Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 22

Sponsored Links

 

Wani mugun ɓacin rai ne ya kama ruma, kamar za ta yi kuka ta ce “Malam meye haka? Meyasa zaka taɓani ka cikani”

Cikin tsananin mamaki, da rashin abin yi yake sake sauraren muryar ruma “Da..d…dama kece, meyasa ki ke bibiyata mai na yi miki ne?”

“Ni yaushe na sanka ma? Ka cikani kafin na yi maka hauka da tijarar da zaka yi dana sani, ka sakar mini hijjabi”

Tsananta riƙon da yayi wa ruma ya yi, yana sake bin ta da kallo, yana jin tamkar ba shi bane ba, anya mutum ce yarinyar nan, ko kuma dai muryar ce ke cigaba da yi masa gizo.

Ganin yadda duk ya gigice kamar zai fita hayyacinsa, ya sanya Jabir ƙoƙarin cire hannun takawa daga jikin ruma.

“Takawa, dan Allah ka kula mana, yarinya ce fa ƙarama ba sa’arka ba, dan Allah ka saketa, sannan kamar yaya tana bibiyarka?”
Hankaɗe ruma yayi, ya koma gefe ya zauna, yana dafe goshinsa.

Kuka ruma take wiwi, ta ɗauki jakarta.

Jabir ya kalli wanda suka kawo ruma ya ce “Sidi ku mayar da ita”.

Suka tasa ruma a gaba, ta waiwayo ta kalli takawa ta ce “Wallahi ban yafe ba ku…..”

“Ke wuce mu tafi, kin samu an ƙyaleki kuma kina yi wa mutane iskanci, mara tarbiyya”

Cikin dakiya ta ce “Eh bani da tarbiyyar, ku tarbiyyar ce ta saka kuka ɗauko ni ba da sanin iyayena ba ku ka kawo ni nan, cikin maza Allah sai ya saka mini”

Jabir ya ce “Kar ka kuma tankawa yarinyar nan, mayar da ita”

Jabir ya zauna a kusa da takawa ya ce “Takawa, wa me yake faruwa ne, ka san ta ne?”

Adam yayi shiru bai motsa ba, kuma bai ce komai ba, Jabir ya yi masa tambayoyi har ya gaji, amma bai amsa masa ba.

Ruma kuwa suna zuwa unguwar su, suka ajiyeta suka tafi, ta samu wani borehole ta wanke fuskarta, sannan ta tafi gida.
A tsakar gida ta tarar da Yaya Aliyu, ya kalleta ya ce “daga ina ki ke?”

“Makaranta” ta bashi amsa tana ɓata rai.

“Ba jarrabawa ku ke yi ba?”

“Laifi muka yi aka saka mu punishment” ta bashi amsar tana tsoron kar ya ganota.

“Haka dai ki ka iya, kullum cikin laifi kamar ke kaɗaice ɗaliba a makarantar”

Ganin bai ganota ba, ya sanya ta shiga ɗaki, ta ajiye jakarta ta tafi gaban mudubi ta tsaya, ta ƙarewa kanta kallo, ta tuna yadda takawa ya shaƙeta hannunsa har yana taɓo ƙirjinta.
Wasu hawayen ne suka shiga ziraro mata. “Wallahi sai ka gane baka da wayo, ka zunguro sama da kara, ni za a ciwa mutunci? Wallahi sai na kuma rubutawa, zaka gane ba ka da wayo, ai talauci ba hauka bane, mai kyan banza” haka ta tsaya a gaban mudubi, ta cigaba da kuka.
Kamar zararriya ta ɗauko jakarta, ta ɗauko wayar ta kuma komawa kan account ɗin da Jabir ya saka hoton takawa, ta sake rubuta “Wallahi Allah ban yafe ba, sai na kai ƙararka wurin ‘yan sanda, zaka san da ni kake yi” ta ajiye wayar tana fatan Allah ya sa kar idan mama ta dawo ta fuskanci wani abu.

****

Baba uwani ce ta shiga kitchen ta tarar da iman tana faten dankali.

“A’a mutuniyar ba kya gajiya da aiki, Ammin ake yiwa girki ne?”

Iman ta yi murmushi ta ce “A’a baba uwani, nice zan ci”

“Au yau ba za a ci abincin namu ba ne?”

