Hausa NovelsHausa NovelsNamijin Zuma Hausa Novel

Namijin Zuma 48

Sponsored Links

48…

Har zasu nufa babban private hospital din aeezaad yace su nufa asibitin da nabeelah ke Awo , Sbda yanaso a duba masa babynsa sosai Da uwar babyn, Kuma ya yadda da Aikin doctor maryam. ba nisa da inda suke da asibitin,ba bata lokaci suka isa asibitin,. Doctor maryam ce ta dubata da ace aeezad ba security bane, da Sam bazata dubata ba ganin uban tabon bulalar dake jikinta, a fari doctor tambayar Aeezad tayi tace ”Hatsari kukayi ne?” aeezad yace “aah doctor shaidar bulala ce…”doctor ta Kuma duba nabeelah da kyau taga bulalarce da gaske, har kwallah seda doctor tayi, doctor Maryam nada imani, Sam imaninta be fita ba akasin wasu doctor’s da babu d’igon imani a zuciyarsu. Ba bata lokaci Doctor Maryam ta bawa nabeelah DUk Wani taimako da take bukata, ta duba babyn dake cikinta Nan take aka mata scanning, a nan taga akwai problem tabbas da ace cikin ya Kai 9months da yau yau za a mata CS a ciresa,. Doctors ta kira Aeezad office bayan an bawa nabeelah daki an mata komi da komi ansa mata drip Sbda galabaitar da tayi, sannan tayi 3days ba abincin kirki a cikinta. doctor tana Kiran aeezad jiki na rawa ya iso office dinta big hajiya ta biyosa, a baya, Zaks baya Nan ya tafi gida ya dawo ynzu, wata nurse aka bari a dakin domin kula da nabeelah. a zahiri da bad’ini kaunar da big Hajiya take ma Cikin jikin nabeelah bana wasa bane,. Doctor ta fara bayani Cikin nutsuwa idonta na kan Aeezad “A gaskiya nabeelah Ahamad, ta wahala sosai, sanadiyar Hakan yasa cikinta ke Cikin tsananin galabaita….” Kafin Doctor ta karasa big hajiyar dake tsaye ko zama batai ba ta amshe da “na shiga uku ni y’asu! Wallahi in aka kashe Cikin jikin yarinyar nan, dukse naci kaciyar bura uban rafi’ah da yarta,shaggu Yayan mage, yan babbar bura bura, matsiyata,” Doctor maryam ta tsurawa big hajiya Ido, tace “Wasu be suka mata wannan dukan mama? Ni ai nasha barayi ne suka shigo muku sukayi wannan aika-Aikan….” Aeezad de ya dafe goshi ubangiji ne kawai Yasan irin bakin Cikin da yake ciki da Kuma tsanar hajiya mommy da na’eema dake kara ratsashi, ji yake a bakar zuciya irin tasa yana iya kashesu in har ya hadu dasu Yana kan dokin zuciya. Big hajiya ta amshe doctor Maryam dacewa “wad’annan sunfi barayi likita, kasurguman shaggu ne yayan tsiya jima’in rana tsaka, haihuwar tsakiyar kasuwa…” Doctor ta girgiza Kai Cikin tausayawa tace “Innalillahi wa’inna ilaihirraju’un!” Aeezad yace “Doctor amma ita ba Wani Abu Daya tabu a jikinta kou? Ta fannin lafiyarta?” Doctor tace “Aah Alhamdulillahi de za ace karka damu, Amma ai galabaitar da tayi ne ya shafi babyn, kasan me juna biyu ko zazzabi tayi se babyn cikinta yayi zazzabi, insha Allahu Amma ba Wani abu, sede shadin bulalarce dake jikinta, shima likitan fata zataxo gobe zata bata cream din daza a dinga shafa mata bulalar bazatai tabo ba ko kadan inta warke…” Aeezad ya sauke ajiyar zuciya a ransa shi ko a yaya mommy take Yana santa, shi daxa a bar masa ita a haka ma zeci gaba da santa har gabanin abadan, ya kara santa ma kan San da yake mata, shifa koda turata akeyi a baro Yana santa haka, ba abinda zesa santa a ransa yayi rauni, ajiyar zuciya ya sauke kana yace . “Yanzu yaza ayi da Cikin jikinta doctor? ki temakamin pls a kulamin da Cikin jikinta, Dan girman Allah kar a bari Wani Abu ya samarmin babyna dake cikinta pls,da itama Dan Allah ki temakrni doctor…. in abun bazeyu ba a gayamin in fita da ita waje pls inasan matata da babyna na cikinta banaso na rasa kowa Dan