Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 45

Sponsored Links

 

Wani irin tausayinsa ne ya kama Aliyu, duk yadda adam ya so ɓoye hawayensa kasawa yayi, ya barsu suka din ga zuba son ransu.

Da ƙyar Aliyu ya ɗan yi gyaran murya ya ce “Kamar yadda ka ce kai musulmi ne ka yarda da ƙaddara, to Yakamata a ga hakan a aikace, ka yi haƙuri in sha Allah sirikinka zai fuskance ka, Allah ya yi mata rahama”.

Mama ce ta yi sallama a ɗakin tana faɗin “Aliyu ya tashi kuwa?”.

Ta tarar da su a zaune, mama ta ce “Alhamdilillah ala kulli halin, Allah mun gode maka, sannu ka ji?” Ya jinjina wa mama kai yana share hawaye.

“Ayi haƙuri, a fawallawa Allah, yaronka mahaifiyarka da sauran makusantanka suna buƙatar ka, ita tata ta ƙare ta yi shahada sai fatan Allah ya karɓi shahadarta, ayi haƙuri, Aliyu je ka ɗaki ka kawo ruwan shayi da abinci ya samu ya saka wani abu a cikin sa”.
Aliyu ya tashi ya fita, yana fita lokitan dare ya shigo, ya dudduba Adam aka bashi maganinsa na dare, likita ya jaddada masa ya kula da magani da dokokin da aka saka masa.
Sam Adam ba ya fahimtar abun da likitan yake faɗa, mama ta miƙa masa kofin shayi cikin kulawa ta ce “Daure ka sha, ka ga an baka magani, dole sai ka ci abinci” kallon mama kawai yake yi, wato duk in da uwa take uwa ce, yadda ta ke ta nuna kulawa a kansa sai ya ji daɗi, duk da tarin damuwar da yake ciki.
Duk da ba zai iya tantance manufar kulawar da mama take bashi ba, amma tun da ya taso kulawa ɗaya ce yake gani ta zahiri, wato kulawar ammi ban da haka galibi masu yi masa murmushi suna yin sa ne da biyu.

Da ƙyar ya karɓi kofin shayin, ya ɗan sha kaɗan ya ajiye, mama ta yi ta masa nasiha, da rarrashi cikin siga ta dattaku da manyance.
Ya ɗan murza zoben hannunsa ya ce “Da ke da iyalinki, babu abun da zan iya ce muku sai godiya, a rayuwata na daɗe ban ga mutane masu karamcinku ba. Amma dan Allah ku yi haƙuri da abun da zan faɗa, ina son zan karɓi yarona, dan Allah a rarrashi mamansa, na san zata tsaneni fiye da da, amma ni ba zan iya da rigimarta ba, a bata haƙuri zan ɗau yaron nan zan tafi da shi wurin kakansa, sai hukuncin da ya yanke a kanmu”.

A take mama ta ji babu daɗi, domin ita kanta ta shaƙu da jaririn ba kaɗan ba, ya shiga ranta.

A zahiri ta ce “Babu laifi, Ubangiji Allah ya raya shi bisa tafarkin addinin musulunci, ya jiƙan mahaifiyarsa. Amma ina fatan ba zaka rabamu da shi gaba ɗaya ba, dan a halin rumaisa bana jin za ta iya haƙura”.

Yayi murmushi ga hawaye na zuba daga idonsa ya ce “Za ta saba in sha Allah, ba zata damu sosai ba amma yarona yana buƙatar kariya ta musamman, ba zan manta soyayyar da ta nunawa gudan jinina ba”

Jiki a sanyaye mama ta ce “Babu laifi, Allah ya jiƙan mahaifiyarsa, kai kuma ya baka lafiya” da haka mama ta yi musu sallama ta koma ɗakin da rumaisa take. Ta kwanta tana facing ɗin Sabir, tana ta baccinta, ta saka hannu ta riƙe masa nasa hannun suna bacci.