Iman ta yi murmushi ta ce “Ba haka bane, kawai da wannan ɗin nake sha’awa bana son takura muku ne”

“A’a ai da kin faɗa ma babu wani abu, sai ayi miki, ni kuwa na ce takawa lafiya ƙalau kuwa yake?”

Cikin rashin fahimta iman ta ce “Me ki ka gani?”

“Ganinsa na yi duk wani iri”

“A’a lafiyarsa ƙalau, ina ga hakan ya na da alaƙa da yanayin aikinsa, kin san abubuwa su kan yi masa yawa”

Baba uwani ta ce “haka ne wallahi, ina tausayawa takawa yadda al’amura suke shan kansa Allah ya yi masa jagora”

Iman ta ce “Amin” a dai-dai lokacin ta juye dankalin a plate ta ɗauka ta fice.

Baba uwani ta yi tsaki ta ce “Kai wannan yarinyar kininabbiya ce ba wani abu da zaka samu daga wurinta”.

Takawa fa abubuwa suka sake rikice masa, tun bayan haɗuwarsa da ruma, da ya ji muryarta da take masa yawo a kunne, yana ta tuntuntuni, mutum ce ko akasin haka, dan iya ƙwarin gwiwar ta, da rashin kunya da ayar tambaya a kanta.
Yau gaba ɗaya bai koma gida ba, ya wuce gidansa ya tura wa Ammi message a kan ba zai shigo gida ba, a gidansa zai kwana.
Bayan ya turawa Ammi saƙon, ya kuma komawa Instagram, ya duba comment ɗin da ruma ta yi a kansa, kawai ya ci karo da sabon saƙonta, ya tabatta kenan ita ɗin ce dai ta yi comment ɗin farko.
Kiran Ammi ne ya shigo wayarsa, ya saita nutsuwarsa ya ɗaga tare da yin sallama.
Ammi ta amsa sanna ta ce “Yanzu na ga saƙonka, ka sam yadda yanayin jikinka yake, amma ka ce zaka kwana a gidanka kai kaɗai, kar wani abu ya sameka fa”

“Ammi kar ki damu, babu abin da zai sameni in sha Allah, ina son gabatar da wani aiki ne”

“To shikenan, amma dai da ka ji wani abu ka kirani a waya”.

Ya jinjina kai ya ce “To shikenan, in sha Allah sai da safe” suka yi sallama ya katse kiran.

Ya rintse ido, yana jin muryar ruma na sake amsa kuwwa a kunnuwansa, ya tuna yadda ta danganta shi da sata, take ya ji ya tsani yarinyar, kuma daga uniform ɗin jikinta zaka gane ‘yar talakwa ce, amma sai ƙarfin hali da rashin mutunci, to yayi faɗa da wannan ‘yar ma ya ce ya yi da wa? Wani uban tsaki ya ja, ya koma ya kwanta yana ƙwafa. Ya kuma komawa ya na duba comment ɗin ruma, amma ya tarar Jabir ya goge posting ɗin gaba ɗaya.

***
Ko da mama ta dawo, ta tarar gaba ɗaya ruma ba ta da walwala, duk tayi wani iri, mama ta tambayeta ko ba ta da lafiya, ta ce ita lafiyarta ƙalau kan ta me yake ciwo, mama kuwa ta ƙayleta, amma ta cigaba da monitoring ɗin ta.
Yau ko wannan uban surutun da take kamar an jefeta a ka, babu ta yi shiru sai tunane-tunane take a ranta, a kan me za ta yi wa wannan ɗan tahalikin ta huce, gashi ita ba ta san a ina ma za ta sake ganinsa ba, balle ta gaggaya masa magana ta huce da abin da yayi mata.

Mama suna ta hira suna tsara yadda bikin saukar su Yasir zata kasance, ruma ta koma kusa sa Abdallah ta ɗan yi ƙasa da muryarta ta ce “Yaya Abdallah, dan Allah waye galadiman Kano?”

Ya dubeta ya ce “Basarake ne a Kano, ba shi ne aka ce yana Germany ba bashi da lafiya, meyasa ki ke tambaya?”

“Babu komai kawai tamabaya na yi, amma ba ya mutu ba?”

“Anya, gaskiya ban sani ba, na ji dai an ce yana Germany babu lafiya”

Ɗan shiru ta yi ta na tunani, a wurin Hauwwaliya kawai za ta samu abin da take so, dan haka ta sake gyara zama ta ce “Yaya dan Allah ranar juma’a mu je cikin gari”

“Ba zani ba, ina da abin yi ranar”

“Dan Allah, na ji mama tana waya da mamansu, an ce Hauwwaliya babu lafiya dan Allah ka kaini na ganta”

“Ke na ce miki ina da abin yi ranar”

“Ai Allah na ce, ka taimaka” ta yi maganar cikin magiya.