Allah…..” Aeezad ya fadi Kmr ze kuka. Cikin muryar kwantar da hankali Doctors tace “Karka damu ranka ya dade, insha Allahu ba abinda ze gagara, da ace de cikin nata karami ne da dole ya zube, insha Allah Wannan ya riga ya girma ba abinda ze sameta, NASA mata drip da Allurorin ze taimaka mata sosai insha Allah, ,sede zaku zauna a asibitinnan har Nan da 2weeks kawai se a mata CS zuwa lokacin cikinta yashiga month dinsa na haihuwa insha Allahu, Amma sede za a dinga bata kulawa sosai,Muma zamu bata insha Allahu sir se kun dauki babynku cikin koshin lafiya…” Aeezad ya amshe da “Allah amin ….” A zuciyarsa yasan ranar daya dauki gudan jininsa Kuma nabeelah ce ta haifa masa ba karamin farin cikin zeyi ba, sannan shida kansa besan Wani irin SO zeyima babyn daya fito daga Cikin wadda yafi so ba a kaf rayuwarsa. Big hajiya se washe Baki takeyi. Sukema doctor godiya suka fice a office din zuwa dakin da Aka kwantar da nabeelah. Har yanzu bacci Takeyi, Aeezad ya karasa ya zauna kujerar dake kusa da gadonta ya kamo hannunta ya rike Wanda yake daure da drip din, hajiya mommy ta zauna gefen gadon, nurse din dasuka bari a dakin ta fice a dakin. Sam aeezad bayajin Taba nabeelah a gaban kowa, shi Sam in Yana ganinta ma hankalinsa ke gushewa.
Ba ita ta farka ba se cikin dare, Daman tini Aeezad yasa Zaks ya siyo mata DUk abubuwan dazata bukata dama wanda bazasu mata amfani ba. Se lallabata Aeezad keyi Yana bata hakuri kan abinda su hajiya mommy suka mata,big hajiya ma tasako Baki a bata hakurin,zaks ma dake zaune gefe yasa Baki Shima a Bata hakurin cikin sanyin murya nabeelah tace “bakomai, ai baku kukamin ba,suma dasukamin na yafe musu…” Kowa tsayawa yayi kallonta, ba Kmr ma Aeezad, Nan take yaji ya kara santa Sosai, sbda sanyin hali irin nata da hakuri da juriya. Tashi Aeezad yayi kawai ya rungumeta yayi kissing dinta, zuciyarsa na kara narkewa a santa. “Ahhh wlhi karki yafe musu, wad’annan shaggu basu chanchanci yafiya ba…” Cewar big hajiya. Aeezad Daya saketa daga rungumar da yayi mata ya koma ya zauna still hannunsa na rike da nata, Allah ne kawai Yasan irin santa Daya karu a zuciyarsa.nabeelah tayi kasa da kanta. Da kansa ya Bata DUk abinda takeso taci a baki, har ta gama ya temaka mata taje toilet ta kama ruwa ta dauro Alwala, tayi sallolin dake kanta a zaune, ta idar ta koma ta kwanta tanajin knta Kmr ze buga har yanzu muryarta bata fita Sosai a gaskiya tasha whla a gurin su hajiya mommy, ko ina a jikinta ciwo yakeyi karfin hali ne kawai, tana kwanciyar bacci ya dauketa, doctor tashiga ta mayar mata da drip. Washe gari Aeezad nayin sallah Asubahi,zuciya ta tsumosa sbda kwana sukayi nabeelah na wassshhh wassshhh ciwon kai, ciwon baya, ciwon mara, ciwon ciki, ciwon kafa, seda doctor tazo ta mata Allurori da kyar tasamu tasamu bacci ganin asubahinnan ko tashinta Aeezad beyi ba tayi sallah, domin ynzu tayi baccin Kuma Allurar bacci aka mata, har fuskarta ta Kuma kumbura Sosai a yau din jiki ya kuma tsami tako ina ciwo yake ma nabeelah. Ba tare da Aeezad ya gayama kowa ba yaja motar zuwa inda yasa a Kai hajiya mommy da Naeema da tawagarsa. Kafin ya Isa ya tsaya ya siya ruwa me azabar Sanyi sbda tunawa da yayi da a sume Naeema take. Yana Isa ya bude dakin duhun dasuke, duk suna rarrabe, sauraye sun hanasu bacci Dan haka ba Wanda ya rantsa cikinsu Wasu Kam harsu kamu da zazzabi abinda da ba a saba ba, hajiya mommy Kam gabaki daya hakoran bakinta ke mata ciwo ga fuska tayi himmmmm tayi ukun ada fuskar tata, ta kame yarta ta rungume wadda take a sume har yanzu, Naeema