Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 28

Sponsored Links

Ayshercool.

Paid book ne, 500 ne via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143, wanda suke ba a Nigeria ba kuma, za su iya saya a arewabooks*

Gaba ɗaya suka bi ruma da kallo, ita kuma ta ƙare masa kallo ta ce “in biyo ka mu je ina?”.

“Cewa ki ka yi sai dai ayi miki duk abin da za ayi miki, abinda yakamatan zan miki ai”.

Ruma ta ce “Koma mene ka yi mini a nan ba in da zani”

Mutumin da yake ta ƙoƙarin bata kariya ya fara fusata ya ce “Wai ke wace irin yarinya ce?, duk yadda za ayi a kare mutuncinki a rabu lafiya ana yi, amma ke sai ka ce baki san ciwon kanki ba, ke kin san me zai miki ɗin ne ki ka tura baki kina cewa ayi miki koma menene?”.

Cikin kuka ta ce “Ta ina kake kare mutuncin nawa, da kuka haɗamu maza da mata kuka rabo ni da ‘yan uwana, yanzu ka gama cewa a kasheni, wallahi babu in da zani daga nan, koma me zaku yi mini ku yi mini ni na gaji”

Su kansu waɗanda aka kamo su tare da ruma mamaki suke yi, yadda take rashin mutuncinta yadda ta ga dama.

Ƙaton nan ya sanya ƙafarsa iya ƙarfinsa ya taka ƙafar Rumaisa, ta riƙe kanta ta yi wata irin ƙara, ba ta warke daga waccan azabar ba ga wata ana gana mata, ji ta yi kamar ya karyata, saboda azabar da ta ji, dan ƙato ne na gaske.

Mutumin da haryanzu ba ta san sunansa ba ya ce “Ina ga daga yanzu ba zan sake magana ba, su yi miki duk abin da zasu yi miki, akwai dalilan da yasa nake baki kariya, amma tun da ke na fuskanci baki da hali, duk abin da aka yi miki ke ki ka saya, idan baki nutsu ba haka zaki ta shan baƙar wahala, kina raye amma na lahira sai yafi ki jin daɗi, ki cigaba mara kunyar banza”.

Fuska duk hawaye cike da dakiya ta ce “Eh ayi mini ɗin, ku kasheni daga nan sai me?, wallahi ba zan daina magana ba sai kun gaji kun kasheni, kuma ba lambar wanda zan bayar a gidanmu, ku da Allah ba zan yafe muku ba, ba laifin da na yi muku kuke cutar da ni, Allah ya saka mini duniya da lahira”.

Buɗe baki yayi yana kallon rumaisa, ga fuska duk busashen jini, amma sai kwaroroto take ba tare da ta na tsoron ayi mata wani abu ba.

Aikuwa ƙaton nan ya dinga takata da ƙafarsa, yana dukanta tana ihu tana “La’ila ha illa anta, subhanaka inni kuntu mina zalimin” shine kawai abin da take maimaitawa, dan idan ya takata ji take kamar ana buga mata itace, ko wani nannauyan ƙarfe.

Ɗayan kuwa yana kallo bai kuma cewa komai ba, sai da ƙaton nan yayi mai isarsa ya ƙyale ruma, ba dan ta yi shiru da bakinta ba, sai dai ihun ma da ƙyar take iya yin sa saboda ta galabaita. Haka kowa ya zura mata ido yana kallonta, duk wurin ita ce ƙarama sauran duk da girmansu, amma tafi kowa baki da rashin mutunci.

A gigice mama ta dafe ƙirjinta, hawaye na zuba daga idonta, mutane na ta bata haƙuri, amma a zuciyarta take jin kamar wani na faruwa da rumaisa, mussaman da zuciyar ta ta ta tsananta bugawa.
Idan ka ga mama sai ka zata wani ciwon tayi, duk da ba mace ce mai ƙiba dama, amma ba ramammiya bace ba, tana da kumarinta, amma lokaci guda duk ta zube sai tsawo.
Ba ta iya cin abinci sai su Abubakar sun yi da gaske, da rarrashi da ban baki, ake samu ta ɗan sha abu mai ruwa-ruwa. Duk wata walwala da ake a gidan nan suka dainata, bacci kuwa sai dai ɓarawo, babu mai iya yin sa yadda yakamata a gidan.

‘yan uwa da abokan arziki ana ta shige da fice, ana yi wa mama jaje tare da addu’a Allah ya baiyyana ruma.

Habiba ce ta faɗo gidan su rumaisa a gigice, ta din ga kallon yayyen rumaisa da mutanen da suke zazzaune, can ta hango mama, ta ƙarasa wurinta da gudu, ta zube a kan gwiwoyinta “Mama, wai da gaske an sace ruma?”

Mama ta ƙura mata ido, amma ta kasa magana.