Abdallah ya ɗan yi tsaki ya ce “Zan yi tunani”

Ta ce “Dan Allah ka kaini”

Bai sake kulata ba, saboda baya son magiya, ruma kuwa ta ƙware a kanta.

***

Kamar wasa Samha ta kira Khalifa a waya, kamar dama jiran kiranta yaje, tana kira ya ɗaga.

“Adon gari ya kike?”

“Ba dogon surutu ba, ina son sanin deal ɗin da kake son mu yi, na gani idan zan iya”

Murmushi ya yi, tare da kashe sigarin hannunsa ya ce “Kin yi tunani kin ga ni ke da mafita dai kenan? Sai dai kin so ki makara dan na samu wanda ya kawo tayin shiga deal ɗin, ban sani ba ko ta wurnki aka samu bayani, amma duk da haka kema akwai role ɗin da zaki taka, a ina zamu haɗu?”

Cikin mamaki Samha ta ce “Amma waye haka, da har ka ke tunani ta hanyata ya ji labarin deal ɗin nan?”.

“Kar ki damu da sanin waye, mu haɗu a hotel ɗin da muka haɗu last”

Ta girgiza kai ta ce “No, kar ka manta ni ‘yar babban gida ce, ba zai yiwu ma din ga yawon hotel ba, ka sama mana wani wurin kawai”.

“To Shikenan, zan turo miki wani address ɗin, ki huta lafiya” ta sauke wayar daga kunnenta, tana tunanin anya ba ta yi garaje ba wurin amincewa da Khalifa ba tare da ta san aikin sa za ta yi masa ba?.

***

Ranar juma’a ana tashi daga makaranta ruma ta taho gida, saboda ta tirke Abdallah ya cika mata alƙawarin kai ta cikin gari, dan tuni ta tambayi mama, mama ta barta Abdallah ya kaita, musamman da ta ji ta ce Hauwwaliya zata duba.
Ƙasan zuciyarta kuwa, so take ta sake haɗuwa da takawa, ta yi rashin kunya ko ta huce abin da ya yi mata.
Duk wani hoton Adam yake kan account ɗin Jabir, sai da Jabir ya sauke shi, ƙarshe ma yayi blocking ɗin ruma, bayan yayi reporting account ɗin ta an rufe mata shi.

Abdallah ya ce “Sai dai ruma ta yi haƙuri, dan wani wurin za shi, amma mama ta ce ya daure ya kaita, dan ruma a zahiri damuwa ta nuna da rashin lafiyar Hauwwaliya.

Ba dan ya so ba ya tasa ruma a gaba zuwa mandawari, Hauwwaliyarma ta samu sauƙi, bayan sun gaisa da mutanen gidan, Abdallah ya ce da yamma zai zo ya ɗau ruma.

Hauwwaliya ta yi ta murna da ganin ruma, dan rabon da su haɗu tun wancan zuwan.
Bayan ruma ta ɗan jima, ta fara ƙoƙarin aiwatar da abin da ya kawota.

“Hauwwaliya, ina ne gidan Galadima ne?”

Hauwwaliya ta ce “Wai makaranta?”

Ruma ta yi tsaki ta ce “Galadiman kano”

“Wanne?”

“Au biyu ne?”

Hauwwaliya ta ce “Ai akwai Galadima na yanzu, wanda ba shi da lafiya yana Germany, sannan akwai gidan Galadiman kano wanda ya rasu”

Ruma ta ce “Wanda ya mutun”

Hauwwaliya ta yi dariya ta ce “Ke ai wan baban su Janna ne, jikar turakin nan da muka je gidan su biki ta bamu kaya, kuma yayan Galadiman kano na yanzu ne duk fa ‘yan uwa ne, sarautar ba a rabawa a bawa bare dole sai su”

Ruma ta yi tsaki ta ce “Ni fa ba nasaba na tambayeki ba, ina ne gidan na sa”

Hauwwaliya ta ce “Shi wa?”

“Ke wai ya ina magana kina raina mini hankali, maganar wa muke ne?”

“To ke meye alaƙarki da su da ki ke tambayata?”