hajiya mommy tayi kuka-tayi kuka harta gode Allah, a tunaninta mijinta baze bari ta kwana a gun azabar Nan ba, ga uban kishi tanaji, Amma Sam seta fahinci ma mijin nata da wuya in Yayi yunkurin ganinta,itace bata Sani ba Amma ya kikkira Aeezad yafi Sau talatin, Sam ma wayoyin Aeezad basa tare dashi suna cikin motar Kuma duk suna silent,ya kira Zaks ma Shima motarsa tana cikin mota Tinda abun ya faru har yanzu be dauki wayarsa ba,se dayarce ahannunsa Kuma Alhaji sunusi beda number din wayar dake hannun Zaks din yanzu. Ba wadda Aeezad ya kallah iya iyaka, ya watsawa Naeema ruwan sanyi ta farka a gigice tana ihu da sambatu tana fadin “Da gaske ne mijina yayi aure? Wallahi karya ne Aeezad bazemin kishiya ba!..” sune kalaman dake fita daga bakinta knr sabon kamun hauka. Sam aeezad ko tausanta beyi ba,yasa aka dakko masa bulalar dasuke dukan barayi dashi, tayi ashirin din bulalar belt din dasuka daki nabeelah dashi. Da zuciya da Rai da jinin jiki Aeezad yashiga zubawa na’eema bulalar Kmr yasamu babban barawon Daya sace masa kaf dukiyarsa Daya wahala Yana nema. Na’eema ta hau ihu kmr ranta se fita, ta rasa Ina zatasa rayuwarta sbda azaba. Kaf jamaah dake dakin jiki yayi sanyi, sunsan ana gamawa da na’eema se su tini Wasu suka fara kuka a dakin Tin kafin Azo kansu . hajiyan mommy tasaka ihu, tana fadin “Wani irin cin mutumci ne Wannan kake min? Karka kara dakarmin y’a! Zansa ubanka ya tsine maka! ” sune kalaman dake fita a bakin hajiya mommy San Aeezad ma besan tanayi ba, ga Naeema se ihu takeyi tana Sosa ko Ina a jikinta gata Yar tuburbura ko Ina namomi a jikinta, Aiko tana amsar azabar bulalar sosai, Se Kiran sunan mommynta takeyi hnklinta tashi sbda azabar zafin dake ratsata, ta bawa Aeezad hkri Amma Sam bejinta, se basa hkri takeyi Amma Shiru be saurara mata ba tamkar tana zugasa,. Hajiya mommy ta rugo zata janye yarta aeezad ya hada da ita a dukan, gashi Naeema ta riko uwar tata gam ba halin ta matsa.haka Aeezad ya hadasu ya musu dukan bura uba, hajiya mommy se ihu takeyi, ga yarta na tana ihu, duk se ihun neman agaji sukeyi, seda Aeezad ya tabbatar ya fasa musu ko Ina a jikinsu, kana ya barsu,harsun sume,kana ya dakata ya yayyafa musu ruwa suka farfad’o kana yaci gaba da dukansu seda sukayi Suma uku uku suna farfad’owa kana ya kyalesu, Sam shi beso dukan hajiya mommy ba ita ce ta shigo ya hada da ita Amma beso ya mata komi ba, sbda tana matsayin uwarsa ne sbda matar ubansa ce. Bayan ya musu dukan karshe ya yayyafa musu ruwa sun farfad’o,se Nishi whla sukeyi gabaki daya suffofinsu seda ya chanza, duk ya chanza musu halittu ba kmr ma a fuska, yafi dukan hajiya mommy sbda itace a Saman na’eema, tini ma hakoranta na gaba sama da kasa sun zube guda goma kasa biyar sama biyar, dman Tinda turame suka zube a Bakin nata kaf hakoran nata suke rawa. ya juya ze fita daga dakin duhun dayasa aka kunna haske sbda shigowar da yayi, ya juyo yace “Na sakeki na’eema saki daya, inkin samu miji Kiyi Aure…!!!” Yana gama fadar hakan ya fice daga dakin,Nan take na’eema ta Kuma sumewa, uwarta Kuma ta Saka ihu tana fadin “Wallahi baka Isa ba,wlhi na’eema Bata saki ba, aurenku da ita har abadan mutuwace zata rabaku, wlhi ban aminta da Wannan dakinba,,ohhh rafi’ah, Wannan Wacce iriyar matsifa ta tunkaroni? Magauta sunmin Asiri Innalillahi!! Nashiga ukuuuuu!!” Ta Saka ihu k
Kmr wadda ta kwato daga gidan mahaukata, ta kama ihu tana tima a kasa ga yarta a sume, Wannan rana Sam Hajiya mommy bataji dadin zuwanta ba, ko a mafarki batayi tsammanin zata riski Wannan baqar ranar ba.

