Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 8

Sponsored Links

P8

Da rige-rige Usman da Abdallah suka shigo ɗakin, suna tambayar meyafaru da ruma take wannan uban ihun.
Kallonta Usman ya yi, ya kalli mama ya ce “Mama meya sameta ne?”

Mama ta ce “Ku tambayeta mana, ba gata nan a zaune ba”

Abdallah ya ce “Ke menene?”

Nuna masa hannunta ta yi, tana sake fashewa da wani uban kukan.

“Wannan ledar ta meye haka a hannunki, kamar wata miskiniya”

Ɓare baki tayi, ta cigaba da kuka iya ƙarfinta.

“Dalla ki rufewa mutane baki, kiyi mana bayanin menene?” Usman ya daka mata tsawa.

“Ba mama ce ba”

“Me maman tayi?”

“Ta yi mini lallen tsofaffi wai tsohuwa ta faɗa kwata ina bacci, wallahi dariya za ayi mini idan aka ganni da shi”.

“Kuma saboda baki da mutunci, ki ke mana wannan uban ihun da Asubar nan, ke dai ba zaki yi hankali ba ko?”

“Wallahi mama ba ta sona, ban san meyasa ta tsaneni ba, wayyo Allah na”

Abdallah ya ce “Allah ya ƙara, a wannan shegen baccin naki, har aka yi miki lallen baki sani ba”.

Mama ta ce “Ki tashi ki kwance lallen nan kiyi salla”.

Ko motsi ruma ba ta yi ba balle ta tashi.

Abdallah ya ce “Wai wane irin lalle ne tsohuwa ta faɗa kwatar ne?”

Cikin kuka ruma ta ce “Irin fa wanda mama take yi a ƙafarta”

Dariya ce ta ƙwacewa Abdallah, ya ce “Haba mama, ya zaki yi mana haka?”

Mama ta ce “Hukunta ta nayi, duk rashin jin da take yi ba ta zaci ina da hanyar hukunta ta ba, na bada kuɗi ayi mata abin arziki na zamani, amma taƙi zama, ai da ni ki ke zancen, kuma ajima da kaina zan kai ki kitso zane huɗu za ayi miki”.

Sosai ruma take kuka, Usman kuwa ficewa yayi ya cigaba da sabgarsa, Abdallah ne ya kaita bakin rariya, ya tayata ya cire ta wanke, aikuwa hannunnan yayi jawur, lalle ya kwanta ɗoɗar hannunta da ƙafarta.

Da gari yayi haske kuwa, Huzaifa ya ga lallen rumaisa, ya zauna ya sakata a gaba ya dinga yi mata dariya, har da kifawa, wai hannunta kamar kuturwa.

Ko Abincin safe ruma ba ta ci ba, sai kuka da goge hawaye, wajen ƙarfe goma na safe, mama ta sakata a gaba zuwa gidan kitso.

Kamar yadda mama ta faɗa, kitson hannu biyu aka yiwa ruma, gashi ta sha azaba a wurin mai kitson, saboda da ta ƙi tsayawa, mama na dukanta, matar kuma ta matse mata kai a tsakanin cinyoyinta, ga kitson azabar zafi tamkar za a zaro ƙwaƙwalwarta saboda yadda matar ke jan gashin.
Ko da aka gama kitson, ruma ta haɗa gumi ga hawaye da majina saboda azabar zafi, mama ta sakata a gaba suka tafi gida.

Ruma da ta kalli hannunta ranta yake ɓaci, saboda hannun ganinsa take kamar ba nata ba.

Har ana gobe salla ruma bata farin ciki, ji take ina ma ace an fasa sallar idi wannan shekarar, saboda wannan yankan ƙauna da mama tayi mata.
Har bata son a aiketa, dan idan ta fita ta ga yara sun sha kitso da ƙunshi, sai ta yi kuka, saboda yadda ta ƙarfi ita aka mayar da ita zamanin mutanen da.
Yanzu haka tana tafe a hanya, zuwa aiken da mama tayi mata, ta gaji da tafiya ga ɓacin rai, ta samu wuri tayi zamanta a kan wata baranda, tana share hawaye.