Ruma ta ce “Assignment aka bamu a makaranta”

“Aka ce me?” Ruma ta ɓata fuska ta ce “Hauwwaliya, ni zaki wulaƙanta?”.
Hauwwaliya ta kwashe da dariya ta ce “Yi haƙuri, Galadiman da ya rasu gidansa a bayan gidan sarki yake, wani ƙaton gida gari guda, baki ga katangar gidan ba, doguwa sosai a nan dai gidan yake”

“To kin san ‘ya’yan gidan?”

“To meye alaƙata sa su da zan san ‘ya’yan gidan, suma ‘ya’yan gidan duk a cikin assignment ɗin suke?”

Ruma ta yi murmushi ta ce “A’a dan Allah in anjima mu je, ina son in ga dokuna”

Haka ruma ta din ga lallaɓa Hauwwaliya, suka tafi yakasai, har family house ɗin su Takawa.

Ruma ta yi mamakin girman gidan, ya fi na Turaki da suka je rannan, suka gama yawonsu suka koma gida.

Yau ma sai magariba sannan Abdallah ya ɗauketa, suka koma gida, sai dai tun da suka koma gida, ruma take tunanin ta ina za ta ga Takawa, dan ta ƙudirce a ranta ba zata haƙura ba.
Sai dai gate ɗin gidan na su kawai girmansa abin mamaki ne, babu wata ‘yar kafa da za ta bi ta shiga, ga masu gadi a zaune a ƙofar gidan, da alama shiga gidan ba zai zama abu mai sauƙi ba.

***
Tun da Samha ta koma gida, take tunani a kan abin da Khalifa ya zo mata da shi, dan ba abu ne mai sauƙi ba. Amma duk tunanin da ya kamata ta yi ta yi, shikaɗai me mafitar da ya rage mata, dan takawa hankalinsa sam ba ya kanta, idan har ba kawar da alaƙar nan ta yi ba, to ita da Adam sai dai kallo daga nesa, haka zalika sai ta yi ƙoƙari wurin takawa su Hajiya Jamila burki a wasu ɓangarorin dan idan suka nakasta shi, to ita suka yi wa.

***
Mama ta zauna ta tattauna da yaranta, a ƙarshe suka amince da a sayar gonar mahaifinsu ta can katsina  a garin Ƙanƙara, domin yin hidimomin da suke gabansu, masu registration ayi musu, masu exam a biya musu, masu buƙatar jari duk ayi musu. Sannan still akwai filinsu da aikin gwamnati ya bi ta kai, za a basu diyya.
Sai dai mama ta ce ita tsoron garin nan take ji, kawai ayi waya su sayar ɗan abin da ya samu da na diyyar a aiko musu, can dangin babansu suka hau mitar cewa mama ta mallake yaran ba ga son su je in da suje, ƙarshe aka yanke Aliyu zai je.
Yaya Abubakar ya ce “Dan Allah mama idan zai je, ya kai musu ruma, tun da dama exam za su yi, su yi hutu, ko a samu su daina surutun nan da suke yi na rashin zumunci, rabon da aje da ita garin fa tun yaye, rannan da na je baki ga mita da faɗan da suka din ga yi ba, wai kin fiye son ‘ya’ya, wayar da muka yi da baba Habu shekaranjiya a kan biyan diyyar nan shi ma ba ki ji faɗan da ya yi ba”.

Mama ta ce “Ba ƙi nake ba, ka san halin rashin jin yarinyar nan shi nake tsoro, ga yanayin garin babu lafiya”.

“Mama ai a cikin ido ake tsawurya, in Allah ya yadda babu abin da zai faru sai alkhairi”
Mama ta ce “To, Allah ya sa”

Ruma ta ji dadin batun tafiya da ita garin mahaifinta, amma gefe ɗaya ta fi son sai ta tafkawa takawa ɓarna, sannan su tafi yadda zai nemeta ya rasa.

***
Zaune take a kan kujerar da ke gaban mudubi, tana ta shafe-shafen turare, ƙamshi duk ya gauraye ɗakin, sannu a hankali ya tako gabanta yana kallonta.

“Mutum kwalliya sai ka ce aljana” dariya ta yi har sai da dimples ɗin ta suka lotsa, ta ce “To idan ban kwalliya ba me zan yi?”

Ya saka hannu ya fara jan kumatunta ya ce “Kai na yi missing kumatun nan naki sosai da sosai” ɓata fuska ta yi tana sake tura kumatun, shi kuma ya cigaba da ja yana dariya yana faɗin “My Chubby girl”.

