Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 40

Sponsored Links

Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau’in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*
Abubakar ne ya shigo, yana dira daga tasha ya wuto asibitin ba tare da ko gida yaje ba, da gudu ya ƙaraso ya rungume rumaisa, ko sauran mutanen da ke ɗakin bai kalla ba, ya rungume rumaisa yana zubar da hawaye.

“Yaya Sadik ɗina” rumaisa ta yi maganar tana ƙanƙame shi tana kuka”

Bashir ya kalli Usman ya ce “Abokina, wai har ku nawa ne yayyen nata ne?”

Usman ya yi murmushi ya ce “Mu bakwai ne, ita ce autar mu”

“Masha Allah, ba wanda zai ce mamanku ce ta haifeku, sam ba ta tsufa ba” yayi maganar yana murmushi.

Abubakar ya kalli Usman ya ce “Meyasa ba a gaya mini tun a jiya ba, sai yau da asuba Aliyu ya gaya mini”.

“Mama ce ta ce kar a gaya maka, kar ka ce zaka taho a jiya, ga wanda ya tsinto ta a katsina nan” yayi maganar yana nuna masa bashir.

Abubakar ya nufe shi ya miƙa masa hannu yana faɗin “Ɗan uwa, mu gode mun gode Allah ya saka maka da alkhairi, tun da aka ɗauki rumaisa muka rasa nutsuwa mun gode sosai Allah ya biya” ya sake komawa wurin ruma yana dubata ya ce “Allah sarki autarmu, haka ki ka koma duk kin rame ruma, kullum tunaninki muke yi”

“Nima kullum sai na yi tunaninku, sai na ganku a mafarkina” tayi maganar tana sheshsheƙar kuka.

Bashir ya dubi Adam ya ce “Akwai buƙatar mu tafi, na san masu zuwa dubiya zasu yi ta zarya, mu ƙyaleta ta keɓe da ‘yan uwanta” takawa bai iya cewa komai ba, Bashir ya ja hannunsa suka fita.

Suna tafe a hanya Adam ya ce “Ka wuce da ni gidana, bana son komawa gida yanzu”.

Bashir ya ce “Shikenan, amma dan Allah kar ka je ka damu kanka, ko ka yi ta tunani, hakan ba wani amfani da zai yi maka” still dai Adam bai ce masa komai ba.

Can bashir ya kuma cewa “Amma it seems you know each other before kai da yarinyar nan, a ina ka santa?”

“Bashir, dan Allah ka ƙyaleni, ina cikin tsaka mai wuya, dole yarinyar nan ta yi magana, kan al’aamrin nan ya ƙara kwaɓewa” yayi ya a hasale.

Bashir ya ɗan gyaɗa kai ya ce “Haka ne, amma dole ka rage zafin zuciyar nan mu bi a hankali, dan yarinyar nan da alama gardamammiya ce ta fika taurin kai” ya cigaba da tuƙi, ba wanda ya kuma cewa komai.

Can gidansu Adam kuwa, su Iman suka ƙara shiga damuwa, ganin ammi ba ta fito karyawa ba, kuma sun je wurinta hadimarta ta tabattar musu da cewa ta ce kar wanda ya je wurinta, tana buƙatar kaɗaici.

Cikin damuwa Nusaiba ta ce “Iman, ko ke kin san wani abu ne da yake faruwa, why are they behaving like this? They all look strange today”

Cikin damuwa iman ta ce “Tare fa muka kwana muka tashi da ke, ban san komai ba, nima dai na shiga damuwa da mamaki, wani abu yana faruwa amma maybe ba sa son mu sani ne”.

“Amma ko menene wannan, abu ne mai girman gaske, tun da har ta kai ga ammi ta ce kar wanda ya je wurinta, ga takawa tunda suka fita da abokinsa bai dawo ba” suka koma suka zauna suna tattaunawa a falo.