Maƙwabciyar su ruman ce ta ce “Eh da gaske ne, yanzu ku je ku yi ta yi mata addu’a, Allah ya bayyanata cikin aminci, ya tsareta a duk in da take”.

Rushewa da kuka habiba ta yi, tana wata irin sheshsheƙar kuka, gaba ɗaya ta gigice tana wani irin kuka.

A fusace mai sunan Baba ya ce. “Dalla ku fitar mana da mai ihun nan, da wane zamu ji?”

Aliyu yayi saurin cewa “A’a ba haka yakamata ayi ba, akwai shaƙuwa a tsakanin su, bai kamata a hantareta ba”

Aliyu ya fita ya je ya samu Habiba, ta haɗa hawaye da majina tana kuka, ya tuna faɗace-faɗacensu na ƙuruciya tsakaninta da rumaisa, kullum cikin sintirin kan ƙara ake, da yadda yake zaneta ita da yayanta a kan ruma, amma yau ta tayar da hankalinta saboda ɓatan ruma.

Hannunta ya kamo ya ja ta gefe yana rarrashinta, amma babu alamar za ta yi shiru, duk jijiyon kanta sun ɗaga idonta yayi jawur saboda kuka.

“Kiyi shiri kar kanki yayi ciwo, sannan addu’a zaki taya mu, Ubangiji Allah ya bayyana mana ita, ki daina kukan, mu je na raka ki gida”

“Allah ya sa kar a kasheta, Allah ya sa ta dawo gobe” ta faɗa tana sake fashewa da kuka.

Ƙwalla ce ta cika idon Aliyu, domin kuwa dauriya kawai suke yi, ya wayance ya ce “Amin ya Allah, dan idan kin yi salla ki din ga sakata a addu’a kin ji”
Habiba ta jinjina kai, tana cigaba da share hawaye. ya saka ta a gaba ya rakata gida, amma yanayin tashin hankalin da take ciki, zai tabbatar maka da ta kaɗu sosai da ɓatan ruma.

Hauwwaliya ma da take a zaune tana jinyar karayar da ta yi kafin tafiyar runa, ita ma haka ta burkice, dan da har tana mitar ruma ta tafi ba ta zo ta dubata ba balle su yi sallama, sai labarin an yi garkuwa da rumaisa suka ji.

Hatta malamansu ruma na makarantar islamiyya da take gallaba, gaba ɗaya suka shiga damuwa, makarantar kanta kamar ana zaman makoki, saboda babu wanda bai santa ba da halinta. Ita kanta tsohuwar da take sayar da kayan yara a makarantar, da suke yawan faɗa da ruma sai da ta yi kuka, dan wataran idan sun yi faɗa wata ran suna shiryawa, dan idan ruma ta zo da abinci wataran tare suke ci, duk rashin jin ta akwai shiga rai.

Takawa yana kwance a ƙaton falonsa a kan doguwar kujera, yayi zurfi sosai a cikin tunanin da yake yi, abubuwa da dama sun yi masa yawa, gaba ɗaya ya rasa wace matsalar yakamata ya fara tsayawa ya nemi mafita a kai, duk matsalar da ya tunkara, sai abubuwa sun ƙara taɓarɓarewa.

Wani irin zazzafan zazzaɓi ne ya kama ruma, saboda wahalar da ta sha, ga azabar cizon sauro da kuma sanyi suka haddass mata zazzaɓin.
Babu wanda yake ta tata, balle ya taimaka mata, tuni wasu aka fara bayar da kuɗin fansarsu, idan sun ga dama su bayar da mutum, idan ba su ga dama ba su karɓi kuɗin sannan su kashe mutum su ja gawar zuwa bayan wani babban dutse da yake nesa kaɗan da in da suke ajiye mutanen su yar gawar ba tare da suturta gawar ba.

Ruma na kwance ta takure tana ta rawar sanyi, ga azabar ciwon jiki, saboda dukan da ta sha, wasu mutane suka zo a kan babur, wanda aka goyo hannunsa ɗauke da ƙatuwar jaka, ta ɗaga ido dan ta ga su waye, wa za ta gani, dattijon bafullacen nan, da ta haɗu da shi har ya rakota gida a garin su Gwaggo.

Kallonsa take, amma ya kawar da kai kamar bai taɓa ganin ruma ba, ya basu jakar, shima suka bashi wata jakar ya hau babur ɗin aka bar wurin da shi. Tunani ta shiga yi a kan abubuwan da ya gaya mata, da kuma tunanin meye alaƙarsa da wannan mutanen? Kenan duk shiri ne?” Idonta ya sauka a kan lambar dake jikin jakar, sak irin lambar jakar da aka nuna mata bullet a ciki lokacin da za su zo katsina!