Tausayinsu ne ya kama mama, amma babu yadda ta iya, haka ta shiga harhaɗa wa sabir kayansa, a daren ta haɗa komai cif a wuri ɗaya.
Suma ta haɗa musu nasu kayan, dan ta ji likitan yana cewa washegari zai sallami rumaisa, tun da ita ma ta warware sai abun da ba a rasa ba.

Sai da ta kammala, sannan ta yi alwala ta tayar da salla.

Da asubar fari, sabir ya tashi yana ‘yan koke-koke, mama ta ɗauke shi ta yi masa wanka, ta bashi madararsa, ita kanta mama tana matuƙar ƙaunar yaron da tausayinsa, ta ɗauke shi ta goya shi a bayanta, ta yi sallar asuba, ta tashi ruma ta yi salla sannan ta fita daga ɗakin.
Harabar asibitin ta koma ta kira mai sunan baba, tana shiga ya ɗaga, ya gaida mama, ta amsa masa sannan ta ce “Babana, dan Allah da gari yayi haske ka taho asibitin nan, yau za a sallami rumaisa, kuma yau za su karɓi ɗan su, ka san halinta sarai, jiya da daddare babansa da ya farfaɗo ya ce zai karɓi ɗan sa ya tafi da shi ya gabatar da shi a danginsa, sannan ya sanar da rasuwar uwar ɗan”.

Mai sunan baba ya ɗan yi shiru sannan ya ce b”Babu laifi, zan shigo in sha Allah, amma a bita a hankali dan Allah, ko a bari na zo tukuna”

Mama ta ce “ai shi ya sa na ce sai ka zo ɗin”

Bayan sallar asuba, Adam ya karɓi wayarsa a hannun Aliyu, ya kira ammi, suka yi magana, ta ji daɗi sosai da jin muryarsa, tayi masa addu’a da fatan alkhairi.
Ya kira Bashir ma suka gaisa, tare da sanar da shi, ya je ya taho da Ammi.

Kiran jabir ne yake ta shigowa tun bayan da ya kunna wayar, kamar ya share sai kuma ya ɗaga.

“Wai ina ka shiga haka baka ɗaga wayata? Ya ake ciki ne akwai wani labari ne? Ko ka koma wurin yarinyar?”

“A’a ban koma ba, zan koma bacci yanzu zan zo gida in sameka anjima” bai ko tsaya saurarar mai jabir zai ce ba, ya kashe wayar ya ajiye, haryanzu ya kasa gazgata maganganun rumaisa, wai Aisha ta mutu, ganin abun yake kamar almara, sai yanzu ya gane ka rasa mutum ka ga gawarsa wata ni’ima ce, ba irin tunanin da bai zo masa a kan gawar Aisha ba.

Abun mamaki yau ruma taƙi komawa bacci, mama har tambayar ta ta yi ba zata koma bacci ba, ta ce ba ta ji.

Ta dubi in da mama ta haɗa kayansu ta ce “Mama wai tafiya zamu yi ne an sallame ni?”.

“Eh, in anjima za a sallame mu”

“Yeeee dama na gaji da zaman asibitin nan wallahi, yau sai gida, ga kayana ga na babyna nima na samu mai sunan babana, sai dai Allah ya sa kar yayi halin mai sunan kakanmu” tayi maganar da sigar tsokanar mama, amma mama ba ta tanka mata ba.

Har gari ya waye ruma idonta biyu, ta damu mama a kan ta bata sabir, amma mama ta hanata.

Wajen ƙarfe tara, Usman da mai sunan baba suka zo, ruma tana ta murna zata tafi gida, dan zumuɗi ta ce abincin ma sai ta je gida zata ci.

Usman ya din ga kwasar kayansu yana fitarwa, sai murna take yi yau ba kwanan asibiti, dan takardar sallama kawai suke jira daga likita.

Bashir ne ya shigo ɗakin rumaisa, ya kalleta yayi murmushi ya ce “Yau sai gida uwar rikici”

Ta yi murmushi ta ce “Ɗan uwanmu, na gode sosai Allah ya saka da alkhairi, jin godiyar nake ma ta yi kaɗan a baki, amma zan din ga yi maka Addu’a idan na yi salla”..

