aka samu tikitin rashin ji dan ma tana tsoron mai sunan Baba.

Yau Malam Habibu yana babban aji, ruma tana tare da shi, yayi musu ƙari, tana ta wasanninta da ciye-ciye, sai da ya kammala yana amsa tambayoyi sannan ruma ta ce “Malam ka ce idan mace tayi mafarkin namiji sai ta yi wanka zata yi salla, to ni kuma kullum sai na yi mafarkin yayyena, Kuma ni sai zan tafi makaranta nake wanka watarana kuma mama ta ce bana fita tayi mini wanka, to yan…..
Kan ta ƙarasa ‘yan ajin suka hau dariya, dan ba zaka taɓa cewa hankalinta na kan abin da yake koyarwa ba.

Malam Habibu ya ce ” ‘ya ta ta kaina, ai wankan da mama take yi miki ya wadatar, duk ɗayane”

Ta ce “Au ho, na gane”

 

Tana dawowa daga islamiyya ta turke Abubakar ta ce “Yaya Sadik yau ka san meyafaru a makarantar islamiyya ?”

Sadik ya ce “A’a”

“Ka san na canza aji a islamiyya, saboda malaminmu baya ƙaunata, Ajin su Yasir kuma ya ce idan na ƙara zuwar musu aji sai ya dakeni, sai na koma ajin malam Habibu gaba ɗaya ajin ‘yan sauka”

Abubakar ya ce “To ban da abinki kin taɓa ganin an fara gini daga roofing, ai daga tushe ake farawa”

“Oho dai koma yane, wani karatu aka yi nake son na tambayeka, da zan tambayi malam Habibu na manta”

“To ina jin ki”

” ‘yan ajin ne da su da wasu na ga wataran ba sa salla fa, ko su ƙi zuwa da Alqur’ani izifi sittin wai Haila suke yi. Na tambayesu sai suka ce mini wai ai mata ba kullum suke salla ba, idan ba su yi salla ba haila suke yi ko biƙi. Aikuwa nima na ƙi yin salla, wata prefect ta ce me yasa ba na salla nima na ce biƙi nake”

Gwaggo da ta idar da salla ta ce “Subhanallahi” jin maganar ruman kamar saukar aradu.

Ita kuwa ko a jikinta, ta cigaba “Shi ne ta ce dan ubana ni na isa in yi biƙi, na ce ba dai ubana ba sai dai na ta, kuma tun da nima biƙi nake ba zan salla ba, ashe wataran mata ba sa salla amma ni kullum mama sai ta ce sai na yi”

Abubakar ya ce”To, wannan zancenku ne ke da maman ita zata baki amsa”.

Ruma ta ce “Mama…..”
Mama ta katseta ta hanyar cewa “Rufe mini baki, kar ki sake ki yi mini shirme, kuma ki tashi ki yi sallar da ki ka ce baki yi ba dan ubanki”

“To mama ai idan ana biƙi ba a salla”

“Biƙin ubanki, ke kin san meye biƙin ne?”

“To meye biƙin?”

“Ba zaki tashi ki yi sallar ba, sai na zane ki da bulugarin nan?”

Ta kalli Gwaggo ta ce “To ke gaya mini”

Kamar wadda ta tambayi meye wani babban zunubi Gwaggo ta ce “A’a ni babu ruwana, ga uwarki nan ta baki amsa ni zaki tambaya wannan babban al’amari ba a bakina ba, ‘ya’yan binki wayewar ku ta yi yawa”.

“Ohh ni ruma, komai na yi laifi ne, ai shikenan”

Tun daga lokacin ba ta kuma kula kowa ba, ta koma tayi shiru wai ita ta ji haushi.

Har zuwa sallar magariba, ba ta sake kula kowa ba, Gwaggo ma ta gaji da yi mata hirar, amma Ruma taƙi saurarata.
Yaya Sadik ne yayi gyaran murya ya ce “Ruma, wai ni kuwa idan kin girma me ki ke son ki zama ne? Da na je taron PTA ɗin ku an ce da kun shiga primary 6, za’a fara shirin common entrance, shi ne na ce idan kin shiga Sakandire me ki ke sha’awa Art zaki yi ko science?”

Ta kalle shi ta ce”Wai in din ga drawing?”

“Wane irin drawing kuma?”

“To ai ji na yi ka ce Art, Art ba drawing ba kenan?”

“A’a ba wannan ba”

“Ni dai kawai sana’ar da zan samu kuɗi nake so, ko kuma in zama ‘yar sanda, in dinga tsayawa a titi ina bada hannu masu mota suna bani kuɗi, ko kuma a buɗe mini kanti, ko na zama mawaƙiya ko ‘yar film!”

Ayshercool
08081012143
A TAIMAKA AYI SUBSCRIBING YOUTUBE CHANNEL ƊINA NA COOL HAUSA NOVELS, KO IN KOMA POSTING SAU ƊAYA A SATI 😒*
[11/07, 4:25 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER’S ASSOCIATES

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ku yi subscribing  YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.

 

Back to top button