“‘Kukan me ki ke yi ne haka, ba aiken ki aka yi ba?”

Ta ɗaga kai taga mai maganar, Auwal ne, na makarantar islamiyya da ta yiwa bori rannan.
Shiru tayi masa tana tura baki.

“Meyasa ki ke kuka?”

Miƙewa ta yi tsaye tana faɗin ‘Babu komai”

Ya ɗan girgiza kai ya ce “Ina Yasir?”

Cikin ƙunƙuni ta ce masa bata sani ba, tayi wucewarta.
Mamaki ne ya kama shi, duk in da ta ganshi ko ba zai kulata ba, sai ta yi masa magana, amma yau tayi masa wulaƙanci.

Aiken da bai fi tayi shi a mintuna ashirin ba, sai da ta shafe awa biyu da rabi, ta koma gida Aliyu sai da ya murɗe mata kunne, saboda yadda ta je ta daɗe.

Da safiyar salla kuwa, an kai ruwa rana da hajiya ruma kafin tayi wanka, dan cewa ta yi ba zata je idi ba.
Huzaifa kuwa musamman ya ƙi shiri da wuri, sai ya ga shigar da ruma zata yi yayi mata dariya.

Ta na kuka, mama ta watso mata wannan atamfa da ta zauna ta dinga kushewa.

“Mama dan girman Allah ki barni na saka tsofaffin kayana, wallahi bana son kayan nan”.

“Ni ki ke gayawa ba kya son kayan nan, zaki saka ki wuce ko kuwa?”

Za ta tsaya gardama Aliyu ya yi mata tsawa, ya ce ta ɗau kayan ta saka su wuce sallar idi.

Ga lalle dungulmi, ga kaya ɗinkin mutanen farko, ga kai babu kitso mai kyau, ba yari ba sarƙa  koma kamar ‘yar ƙauye.
Huzaifa kamar ya shiɗe don dariya.

“Yarinya kin yi kyau kamar bafulatanar ƙauye” Yasir ya yi maganar yana dariya.

“Babu ruwanka da ni Yasir, zan maka rashin mutunci wallahi”.

“Na kuma jin bakin ki sai na ɓarara da ke, maza wuce mu tafi” Aliyu yayi Maganar yana nuna mata hanyar fita.

Usman ne ya miƙo mata sabon hijjabi ya ce “Gashi nan ba dan hakinki ba”.
Ajiyar zuciya ta yi, ko ba komai hijjabin zai taimaka mata ta rufe wannan buhun ɗinkin, tun da hijjabin dogo ne.

Karɓa tayi tana yi masa godiya, ta saka suka tafi idi.

********

“Masha Allah, looking take away my beautiful angel” Ammi ta faɗa tana kallon Iman.

Murmushi iman tayi ta ce “Ammina, an yi salla lafiya”

“Alhamdilillah my dear, ina fatan dai an yi mini Addu’a”

Murmushi ta yi ta ce “Ba dole ba Ammina”

Wata matashiyar budurwa da ke zaune a kan kujera, ta ɗago ta ce “Wai mu Ammi baki ganmu bane?”

“Na ganku mana”

“Ai shikenan Ammi, wannan wariyar launin fata tayi yawa, mu shikenan ba za ki dinga kallanmu ba, sai wannan mai kama da bafulatanar dajin” cewar ɗaya yarinyar.

Ammi ta ce “Kun dai ji kunya, da ku ke kishi da ƙanwarku”

Iman tayi musu gwalo ta ce “Iya wuya dai, nice ta gaban goshin Ammina”

‘Ta mayar da ke ciki, ko a saka ki a zanin goyo a baki Nono, ƙarshen ƙauna”

Ammi ta girgiza kai ta ce”Allah ya shirye ku, Iman ki je ki shirya direba zai kai ki gidan zinariyar Galadima, ki kai musu Abincin salla”.
Ɓata fuska Iman tayi ta ce “Ammi”

Kan ta ƙarasa maganar, Ammi ta ɗora yatsanta a kan lips ɗin ta ta ce “Shhhh, bana son musu, tana ta complain ba kya zuwa” Ɗan gyaɗa kai Iman tayi ta ce “Shikenan Ammi, bari na shirya”

*****
“Ke ba zaki ta so ki fara kai tuwon nan ba”
Ruma ta kwaɓe fuska ta ce “Dan Allah mama ki yi haƙuri, ki bawa su huzaifa su kai wallahi idan na fita dariya za ayi mini”

“Ni nake aiken ki, ki ke cewa na aiki wani ruma, ni ko ruma?”