Aeezad ya shaidawa sojojin dake tsaronsu cewar a Basu abincin a Basu ruwa,sannan a fiddosu in time din Sallah yayi, Amma suyima sauran matan dake dakin Banda hajiya mommy da na’eema, ko Wacce a mata bulala dari-dari…” Cikin hanzari suka ansa da angama sir. Ya juya ya fice yaja motarsa ya koma asibitin da mommy take. Sojojin Kam tini suka aiwatar da umarni seda sukama kaf matan dake dakin duka dari-dari, da bulalar da Aeezad ya daki hajiya mommy da na’eema da ita. Mata sunsha ihu sunyi kuka kmr rayukansu zasu fita, sunyi dasun sanin zuwa bikin yafi a kirga, da aka gama dukansu, duk suka Hadu suka dawo kan hajiya mommy suka hau kanta da bugu, naushi suke kai mata tako Ina, seda suka kara zubar mata da sauran kaf hakoran datake bakinta kana suka barta, azaba iya azaba fa hajiya mommy tashiga, har seda tazama Abar tausai ga yarta kwance ga Aeezad ya sakar mata diyya bala’i goma a eda suka mata dukan da ashidin,tabbas daza a duba jinin hajiya mommy a yanzu da tabbas se an sameta da hawan jini na karshe ma , zuciyarta Kam gaf take da bugawa, Nan kasan simintin dake dakin duhun take kwance tana kuka tana ihu gashi Sam muryarta bata fita, yaude aeezad ya nunawa kowa iyakarta gashi Wadda ta isa da wadda bata isa ba duk sun hasu sun Kuma mara duka bakinta jini kawai yake fitarwa.