Guntun tsaki ta ja, a lokacin da ihun wani mutum ya dawo da ita hayyacinta, kan ta gano dalilin da ya sanya mutumin yake ihun, sai ganin abu ta yi a jikinta kamar an watso ruwa, jinin mutumin ya ɓata su an kashe shi.

Gaban ruma ne ya tsananta faɗuwa, ta ma rasa wani halin yakamata ta shiga, tashin hankali ko kuma fargaba, ga jikinta babu daɗi, ta fara fidda rai da samun mafita.

A hankali ta tashi zaune, ta ƙarasa gaban wanda ya kashe mutumin, ta kalleshi ta ce “Dan Allah nima ka kasheni”

“Saboda me zan kasheki?”

“Na gaji da zaman wurin nan, dan Allah ku kasheni nima” tayi maganar cikin magiya.

Ya kwashe da dariya ya ce “Ai ke zaki yi mana amfani,  ko zamu kasheki sai mun koya miki hankali tukuna, dan ba zaki taɓa barin hannunmu ba, an jaddada mana mu kula da ke, bakinki ba shi da linzami, ko mun karɓi kuɗin fansarki kashe ki zamu yi”.

“Idan kuma baku karɓa ba fa?” Ta tambayeshi.

Ya bata amsa da “Nan ma kasheki zamu yi”

“To ku kashe ni, dan ba wanda zai baku kuɗin fansata, bamu da kuɗi talakawa ne mu”

Dariya yayi, ya cigaba da busa sigari, ya share ruma.

***
“Daddy, ina ganin kamar yadda nace ka bar komai a hannuna, komai ya kankama, kawai mu cigaba da abin da muka saka a gaba”

Senator usman wakili ya girgiza kai ya ce “Ni fa haryanzu a raina ban gama gamsuwa da shirin nan naka ba Khalifa”

Khalifa ya gyara zama ya ce “Please Daddy, ka yarda da ni, ba zan baka kunya ba kamar yadda na yi maka alƙawari zan cika, Ni dai na riga na saka rai, bana son damar ta wuce ni”.

“Ni kaina ba zan so damar ta wuce mu ba Khalifa, amma yaron nan yana da taurin kai da nacin tsiya, bana tunanin zai ƙyalemu, ina matuƙar jin tsoron kar ya tona mana asiri”

Khalifa ya ɗan girgiza kai ya ce “Amma daddy, sauran members ɗin naku ma sun san abin da ake ciki?”

“Sun sani sarai, abin da nake tunani, akwai masu bashi goyon baya da haɗin kai a kan ya kawo ƙarshena, ba wannan ne ya fi ɗaga mini hankali ba, ina tsoron ya bankaɗo mu, dan ko last week na ji yana Abuja ku san kwanansa bakwai a can”.

Cikin damuwa da tashin hankali Khalifa ya ce “To yanzu shikenan daddy, babu wani abun yi?”

Usman wakili ya kwashe da dariya ya ce “Abun yi kai, ka zuba ido kawai yaro, babu wani abu da zai iya, muna da wani shiri a ƙasa”.

“Allah daddy, shirin menene?”

“Kar ka damu, idan ya tabatta za ka gani, kaima ka je ka cigaba da naka ƙoƙarin zan gani idan zaka iya zama magajina”

Khalifa ya yi murmushi ya ce “To shikenan daddy, ba ka da matsala da ni”

***
Iman ce zaune a falo, an saka mata lalle ja, tana ta kwaɓe fuska za ta yi kuka, wai ita ta gaji ammi sai mita take ta ce “Aikuwa kina tashi sai ranki ya ɓaci, ku kamar ba mata ba mutum yayi ta fama da ku a kan ku dinga ado”.

“Ammi fitsari fa nake ji” tayi maganar a shagwaɓe.

“Yi a nan a wanke”.
“Mhmm ammi zan yi kuka fa ya matseni”.

“Ki bari na zo na sameki a wurin nan kin cire lallen nan, ki ga yadda zan yi da ke”.

Jabir ne yayi sallama, Ammi ta amsa ya ƙarasa cikin falon yana kallon iman.

Kan nan nata babu ɗan kwali, gashin kanta sai ɗaukar ido yake ya sha mai, ta tufke shi. Haɗe rai ta yi ta kawar da kai, ya zauna suka gaisa da Ammi, daga nan ya hau zuba kamar an kunna shi, amma hankalinsa ba akan hirar da suke take ba, a kan iman take da ta basar kamar ba ta san da zamansa a wurin ba.
Ganin ba shi da niyyar tashi ne ya sanya Iman tashi, dama a iya hannu aka saka mata lallen, ta wuce ɗakinta.

Ko da ta koma ɗakin zama tayi tai shiru, tana tunanin irin balahirar da jabir zai jefata a ciki muddin ya ce yana sonta, kuma yadda yake da ammi babu abin da zai hana ammin amsawa, dan kamar ɗa shima ta ɗauke shi.