Yayi murmushi ya ce “Kai masha Allah, amma na gode ƙwarai da gaske, sister na asiya ma tana gaishe ki, ita ma ba ta da lafiya ne. Amma kin je kin duba baban sabir kuwa?”

Ta ɗan yi turus tana kallon mama, mama ta ce ‘Yanzu zan sakata a gaba mu je ta duba shi, sai mu tafi”.

Bashir ya ce “Yauwwa mama, dama ga ammi can ma ta zo sai ku yi sallama, ai bai kamata ku tafi babu sallama ba”.

“To ai yaya Aliyu ya ce bai mutu ba, har ya tashi”

“Haba rumaisa, idan da kara yakamata ki je ki duba shi, ko dan albarkacin sabir ɗinki”.

Usman ya ce “Sai ka lallaɓata ma, wuce mu je, kuma saura mu je ki yi rashin kan gadon naki, ya saka dogarai su saita miki zama”.

Suka ɗunguma zuwa ɗakin da takawa yake, suka tarar ammi na zaune a kusa da shi, ta riƙe hannunsa, tana share masa hawaye.

Ammi na ganinsu tayi murmushi ta ce “Kun fito? Yau ban ƙaraso mun gaisa ba rumaisa, hankalina ne a tashe”

Ruma ta durƙusa ta gaisheta, ta amsa mata cikin girmamawa.

Usman ya ce “Ki yi masa sannu mana”ta dubi Adam za ta yi masa magana, amma gabanta ya faɗi, ganin gaba ɗaya idonsa ya koma baƙi, yana fitar da hayaƙi.

Mannewa ta yi bayan usman, tana leƙo shi, taga ita yake kallo, amma idonsa yana ta hayaƙi, kallonsu take yi, tana jiran ta ji wani yayi magana a kan idon takawa, amma ta ji babu wanda yayi magana da alama su ba sa gani.

“Ba zaki yi masa sannun ba?”

Ta sunkuyar da kanta ƙasa ta ɗan zuro kai ta ce “Sannu, Allah ya bada lada” tayi maganar a rikice dan a razane take, bata taɓa ganin idon mutum a haka ba.

Bashir ya ce “Ladan me kuma rumaisa, shi da ba shi da lafiya?”.

“Au ba lada ba, Allah ya warkar da shi”

Usman ya ce “Yau kuma meke damunki ne?”

Mama ce ta kwance Sabir daga bayanta, mai sunan baba ya karɓe shi,  ya ƙarasa gaban gadon Adam ya ce “Allah ya ƙara lafiya, ya jiƙan mamansa, kamar yadda ka buƙata ga yaronka, Allah ya raya shi, Allah ya biyaka ɗawainiyar da ka yi da ƙanwarmu”. Adam ya karɓi Sabir, yana ƙoƙarin mayar da hawayen idonsa.

A rikice ruma ta ce “Ban gane ga ɗan sa nan ba, da shi zan tafi ai, ni anty aisha ta bar wa shi” tayi maganar tana nufar Adam, amma mai sunan baba ya tare ta ya ce “Juya mu tafi” karo na farko da ta tsaya ta saka idonta a nasa ta ce “To ka karɓo mini ɗana”.

“Ni nake magana ki ke mayar mini?”.

“Haba mai sunan baba, ya za ayi a ƙwace mini yarona, dama abun da aka shirya kenan? Mama ki saka baki” ta dubi Ammi ta ce “Dan Allah ku bani yarona, na sha wahala kan mu tsira tare, idan aka ƙwace mini shi, mutuwa zan yi, wallahi ina son sa sosai, ɗan uwanmu yaya bashir, dan Allah ka karɓo mini ɗana”
Gaba ɗaya sai tausayin rumaisa ya kama su. Ammi ta ce “Kina ji ruma, ki kwantar da hankalinki, babu mai rabaki da yaronki, zamu je a kai shi cikin dangi ne, kuma in sha Allah za a din ga kawo miki shi ki ganshi”.