***
Tun da aka ce za ayi tafiyar nan da ruma, mama take mata nasiha da ja mata kunne a kan tafiyar da za ayi da ita, a kan nutsuwa da kama kanta, musamman saboda rashin tsaron da yake garin.

Gaba ɗaya Instagram sun yi banning account ɗin ruma, dan haka yanzu ba ta hawa Instagram ɗin sam.

Mama har mamaki take, duk wanda ya ce za shi cikin gari sai ta ce za ta bishi, mama dai ba ta yi magana ba, ta cigaba da zira mata ido, ta gano sintirin me take yi haka a cikin garin nan.

Yau ma haka ta dage sai ta bi Aliyu, Allah ya taimaketa ya tafi da ita.

Bayan sun je, ruma ta faki ido ta fice, ta tafi gidan Galadima, domin aiwatar da abin da ta yi niyya, ta samu napep daga nan mandawari zuwa cikin yakasai.

A ƙofar gidan ta tsaya, tana kallo tana tunanin ta ina za ta shiga? Cikin dakiya ta tunkari ƙofar gidan, masu gadin suka zubo mata ido su ga iya gudun ruwanta.

Gadan-gadan ta nufi shiga, wani ɗan sanda yayi mata tsawa ya ce “Ke wurin wa ki ka zo?”

Ta ɗan yi jimm sannan ta ce “Wurin wani”

“Waye wanin?”.

“Sunanshi Adamu”

Wado ido suka yi gaba ɗaya suna kallon ruma “Ke! Baki da hankali?” Saroro ta yi tana tunanin me ta yi kuma?

“Ke haka ki ka ji ana kiransa da shi, zaki zo ki faɗi wannan sunan haka? Zaki bar wurin nan ko sai mun saka dogarai sun zane miki jikinki”

“Ai ni ban san me ake ce masa ba, dan Allah ku barni na shiga”

“Ke, ba a zuwa gidan nan sai da izini, wuce ki bar nan ko ki jira idan kin nemi izini sai ki shiga”.

“To a wurin wa zan nemi iznin?”

Ɗaya daga cikin su ya ce “Ke bar nan ko na yi miki duka a wurin nan, ji mini shegiyar ‘ya da baki fil-fil kamar robot”

Ta kalleshi ta ce “Ni ba shegiya bace ba, ka daina zagina” tayi maganar idonta ƙyar a cikin nasa.

Girgiza kai kawai yayi, dan idan ya tunzura sai ya jiƙawa yarinyar nan jikinta.

Ta samu wani ɗan tudu ta zauna, tana kallon hanya. Suka kunna sigari suna sha, ruma ta kallesu ta taɓe baki a hankali ta ce “An yi asara”

“Ke ki ka kuma hararata sai na miki duka, ki tashi ki tafi ko?”

“Ni dai ba a kanku nake ba, ku ƙyaleni mana” ta yi maganar tana kawar da kai, tana ji a jikinta ko zata wuni a nan, sai ta ga abin da ya turewa buzu naɗi.

Wata dattijiuwa ce ta nufo gidan, suna gainta da fara’arsu suka fara mata magana “Baba Sabuwa, kin dawo?”

“Wallahi kuwa, kun ganni sai yanzu ya aiki?”

Suka amsa mata da Alhamdilillah.

Ruma ce ta taso da sauri tana faɗin “Baba” baba sabuwa ta tsaya ta kalli ruma ta ce “Yarinya ya aka yi?”

“Dan Allah gidan nan zaki shiga?”

Ta ce “Eh, a gidan nake aiki”

“Kin san wani Adamu a cikin gidan?” Hangame baki baba Sabuwa ta yi, tana waige-waige da fatan Allah ya sa wani bai ji ba.

“Ke ‘ya ta ai ba a faɗar wannan sunan a gidajen sarautar kano, takawa ake ce masa, eh na san shi”

Ruma ta yi ƙasa da muryarta ta ce “Dan Allah abu zan baki, ki kai masa, so nake na ganshi an hanani shiga, amma dan Allah ki bashi wannan takardar hannu da hannu babata”

Baba uwani ta ce “To shikenan, amma in ji wa zan ce masa?”

“Idan ya ga takardar shi zai gane, dan Allah ki bashi ”

Baba sabuwa ta ce “to shikenan, zan bashi in Allah ya yarda”.