“A’a mama ba haka bane ba, wallahi dariya yara suke yi mini” tayi maganar hawaye na taruwa a idonta”.

“Tashi ki wuce ki je aiken da aka yi miki” Usman ya daka mata tsawa.

Jiki na rawa ta tashi, ta ɗau kwanukan da mama ta zuba tuwo, ta fara kai wa.

A hanya ta haɗu da wasu ‘yan makarantar bokon su, cikin fara’a ɗayar ta ce “Laa ruma, ya ki ke ina kayan sallar ki?”

Ruma ta kalleta ta ce “Ji masifa, to ba ni da su, ba a ɗinka mini ba”

“Daga tambaya sai masifa?”

“Eh, ina ruwanki da ina kayan salla na, tsirara ki ka ganni?” tayi maganar tana saye hannun ta a cikin hijjabi.

“Kutmelesi, ruma meye wannan a ƙafarki?” Gaba ɗaya suka kalli ƙafar ruma, da take sanye da silifas ɗan madina, ga ƙafa tayi maroon da lalle, kasancewar ruma ba  iya ɗaurin zani ta yi ba, zanin ya ɗage har ƙwaurinta, kuma hijjabin bai gama rufe ƙafar ba.

“Kutmelesi, wane irin lalle aka yi miki, lallai mai lallen nan ta cuceki, kut kamar ƙafar tsohuwa”

Dariya yaran suka kwashe da ita suna sake leƙa ƙafarta.
Cikin takaici, ta juya zata tafi, amma wata zaƙaƙurar yarinya, ta biyo ruma tana ɗage mata zani.
Mai jiran ƙiris ya samu a sarari, tuni ruma ta yi watsi da kwanuka, ta fara sana’ar ta ta dambe.
Kasancewar a ƙule take dama, ta rasa in da zata sauke fushinta, dan haka ta zage ta kama yarinyar nan ta dinga jibagarta kamar Allah ya aikota.
Suna cikin damben Allah ya bawa yarinyar sa’ar ketawa ruma hijjabi, hakan ya ƙara tunzura ruman, ta danne yarinyar tana duka.

“Wannan yarinya an yi jarababbiya, duk in da ta tsuguna sai dambe, sai ka ce annoba” cewar wani mai awo a gefe, da bai raba su ba sai zance.

Ɗagowa ta yi cikin masifa ta ce “Wallahi ni ba annoba bace ba”

Ta duƙa ta cigaba da dambenta.  ji tayi an yi sama da ita, ta fara kokowar ƙwacewa tana kai duka.

“Zaki nutsu ko sai na kakkarya ki” yaya Aliyu ne ya tsare ta da ido.

“Dama abin da ta aiko ki kenan?” Ta yi shiru tare da sunkuyar da kai.

“wuce mu tafi, dage uwar faɗa”

Haka ta kwashi kwanukan, da yagaggen hijjabinta a hannu ya tasa ta a gaba, zuwa gida.

Mama na ganin ruma ta shigo tare da Aliyu, a yadda ta shigo kawai mama ta gane halin ta je ta gwada a waje.

“Damben ki ka je ki ka yi kenan ko, mara kintsi?”

Wage baki ruma tayi zata fara yiwa mama bayani, amma mama ta katseta ta ce “Ban tambayeki ba ruma, ki je ji yi tayi, bakin mutane kawai ya ishe ki”

Gefe ta koma ta zauna, tana jin yadda ba ta gamsu da dukan da ta yiwa Hauwwa ba, saboda dariyar da suka yi mata.

Yaya Umar ne ya fito daga ɗakin su, cikin wata dakakkiyar shadda dark blue, ya karya hula sai ƙamshi yake zubawa.
Tsuruu ruma ta yi da ido, tana jiran ya sauke mata masifa, tun da ya ji ance ta yi dambe.