Baba uwani ce ta same su ta ce “Yaran nan meya samu giwar Galadima ne yau, daga ita har ɗan gidana na kasa gane kansu yau, ko abinci ba ta bari an shigar mata da shi ba, shi kuma ina magana bai ko kalleni ba, duk da miskili ne amma ba ya shareni idan na gaishe shi”
Iman ta ce “Zancen da muke yi kenan, bamu san meyake faruwa ba”

“To Allah ya sa dai lafiya” tayi maganar ba tare da ta ji daɗin rashin samun wani bayani ba.

Ƙamsshin turarensa da ya daki hancinta ne ya sanya ta san shine, a take ta ƙara tsuke fuska.

“‘yan matan ammi, ya na ganku kun yi tsilli-tsilli da ido kamar marasa gaskiya ne?”

Nusaiba ce ta fara cewa “Uncle J ina wuni?”

“Lafiya lau” ya amsa yana ƙarewa iman kallo. Banza ta yi masa taƙi kulashi.

“Iman ba zaki kulani ba?” Sunkuyar da kanta ta yi tana wasa da yatsun hannunta.

Ya ja wata irin ajiyar zuciya ya ce “Ina ammi ne?”

Nusaiba ta ce “Tana hutawa ne, ta ce kar a dameta yau”

“Takawa fa, tun jiya rabona da shi, ga wayoyinsa ba sa shiga gaba ɗaya, a gidan nan ya kwana ne ko gidansa?”

“Eh a nan ya kwana, amma yanzu baya nan”

Ya ɗan yi shiru sannan ya kuma cewa “Ba ku san in da ya tafi ba?”

Nusaiba ta waro ido ta ce “Uncle J, takawa ne zai gaya mana wani wuri da za shi? Bamu sani ba”.

“Wai ya nake ganinku duk wani iri ne, ko akwai abun da ku ke ɓoye mini?”.

Nusaiba ta ce “A’a Bakomai”.

Miƙewa iman ta yi zata bar falon “Iman” ya kira sunanta.

Ta tsaya cak ta waiwayo tana jiran abun da zai ce.

“Zo ki zauna ina da magana da ke”

Ji ta yi tamakar ta ce ba zata dawo ba, amma ta nemi wuri ta zauna.

Yayi wa Nusaiba alama da ido, a kan ta basu wuri. Ba musu Nusaiba ta tashi ta bar falon.

Kujerar two seater da iman ke kai, ya zo ya zauna, ya ɗan tsura mata ido, amma ta takure jikinta, kamar yana motsawa zata zura da gudu.

“Iman” ya kira sunanta, ta ɗan ɗago amma ba ta kalleshi ba.

“Meyasa ki ka yi blocking ɗina a what’s app, da phone ɗinki gaba ɗaya?” Tayi shiru tana sauke numfashi.

“Am talking to you, or just because i ask for your pictures, you can deny it if you don’t want, meyasa zaki yi blocking ɗina, bari abun da ki ke ta gudun kar in faɗa, i love you, ina son ki iman, kuma zan bi ta in da na san zan samu abun da nake so kai tsaye, kin san tsarin gidan sarauta ai, so gara ki kwantar da hankalinki ki daina kaucewa” hawaye ne ya cika mata ido, amma ta yi ta ƙoƙarin kar su zubo. Ya gama surutansa ya tashi ya tafi.

Kamar zata kifa haka take sauri, yau ko bari ba ta yi daren yayi ba, saboda yadda maganar ke mimtsininta ji take idan ba ta je ta kai rahoton ba, wani zai rigata.
Sashin Mummy ta isa, ta nemi iso aka yi mata, mummy na ganin yadda baba uwani ta shigo jiki na rawa ta san akwai magana, dan haka ta sallami barorinta, ya rage daga ita sai baba uwani. Ta dubeta ta ce  “Meyasa ki ka shigo mini a yanzu? Sai kin saka an fara zargin mu, ina fatan dai abun da ki ka zo mini da shi, mai muhimmanci ne ba shirme ba?”

“Allah ya baki yawan rai, wani ƙwai ne yake gangarowa daga kan dutse, kuma da alama idan ya fashe zai yi warin da zai addabi kowa”.

Mummy ta yi ajiyar zuciya ta ce “Bani labari”.