“Ku kuma da baku barni na shiga ba kwa ci kanku”

“Zo mu baki sigari ” ɗayan ya faɗa cikin iya shege.

“Sai dai uwar sigari” ta faɗa a hankali.

Tutsiye Baba sabuwa suka yi, a kan lallai ta basu takardar nan su duba, kar a shiga da wani mugun abu gidan, amma ta ce ba zata bayar ba.

Baba sabuwa, hadima ce a cikin gidan ita ma, ita ce shugabar hadimai a ɓangaren Mummy, kuma tana ɗaya daga cikin masu bata rahotanni a kan abubuwan da suke wakana a gidan.
Tun da baba sabuwa ta shiga gidan, take tunani ta kai wa uwar ɗakinta takardar su fara dubawa ko kuwa? Sai dai mummy ba ta nan, dan haka ta sanya takardar a ɗan tofinta, ta cigaba da ayyukanta.

Ruma kuwa jinta take wasai, kamar an yaye mata wata damuwa da take damunta, tana komawa maman su Hauwwaliya da yaya Aliyu suka rufeta da faɗa, dan babu wanda ya san ta fita, ko a jikinta kasancewar yau tana lissafin saƙonta zai je in da take so, sai Addu’a take Allah ya sa baba Sabuwa ta bayar da saƙonta. Aliyu ya tasa ta a gaba zuwa gida, suna tafe yana ƙare mata zagi.

Wajen ƙarfe biyar takawa ya tashi daga aiki, a gaggauce ya nufo gida, dan yau bai samu zuwa gidan ba sai yanzu.
A gate jami’an tsaro suka sanar sa shi zuwan wata yarinya, da take son ganinsa amma suka hanata shiga gidan, suka sanar masa da ta ba wa sabuwa takarda ta ajiye masa.

Bai kawo komai a ransa ba ya shiga gidan, yana tunanin wacce yarinyar ce haka?.

Yana yin parking ya wuce sashin Mummy, ko da ya shiga falon, Fauziyya ya tarar, jiki na rawa ta yi masa sannu da zuwa.

Bai amsa ba ya ce “Kira mini Baba sabuwa” ta miƙe tana tunanin me yasa yake neman Baba sabuwa a yammacin nan?.

Baba sabuwa ta risuna tana gaishe shi, ya miƙa mata hannu ya ce “Bani saƙona” babu musu ta fito da takarda ta miƙa masa. Ya juya ya fice.

Fauziyya ta ce “Sabuwa, takardar mecece?”

“Wallahi wata yarinya ce ta tsareni a ƙofa, ta ce a bashi ban san yarinyar ba ma”

“To meye a ciki?”

“Ai kin san ba iya karatu na yi ba”

“Kuma da baki iya karatun ba, mai ya hana ki kawo mini, tashi dalla usless” Sabuwa ta tashi cike da haushin tsawar da Fauziyya ta yi mata, duk da ba yau ta fara ba.

Bai tsaya duba takardar ba, ya jefata a cikin jakarsa ya tafi wurin Ammi.

Gaba daya ya manta da takarda, sai washegari da daddare yana neman wasu takardu, takardar ta faɗo.
Ya buɗe takardar wasu ‘yan ƙananan rubutu ne, marasa kan gado a cikin takardar, bai yi zaton rubutun zai karantu ba sai da ya fara karantawa, duk an gwamutsa Capital da small latter’s.

*Da farko dai zan fara da yi maka Allah ya isa, dan da alama baka da ƙanne mata shi ya sa ka yi mini abin da ka yi mini. Kamar yadda ka saka aka nemo ni, nima sai da na gano gidanku. Ka saka aka ɗauko ni, ka zageni kuma ka ci mini zarafi, to wallahi ban yafe maka ba taɓa mini nono da ka yi, ina ta kaffa-kaffa da mutuncina, ina kula da kaina amma ka shaƙoni hannunka yana taɓa wurin, kuma bayan idan namijin da ba muharramin mutum ba ya taɓa shi ciki yake yi, to wallahi Allah ya isa ban yafe ba, kuma idan ciki ya sameni sai na kwaso maka yayyena mun zo har gidanku na gaya wa mamanka abin da ka yi mini, kuma na faɗa an saci kuɗin talakawa an je karatu ƙasar waje. Mu zuba mu gani daga maƙiyiyarka  RUMAISA MAHMUD ƘANƘARA ƊORAYI TUNGA ƘANWAR MAZA Kazo ka kasheni*

Zuruu takawa ya yi yana bin takardar da kallo, zuciyarsa na sake karkata ga ruma aljana ce. Ya maimaita sunanta *RUMAISA!* Tunani ya tafi yi, ko ya ga wani abu mai kama da nono a ƙirjinta ranar da aka kai masa ita.