Nufota ya yi, ita kuma ta ƙura masa ido ko ƙiftawa ba ta yi.

Ya kalleta ya ce “Na canza miki ne?”

Ta girgiza kai ta ce “A’a ka yi kyau ne”

Murmushi ya yi, ya miƙa mata leda ya ce “Je ki ka gwada wannan” da sauri ta tashi, ba tare da sanin meye a ciki ba ta karɓa ta shiga ɗaki.

Doguwar riga ce ta shadda kalar kayansa, da mayafi da sabon takalmi da yari da sarƙa.
Ko da ta saka ta fito ba ƙaramin kyau ta yi ba.

“Mama kin ganni, na yi kyau”

Aliyu ya ce “Saboda son kai, shine ku ka yi kaya iri ɗaya babu ko labari”

Cikin tsananin farin ciki ta ce “Yaya Ussy, kalleni dan Allah na yi kyau?”

“Eh to, babu laifi sai ki ka zama kamar budurwa, duk da ƙwaila ce”.

Cikin tsananin farin ciki, ta faɗa jikin yaya Umar tana murna “Yaya na gode sosai, Allah ya saka maka da alkhairi ya sa ka gama da duniya lafiya”

Ganin yadda take murna ya sanya shi yin murmushi na gefen baki ya ce “Allah ya sa ki daina rashin ji”.

“Iyee, lallai mai sunan Baba, ni sai ka haɗani da atamfa kala uku, amma kai da ƙanwarka ka yi muku kaya iri ɗaya, wato an fi son ta a kaina” mama tayi maganar cikin sigar wasa.

Murmushi ya yi, dan ya san halin mama da barkwanci wasu lokutan.

Mama ta shiga ɗaki, ta fito da wata ƙatuwar leda, ta miƙawa ruma ta ce “Gashi nan, ba dan halinki ba, kayayakin da suka yi miki ne, na wannan sallar naƙi nuna miki dan in hora ki”

Rikicewa ruma tayi, dama suna yi mata ɗinke-ɗinke, amma sallar bana bata san sun yi mata ba, dan a ƙalla ta tashi da kaya ku san dozen, banda hijjabai da abun hannu da sauransu.

“Wayyo Allahna, dama kuna so na haka? Duk nawa ne wannan mama kin ga fa duk nawa ne”

Gaba daya suka kewaye ta suna murmushi, ganin yadda ta rikice tana murna.

Bin su ta dinga yi ɗaya bayan ɗaya tana yi musu godiya, tana zuwa kan Huzaifa ya wani maze ya ce ‘Kar ki damu, wannan fa bakomai bane ba, idan har zaki dinga biyayya”.

“Ba zan yi biyayyar ba, na san ma ba uwar da ka saya mini, duk gidan nan waye ya kai ka talauci da son banza?”

“Laaaa, ke fa ba a abin arziki da ke ko?”

“A’a yi haƙuri mama, shi ɗin ne zai ɓata mini rai, yanzu a cigaba da zuzzuba tuwon ina kaiwa, amma wallahi duk in da na san ba za a bani kuɗi ba, sai dai Yasir ko Huzaifa su kai”

Haka tayi ta rabon Abinci cikin annashuwa, gidan da aka bata kuɗi tayi ta murna, idan ba a baya ba tayi ta jin haushi.

********
Ba zata iya ƙayyade rabonta da gidan nan ba, dan haka ta ɗaga kai take ta na kallon sauye-sauyen da aka yi a gidan.
Ya ƙawatu, duk da ginin yana nan a yadda yake, amma an yi wa gidan gyara sosai.
Da haka ta ƙarasa cikin ƙaton falon da ke cikin gidan.

Hadimai ne ke ta kaiwa suna komowa a cikin tangamemen falon, suna aikace-aikace.

Ɗaya daga cikin hadiman ce ta kalli Iman da fara’a ta ce “Maraba da zuwa”.

Iman ta ce “Yauwwa sannunku da aiki, Ummma fa?”.