Baba uwani ce ta yi wa ammi ƙarya a kan zata je ta dawo, ammi ta bata izinin fita.
Tana fita ba ta tsaya ko ina ba, sai harabar gidan ta tabbatar da babu wanda ya ganta ta yi wuf ta faɗa sashin Mummy, ta ɓarauniyar hanyar da ta saba bi.

A ɗaki ta iske Mummy, Mummy ta dubeta cikin mamaki ta ce “Uwani, me ki ka shigo yi nan da yammacin nan sai an ganki”.

“Allah ya huci zuciyarki uwar ɗakina, Allah ya baki yawan rai, wani labari ne nake tafe da shi, ban sani ba ko zai yi daidai da abin da ki ke son ji ba”.

Mummy ta numfasa ta ce “Ina jinki”.

“Dama wani al’amari nake ta sanyawa ido, in tabattar da shi, amma ina hasashena yana daf da zama gaske, Jabir naku na gidan Galadima mai ci a yanzu, kamar shi ne yake sinsina iman, akwai alamun yana daf da cewa yana sonta”.

Wani uban tsaki Mummy ta ja, “To ni ta ina hakan ya shafeni, ni abin da na saka ki ki yi mini kenan? Ki saka mini ido ki kawo mini labari a kan abin da ya shafi ahalin gidan nan kin kawo mini maganar bare wadda ko gashi ba ta da shi a cikin gidan nan, ni ina ruwana na saka ki aikin samo mini maganin da suke yi wa wancan uban ciwon Adam amfani da shi, amma haryanzu shiru kin tsaya kawo mini shirme”

Baba uwani ta duƙa ta ce “Tuba nake, Allah ya huci zuciyarki, Allah ya sanyaya ruhinki”.

“Tashi ki bani wuri, kar ki sake zuwa in da nake idan har baki kawo mini abun da na ce ba”.

“In Allah ya yarda ba zan dawo ba sai da saƙonki, tuba nake”.

Kwanki goma kenan da sace ruma, amma babu wani labari a kan ta, tun mai sunan Baba yana buga waya ko da wani labari, har mama ta ce yayi haƙuri ya daina kiran wayar.
Shi kansa dagaci ba yadda bai yi ba ayi sulhu, su faɗi abin da suke so a basu su sako wanda suka kama, amma suka ce ba zasu bayar ba, yayi musu maganar rumaisa amma suka ce su ba zasu iya gane wata yarinya da suka ɗauka a gidansa ba.
Ruma kuwa sai gwada musu halin take na azabar taurin kai da rashin kunya, wataran ta yi borin amma sun ƙi su kasheta kamar yadda take fata, sannan suka fara yi mata horon yunwa, basu cigaba da takurata a kan sai ta bayar da lambar wanda za a kira a gidansu ba, suka ƙyaleta sai dai tana ganin azaba, idan ta ishesu da rashin mutunci, da kan bindiga suke dukanta.
Duk jikinta yayi tsami, ta fita hayyacinta kamar ba ita ba, ga rashin lafiya da take ta fama, wasu ko ba a kashe su ba wahala ce take kashe su a wurin, ruma ta fara sanya ran ita ma wahalar ce zata yi ajalinta.

Tun ruma na iya addu’a har ta fara sarewa, tayi kukan ta kira maman har ta haƙura ta zubawa sarautar Allah ido.

Tana nan kwance kamar matacciya, ta ji wani irin ƙamshin turare mai daɗin gaske ya gauraye wurin.

Wata mata ce take kuka, amma kamar iyayi matar take a cikin kukan, ruma ta ɗago da ƙyar ta kalli matar.
Tsohon ciki ne a jikin matar, duk da ruma ba ta san kan ciki ba, amma yadda cikin matar yayi girma kana gani ka san ta kusa haihuwa, matar na sanye da wani irin farin leshi mai ɗaukar ido da hankali, mai ɗauke da golden a jiki, hannunta zuwa kunnenta duk gold ne. Kai da gani ka san ba a wahala take ba, gata fara sol kamar ba ta shiga rana, sai kuka take ƙafarta na ta zubar da jini tana haki.

“Rufe mana baki, ko mu harbeki a ciki” suka yi mata tsawa toshe bakinta ta yi da hannunta ta zauna tana kuka, tana ƙarewa wurin da taken kallo.

Tausayinta ne ya kama rumaisa, ita wannan ƙaton cikin na matar ne yafi ba ta tausayi. Ita kuma ko a ina suka ɗaukota oho?.

Fatar matar duk tayi burɗun-burɗun, tayi jaa, alamar ƙwari duk sun cijeta a hanya kan su ƙaraso.

Ayshercool.

Back to top button