“Alamu sun nuna akwai wani abu da giwa take ɓoyewa ita da ɗan ta, dan tun jiya sun kasa sukuni, sun gaza zaune sun gaza tsaye, dan ita yau ta hana kowa ya je in da take har ‘ya’yanta, shi ma kuma tun da ya fita shi da wani abokinsa bai kuma dawo ba, suna ta ƙumbiya-ƙumbiya, amma ina nan zan sanya ido, da na ji ƙyas zan kawo miki rahoto”

Mummy ta ɗan yi shiru sannan ta ce “Ta kaɗaice ta hana kowa zuwa in da take, ciki har da ‘ya’yanta, lallai abun da yake cikin ƙwan nan, ba ƙarami bane ba, ki cigaba da sanya ido, ƙwan ya fashe a kan idonki, kuma da zarar ya fashe ina son ki riga kowa sani, ya kuma nice wadda za ta fara jin ko menene, ina nan ina jiranki, haka zalika nima zan sanya ido a nawa ɓangaren”

“Allah ya baki masara, in Allah ya yarda za ayi duk abun da ki ka ce, na barki lafiya” Mummy ta ɗaga mata hannu alamar zata iya tafiya.

Baba uwani ta tashi tana murnar yadda ta sanya farantawa uwar ɗakinta ta ɓoye.

Unguwar su ruma ta ɗauka cewar ta dawo, magana har islamiyyar su, gaba ɗaya unguwa ta ɗauka, aka din ga yi musu addu’a da tayasu murna.
Huzaifa ne yayi hankalin cewa a kira katsina a waya a sanar musu da anga rumaisa, dan gaba ɗaya ma sun manta da batun su.
Sai da mai sunan Baba ya kai mama ta ga nata likitan, sannan suka tafi Asibitin da rumaisa take.
Gaba ɗaya rumaisa ta kasa daina kuka, saboda farincikin ganin ‘yan uwanta gaba ɗaya a tare da ita, da ta motsa a tambayeta me take buƙata.

‘yan uwa da abokan arziki kuwa da maƙwabta tuni suka fara sintiri a asibitin, domin duba ruma, kowa yazo da ɗan abun alkhairinsa da zai bawa rumaisa.

‘yan uwansu na kano kuwa suma tuni suka cika asibitin, wannan su zo wannan su tafi, sai ga hauwwaliya ma sun zo da sandarta ta dogarawa, kasancewar tun karayar da ta yi kan a sace rumaisa ba ta warke ba. Suka rungume juna.

Ruma ta ce “Hauwwaliya gurguwa ki ka zama ne? Na ganki da sanduna”

Hauwwaliya ta ce “Ke ba gurguwa na zama ba, kin manta na karye ne?”

Ruma ta ce “Au haka ne fa, ban zo na ganki ba ma fa aka saceni”.

“Allah sarki rumaisa, kin ga idi, zaman hannun ‘yan bindiga an ce wahala ake sha fa”
Ruma ta yamutsa fuska ta ce”daina tuna mini dan Allah, wuya ko da magani babu daɗi”

Likita ne yayi sallama shi da nurse, mama ta yi musu sannu da zuwa, mai asibitin ne da kansa ya kalli ruma ya ce “Sai ka ce mun kwantar da shugaban ƙasa, ‘yan dubiya daga wannan sai wancan, kamar ba wani mara lafiya sai ke” ruma tayi murmushi tana kallon trolleyn da suka shigo da ita, tana fatan ba za ayi mata allura ba.

Yayi murmushi ya ce “To yaya jikin naki?”

“Da sauƙi, amma haƙarƙarina fa yana mini ciwo haryanzu”

Ya ce “Mu ga wurin, ya aka yi haƙarƙarin yake yi miki ciwo?”

“Sule ne ya takani a wurin, wani jibgege, nauyin ƙafarsa kamar tsauni”. Yayi murmushi yana ƙoƙarin miƙa hannunsa ya ɗaga rigarta ya duba, amma ta riƙe rigar ta tsareshi da ido.