Rumaisa ta fashe da kuka ta ce “Da na san haka ne, gara na zauna mu mutu a dajin, da da wannan mutumin ya ce in tafi ba zan tafi ba, gara a harbeni, kwanana biyu ba ma bacci ni da sabir, saboda sanyi yana kuka, kwanana uku ina bulayin hanyar da zamu dawo, kuma a ƙwace mini shi bayan mun sha da ƙyar, ba anty aisha ba sabir ɗina. Dan an ga ni yarinya ce za a ƙwace mini ɗa” Mai saunan baba ya danƙi hannunta zai yi waje da ita, tana kuka tana miƙa hannu tana “Dan Allah ku bani sabir ɗina” tun da ruma ta fara kukan nan tana zuba, ko ɗaga kai Adam bai yi ba ya sunkuyar da kansa ƙasa.

Kuka sosai rumaisa take yi, tamkar an ce mata mama ta mutu, bashir ya rakosu yana ƙoƙarin rarrashinta, amma mai sunan baba ya ce ya rabu da ita, ya buɗe mota ya sakata, amma sai miƙa hannu take taka kuka.

“Ki rufewa mutane baki, idan an baki ɗan ya zaki yi da shi, ke wace irin yarinya ce da ba a isa a gaya miki, ko ki rufe mini baki, ko na casaki a wurin nan” mai sunan baba yayi mata wata irin tsawa mai razanarwa.

A gigice ta ƙanƙame mama tana ƙoƙarin haɗiye kukanta, amma ta kusa ƙwarewa saboda kuka, ga hawaye ga majina har da yawu, saboda kuka.

Ammi na tsaye tana hango rumaisa yadda ake fama da ita, wani irin tausayinta ya kamata. Allah kenan ya karɓi uwar yaron, kuma ya sanya soyayyarsa mai tsanani a wata zuciyar.

A hankali ta juya ta koma ɗakin da adam yake, yana rungume da jaririnsa.

Ammi ya dube shi ta ce “To me ka yanke? A ganina mu bari nan da ko kwanaki biyu ne ka gama warwarewa”.

Adam ya girgiza kai ya ce “Ammi, ba zan taɓa warkewa ba, barin lamarin ina sake jinkirta loka8, abubuwa caɓewa za su cigaba da yi, daga nan gidan turaki zan wuce, zan je na sanar masa da laifina gaba ɗaya duk hukuncin da ya yanke a kaina shikenan”.

Cikin damuwa Ammi ta ce “Kana ganin hakan shine mafita?”.

“Ammi dole ita kaɗai ce mafita, na yi zaton aisha tana raye ne dama, shi ya sanya nake ta jinkirtawa, amma na yadda ta rasu yanzu, yanzu zan fara fuskantar mai girma turaki, daga baya kuma sai na fuskance ƙalubale na gaba”.

Ammi ta ɗan yi shiru yana kallon ƙasa, daga bisani ta yi ajiyar zuciya ta ce “Shin, Ubangiji Allah ya yi mana jagora baki ɗaya ”

Ya amsa da amin.
Bashir suka shigo tare da likita, likitan ya dubi adam da yake rungume da jariri ya ce “Allah sarki rumaisa, gaskiya ta shaƙu da yaron nan, ba ka kyauya ba da ka ƙwace mata ɗa” Adam ya sunkuyar da kai ba tare da ya iya yin magana ba.

“To Yanzu me yake damunka, zan rubuta maka teses na yi reviewing file ɗin ka, na ga vitals ɗin ka duk normal”.

“Sallama nake so” ya faɗa a taƙaice.

“Meyasa zamu sallameka? Dole mu riƙe ka zuwa gobe in Allah ya kaimu mu ga abun da hali zai yi”.

“Ba zaku hana Allah zartar da hukuncin sa ba, ku yi haƙuri tafiya zan yi ” duk yadda likitan nan ya so lallaɓa adam ya ɗa zauna, amma yaƙi ammi ta ce ya basu sallama kawai, suna da issue a gida.

Haka kan likitan ya rubutawa adam sallama, da yayi tunanin ya kira jabir su tafi tare, sai ya ga babu wani amfani ma da jabir ɗin zai yi masa a halin yanzu, dan haka kawai ya share suka tafi.