Seda ya tsaya ya mata shopping abubuwa na ciye ciye,Dana tande-tande kana ya nufa asibitin wuraren karfe Sha biyu,. Yana Isa ya tadda ta tashi tin 11, doctor tazo ta dubata, se kulawa kawai hajiya mommy ke bata ga Zaks saune shima Yana d’an musu Hira, Daman Aeezad yasan zata samu duk kulawa da take bukata a gun big hajiya, har wanka ta mata ta chanza mata kaya cikin kayan da Aeezad Yasa Zaks ya siyo mata jiya, doguwar rigace ta hutawa mara nauyi jikinta se kanta sanye da hula, fuskarnan tata ta kumbura, inya kalleta ya tuna su hajiya mommy ne suka mata seyaji ya kuma tsanarsu shifa har yanzu be huce takaicin abinda suka masa ba, already an riga an cucesa kome ze musu bazeji Sanyi ba,dukda ko ynzu ya barsu ya musu dukan dayafi wanda sukama nabeelah. Karasowa yayi ya zauna, kujerar dake kusa da gadon tana zaune ta jingina bayanta Da pillow din da Big hajiya tasa mata a bayan nata, se uban ciki Daya turo gaba gaba, taji dadin jikinta sbda wankan Da big Hajiya ta mata, dukda de taji zafin wankan a fari sbda jikinta dake a farfashe, ba sosoma aka mata wankan.”My love one, ya jikin?” cewarAeezad da yayi mgnr yayinda jikinsa ke rawa a kan nabeelah.”Da sauki..” ta basa amsa,yayi murmushin yace “Meyasa kikayi wanka Baki bari nazo na Miki ba…” Ta basa amsa da “big Hajiya ce tamin…”yayi murmushin kasa-kasa yace “Ta gama ganinmin gindin da nakesa burana inyi gwatso, Kuma ta gama ganemin nonuwanki da nakesha kou?” girgiza Kai kawai nabeelah tayi tace “har yanzu baka shiryu ba?…” Aeezad yace “Da wuya na shiryu..ta Yaya zan shiryu? Bayan kin bani gindi naci Naji dadih…” Kasa kasa yayi mgnr ta yadda ita kadai zataji. Kauda maganar nabeelah tayi kasa-kasa,yayinda kanta ma yake kasa tace kanta “Inaso Ka maidani gun ummih gaskiya, kawai semu mata bayani a kan cikinnan dake jikina,nasan ummih zata amince, inma Bata amince se mu dauki Alqur”Ani mu mata rantsuwa,muce aure mukayi kafin aka samesa, karka ce aah, sannan in aka ciremin babynka, se in baka yarka ko d’anka, kawai seka sawwakemin Aurennan naka dake kaina Dan Allah wlhi bazan iya ba,, wata rana se a dauki raina a kanka! Dan Allah Ka sawwakemin kawai, Ka maidani kasata na har abadan, bazan dawo kasarnan ba wlhi, zaman Aure mutum biyu Akeyinsa, nide bazan iya ba kayi hkri Dan Allah Ka sawwakemin kawai na huta da fargabar dake tunkaroni yanzu!….” Ta karashe cikin magiya da roko kawai so takeyi ta bude Ido ta ganta a dakin uwarta, Kuma taga babu auren Aeezad a kanta shine burinta. Tinda Taga irin dukan da Naeema da hajiya mommy suka mata ama basusan cewar cikin jikinta na Aeezad bane, Ina maga yanzu dasuka Sani tasan next time kawai kasheta zasuyi har lahira, so maganin Ayi kar a fara,dukda tasa sansa Amma ta shirya kawai kwara ta rabu da Aeeezad shine kwanciyar hankalinta.

 

Ko kadan ba editing se hkri.

 

This book is 1k 08101626484.

[7/31, 3:05 PM] Maman Aslam: NAMIJIN ZUMA

Back to top button