Ta yaya aka yi ta gano gidan su har ta kawo wannan takarda? Rubutun nata cike yake da wauta da ƙuruciya.

“Zan ƙure miki gudu, zan gane idan ma ba mutum ba ce, da ni ki ke zancen” ya maimaita wasiƙar nan ya fi sau goma, babu abin da ya fi ƙular da shi irin wai ya taɓa mata nono, duk da bai riƙe cikakkiyar suffarta ba, amma shi ba ya tunanin akwai wani nono a jikinta.

Mama ta haɗawa ruma kayanta cif, da zummar gobe da sassafe za su tafi ita da yaya Aliyu, yau kuma Alhamis za ta je za su yi exam ta ƙarshe, haka kurum mama ta ji ba ta son tafiyar nan da ruma, amma ta bar hakan a alhini, kasancewar ruma ba ta taɓa nisa da ita na kwanaki ba, ga kuma rashin ji irin na ruman.

Uniform ɗin ruma sun sha guga, karin nan ya tsaya ɗoɗar Abdallah ne ya goge mata su, sai ƙamshi take, sai dai kamar kullum tana tafe tana zira hannu a aljihunta tana ciye-ciye.
Kamar a mafarki ruma ta ga an wanketa da ruwan kwatamin ruwan sama da aka yi ya kwanta, ƙazantar ruwan har fuskarta. A gigice ta tsaya cak, ta buɗe idonta, dan ta ga wani mara mutuncin ne ya ci mata zarafi haka?

A hankali ya sauke glass ɗin motar, suka yi ido huɗu da Rumaisa. Bakinta mutuwa yayi ta ma kasa magana gaba ɗaya.

Buɗe motar ya yi ya fito yana ƙare mata kallo.

“Ko zaki rama ne, ko da yake ba ki da abin ramawa ai, banbancin talaka da mai arziki kenan, na ga saƙonki, abin da ki ka ce na taɓa ɗin ni ban ganshi ba ranar, shi ne na biyoki yanzu in duba in gani ko akwai”.

“Wai kai ɗan iska ne?” Tayi maganar ba tare da jin nauyinta ba, ga babban mutum kamar Takawa, saboda ya kaita bango.
Maganar ta dake shi, amma ya ce “Eh shi ne, yayyen naki maza da ki ke taƙama da su, sai na kamasu na rufe, kuma na rushe gidan na ku, na ga ta tsiya”.

Karo na farko da ruma ta tsaya aka sakata kuka, hawaye ya wanke mata fuska.

“Wallahi sai ka yi dana sanin abin da ka yi mini, daga yau ba zaka sake yi wa wani abun da kayi mini ba, ba dai taƙamarka kuɗi ba, to ni nan Rumaisa kai da kuɗin naka da sarautar ta ka sai ka durƙusa mini a kan gwiwoyinka, kuma ka saka a ranka nice nan abokiyar gabarka” tayi maganar har da dukan ƙirjinta.

Girgiza kai ya yi, ya buɗe motarsa ya shiga, ta durƙusa ta ɗebi taɓon wurin ta fara watsa wa motarsa, ya taka reverse ya sake wanketa da taɓon wurin ya tafi.

(*ALHAMDILILLAH, TIRKA-TIRKA, YA KUKE GANIN ZATA KAYA A TSAKANIN RUMAISA DA TAKAWA? WACE IRIN LARURA CE DA TAKAWA, KUMA MEYE ALAƘARSA DA MAITA DA HAJIYA JAMILA TA FAƊA? YA ZATA KASANCE? WANE DEAL NE KHALIFA YA SAKA SAMHA? MEYE TARIHIN GIDAN SU TAKAWA, DA ASALIN GABARSA DA ƊAN UWANSA. ME ZAI FARU IDAN RUMA TA JE KATSINA??? WA RUMA ZATA AURA, SHIN ZA TA NUTSU KO KUWA? KAR AYI BABU KU, MAI BUƘATAR BOOK2 YA TUNTUƁENI TA LAMBAR WAYATA 08081012143 YA YI PAYMENT*

 

Back to top button