“Dubawa zan yi na gani”

Aliyu ne ya taso, ya kama rigar tata zai ɗaga “Yaya Aliyu ni kar ka buɗe mini jiki a ganni”

Aliyu ya ce “Ke dallacan, ina tsintoki a ka yi kanki ko ɗan kwali babu, wa zaki yi wa iyayi? Ko shi wanda ya taka kin kin yi masa iyayin?”

Tana zumɓura baki ya ɗaga rigar, likitan ya danna haƙarƙarin, ta saki wani marayan kuka.

Ya ce “Is ok, zan rubuta muku hoto in sha Allah, ayi mini hoton wurin, da kuma kanki”.

“Wurin mai hoto za a kai ni? Ayi mini a waya mana, bana son motsawa ko ina ns jikina ciwo yake”

Ya girgiza mata kai ya ce “X-ray nake nufi, ba hoton passion ba, sauko yau ki taka ƙafar nan na gani” ta girgiza masa kai ta ce “Tana yi mini ciwo fa”

“Sai fa kin taka yau saukko, da yayi ki ka yi gudu ki ka fito daga daji?”.

Shiru ta yi sannan ta ce “Ikon Allah ne ya fito da ni” ta fara ƙoƙarin saukowa a hankali ta tsaya a kan ƙafarta. Likitan ya ce “Good, taka a hankali mu gani”. Tana ƙoƙarin ɗaga ƙafar, amma ji take kamar ba a jikinta take ba, dan haka ta kasa.

Likitan ya ce “Riƙe hannuna, ki ɗaga ƙafar a hankali, bana son ganinki a kwance kullum”

Noƙe kafaɗa tayi, ita ba zata riƙe hannunsa ba.

Ya saka hannu ya riƙo na ta hannun, ya ɗan ja ta sai da ta ɗaga ƙafar sai da ta yi ƙara saboda ciwon da ƙafar take yi.

Usman ne ya taso, ya cire hannun ruma da ga na likitan ya ce “Zamu zagaya da ita in sha Allah, in dai ƙafar ce zata din ga takata” murmushi yayi ya girgiza kai, ƙiri-ƙiri ba sa iya ɓoye kishinsu a kan ƙanwarsu, zai duba mata rauni, Aliyu ya taso ya buɗe masa da kansa, yanzu kuma Usman ya zare hannun ruma daga nasa.

Ya rubuta musu duk abun da yake so a kawo masa, ya fita daga ɗakin.

Hauwwaliya ta dogaro sandarta, Usman kuma yana riƙe da rumaisa suka fita zagaya asibiti.

A hankali rumaisa tana takawa, har suka je ɗakin da jaririnta ke kwance, nurses na kula da shi, sune suke yi masa komai. Ruma ta daɗe a wurinsa, sanann suka fito, a wurin komawa ɗakimta kuma ƙafa taƙi takuwa, ƙarshe sai Goyata Usman yayi ya mayar da ita ɗaki.

Ammi ba ta fito ba sai la’asar, shi ma da ta fito tea kawai ta saka a kai mata, shi kawai ta iya sha, kai da ka ganta ka san a tashin hankali take.
Wayar Adam take ta kira amma ba ta shiga.

Ta fito falo ta tambayi barorinta ko Adam ya shigo? Suka ce mata tun safe da ta raka shi ya fita, bai kuma dawowa ba.
Ammi ba ta samu wayar Adam ba sai magariba.

“Ina ka ajiye wayarka nake ta kira amma ba ta shiga?”.

“Ammi na kashe wayar ne, saboda bana son a dameni da kiran waya”.

“Wannan ba hujja bace, ka san dole zan neme ka ai, ya ake ciki akwai wani abu ne, ko yarinyar ta yi magana a kan Aisha?”

Kamar yana gaban Ammi, ya girgiza kai ya ce ‘Ta ƙi magana, ta ce bata san komai ba”.

Cikin rashin fahimta Ammi ta ce “Kamar yaya?”

“Haka dai ta ce”

Ammi ta yi ajiyar zuciya ta ce “Ka zo ka sameni, asibitin zamu tafi yanzu “.