Suna tafe a mota, yana kalon sabir da yake ta ƙamshin turare, yana wasa da hannunsa, har da farar hoda da kwalli mama ta shafa masa, ba ayi masa aski ba, dan haka suma ta cika masa kai, ga ta a cike baƙa siɗik, har ta ƙasan hularsa ta fito, ga gashin girarsa a hankali yana tofowa.
Ƙasan zuciyar Adam yana ta fargaba da tunanin, yadda zai fuskanci turaki.

Har gidan turaki bashir ya kai su, sai dai shi ya tsaya a mota, su kuma suka shiga.

Da fari ta ƙofar turakar turaki ta harabar gidan, Adam ya shawarci Ammi su shiga, amma sai suka tarar da ita a rufe, dan haka dole suka bi ta cikin gida.

Falon ba kowa sai hadimai, suna ganin Ammi tare da Adam, cikin rawar jiki suka gaishe su, aka tafi nema musu iso wurin matar gidan.

Ba su jima a zaune ba sai ga mama ta fito cikin taƙama, ta dubi Ammi ta yi murmushi ta ce “Giwa, yau ke ce a gidan namu?”

Ammi ta ce “Ni ce, kin san ɗaurowa take a ɗaure alƙali, ya gida ya iyali?”

“Alhamdilillah, takawa magajin takawa, dan kujerar galadima ta yi maka ƙanƙanta babbar kujera muke fata” tayi maganar tana kallon jaririn hannun Adam.

Ta sake cewa “Ina ku ka samo ɗa?”

Adam ya ce “Dan Allah idan babu damuwa, muna neman iso wurin mai girma turaki idan yana nan”

Ta ɗan jinjina kai ta ce “Yana nan, bari ayi masa magana”.

Ƙanwar Samha ce ta fito sumayya, ta gaida Ammi tare da takawa, ammi tambayeta ina samha, ta ce mata ta je abuja.

Mama ta fito ta ce “Bisimillah, ku shigo”

Ammi ta tashi, tana gaba adam na bin ta a baya, suka shiga falon turaki.

Yana zaune a falonsa, gefensa ga Alqur’ani a ajiye, da alama karatu ya idar.

Ya kallesu yayi murmushi ya ce “Maraba da manyan baƙi”.

Ammi ta risuna ta ce “Barkanmu da wannan lokaci”

“Barka dai, ya iyali ya kuma rayuwa”

Ammi ta amsa da Alhamdilillah, maimakon mama ta fita ta bar ɗakin, sai ta nemi wuri ta zauna.

Turaki ya kalli Adam ya ce “Takawarka lafiya, ana lafiya?”
Adam ya jinjina kai kawai, amma bai yi magana ba.

Ammi ta gyara zaman ta ta ce “Allah ya baka nasara, wata muhimmiyar magana ce ke tafe da mu, amma kan in ce komai, zan fara da neman afuwa sannan a sassauta mana hukunci”

“Babu laifi, ku muke sauraro”.

Adam ya tashi a hankali, ya tafi gaban turaki ya durƙusa, ya ɗora masa Mahmud a kan cinyarsa”.

Turaki ya rungumi sabir ya ce “Masha Allah, ina na samu ɗa, ɗan kyakykyawa Masha Allah?”.

“Ɗan wurin aisha ne” takawa ya faɗa jiki a sanyaye.

Turaki ya faɗaɗa fara’arsa ya ce “Ikon Allah, uwata yaushe ta haihu?, yaushe rabona da ita?”

“Allah ya baka yawan rai, haƙiƙa ni mai laifi ne, kuma a shirye nake da karɓar hukuncin da duk ka zartar a kaina. Wannan jaririn ɗan wurin aisha ne matata, kamar yadda aka kai ruwa rana da surutu a kan karatu da nace zata tafi. Duk ba wannan ba ma, maganar da nake maka, yanzu haka fulani ba ta duniya, ya rasu” Adam yayi maganar kansa a ƙasa hawaye na gangaro masa.

Ayshercool.

paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, masu buƙatar vip ko special kuma, suna iya garzayawa arewabooks ku searching sunan littafin*

 

 

Back to top button