Ya sauke numfashi ya ce “To gani nan” ya ajiye wayar yana jin yadda kan sa ke sara masa, saboda damuwa da tunani.

Sai kusan ƙarfe tara na dare sannan Takawa ya zo tafiya da ammi, sai a lokacin su Iman suka samu damar ganin ammi.

Cikin damuwa Iman ta ce “Ammi ina zaki?, yau gaba ɗaya bamu ganki ba”

Cikin ƙarfin hali Ammi ta ce “Ku yi haƙuri, wata unguwa zamu je, yanzun nan zamu dawo ba daɗewa zamu yi ba” daga haka ta yi gaba ta bi bayan takawa suka fice.

Iman ta ce “Yaya Nusaiba, akwai matsala fa, Ammi suna ɓoye mana wani abu ba sa son mu sani”.

Nusaiba ta ce “Nima na gani, amma bari mu jira mu gani”.

Ita iman abubuwan sun yi mata yawa, ga maganganun wambai, ga zancen da yake yawo a kan su da takawa, ga abun da take gudu Jabir ya furta wai yana son ta.

Kamar kurame haka su Ammi suka ƙarasa Asibitin da rumaisa take.

‘Yan dubiya duk sun watse, sai Mama da Abdallah mai sunan baba suna ta shirin tafiya gida, Mama ta wanke jaririn nan tas, an haɗa madara an bashi, ya gama sha ruma tana rungume da shi, tana kallonsa tana tuna irin yadda suka sha gwagwarmaya kan su kuɓuta.

A hanyar barin asibitin, mai sunan Baba suka haɗu da Adam da Ammi, ɗan kallon kallo suka yi da shi da takawa, amma babu wanda ya kula wani, suka wuce.

Sallamar su Ammi ce ta dawo da rumaisa daga tunanin da take yi, ta ɗaga kai ta kallesu ba tare da ta amsa sallamar ba, Abdallah da mama suka amsa suna yi musu barka da zuwa.

Ruma ta ɗan ƙare musu kallo, fuskar takawa kamar ta mai amai da gudawa, duk yayi wani iri, mama ta basu wurin zama, suka gaggaisa ammi ta dubi ruma ta ce “Maman baby ba magana?”

“Ina wuni” Ammi ta ce “Lafiya lau, ya jiki ya baby kuma?”

“Lafiya lau”.

Ammi ta ce “To Alhamdilillah”

Mama ta ce “Jiki da sauƙi kam, domin yau har ta tattaka, gobe in Allah ya kaimu zamu je mu kaita hoton ƙafar da kai, da kuma haƙarƙari da take kuka da shi”.

Ammi ta ce “Allah sarki, karki damu, zan aiko s kaita”.

Mama ta ce “A’a kar ɗawainiyar ta yi yawa, zamu kaita in sha Allah”

Ammi ta ce “Ɗawainiya ta wuce tserato wa da ta yi da wannan jaririn, ai duk abun da muka yi mata bamu faɗi ba”.

Mama ta ce “Rumaisa kawo jaririn su ganshi mana”.

“Amma mama kar ki bashi ɗana”

Mama ta ce “Shi wa?”

“Wancan mutumin” tayi maganar ba tare da ta kalli Adam ba.

Guntun tsaki mama ta yi, ta karɓi jaririn, ta miƙawa Ammi shi, Ammi ta karɓe shi tana murmushi tana ƙare wa yaron kallo, kamannin adam ne sak yaron ya kwaso.

Ta dubi ruma ta ce “To maman baby, ba a saka masa suna ba haryanzu?”.

Ruma ta ce “Na saka masa suna, sunansa Mahmud!” A tare Ammi da Adam, suka ɗago suka kalli rumaisa, ita kuwa ta basar dan ba ta san me ta yi ba.

Paid book ne ₦500, via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank
Ayshercool.
08081012243

 

 

 

 

https://chat.whatsapp.com/G9XU8tDJMjq02zlZMHurZ5*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI’IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA’A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA’IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA’IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni’ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau’in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

 

 

Back to top button