“Tana cikin turaka, bari ayi miki iso”

Babu jimawa hadimar ta fito, ta kalli Iman ta ce “Bisimillah, ta ce ki shiga”

Bayan hadimar Iman ta bi, zuwa turakar Ummma.
Shigarsu ɗakin ke da wuya, gaban Iman ya faɗi, bisa tozali da mutanen da ba ta son ko haɗa hanya da su, ba dan jinin Ummma bane su, to tabbas da kai tsaye zata iya cewa mutanen da ba ta ƙauna.

Faɗaɗa murmushi Ummma tayi ta ce “Masha Allah, Iman dama talaka na ganinki?”

Murmushin yaƙe iman ta ƙaƙalo, ta durƙusa a kan gwiwoyinta tana gaida Ummma.

Cikin mutuntawa Ummma ta amaa mata, tare da tambayarta ya Ammi.

“Hajiya Iman, manya manyan ‘ya’ya a gidan Galadima, ya kike ya school?” cewar wata matashiya da ke zaune a gefen Ummma.

Ko ba a gaya mata ba, ta san da biyu budurwar ta yi wannan maganar, ta dake ta ce “Lafiya lau Anty Soafy, an yi salla lafiya?”

“Hmm lafiya lau, irin wannan ado haka, Ummma wannan leshin kamar irin sa Khairiyya ta saka ranar kamunta ko?” Tayi maganar tana ƙarewa Iman kallo.

Umma ta ce “Eh irinsa ne”

“Wow, it worth 120k fa, lallai autar gidan Galadima, kin riƙe wuta”.

Iman jin ta take tamkar a kan wuta, dan haka a gurguje ta ce “Ummma dama abincin salla ne, Ammi ta ce na kawo miki, kuma nazo mu gaisa, bari na tafi”.

“Kai Iman tun da wur haka, ke dai ba kya son mutane, shikenan bari na baki barka da salla”.

“A’a Umma, ai na girma da barka da salla” iman tayi maganar tana miƙewa .

“Ƙaniyarki, tsaya ki karɓa mana” girgiza kai iman tayi, ta fice daga ɗakin da sauri.

Har ta kai tsakiyar falon, ta ji an riƙe mata jaka.
Ta waiwayo tana kallon wadda ta riƙeta.

“Duk na san kin ci kin ta da kai, Ammi tana ji dake, na san kina da kuɗi baki rasa komai ba, amma yakamata ki karɓa tun da kin san baki da gado a cikin dukiyar gidan Galadima?”

Cikin rauni Iman ta ce “Anty Soafy me kuma ya kawo wannan maganar?”

Cikin ko in kula Soafy ta ce “Yau aka fara gaya miki irin wannan maganar ne, ai gara a dinga yi ana tuna miki, ko ba haka ba?” Ta fizgi jakar iman, ta saka mata kuɗin, ta saƙala mata jakar a kafaɗarta ta koma ciki.

Gwiwa a saɓule, iman ta nufi fita daga falon, tuni idanunta suka cika da hawaye, sai dai tana fitowa ya sha gabanta, ya ƙureta da idanuwansa.

Ƙoƙarin ratsewa take ta wuce, amma ya ce “Me ta ce miki ne, har ta saka ki kuka?”

Girgiza masa kai tayi alamar bakomai.

Yayi murmushin gefen baki ya ce “Anyway, kin yi kyau sosai a outfit ɗin nan, ashe yayanki yana Saudiyya babu ko sallama?”.

“Uncle J, am sorry sauri nake, Ammi na jirana” daga haka ta wuce ta bar shi a wurin a tsaye.

**********

Zuwa yamma mama ta saka ruma a gaba sai sa ta cire shaddar nan, dan idan ta bar ruma da ita sai shaddar ta fita daga hayyacinta.

Kwanukan da aka ɓata, Yasir ya tattara yana wankewa, mama ta ce “Ke, shiga ɗakinsu ki dudduba mini idan da kwanukana, cokula ko kofi, duk ki fito mini da su, dan na san hali, sai a kai mini kwano ɗaki a ƙi fito da shi”
Ruma ta tashi ta nufi ɗakin samarin nan, ba tare da ko sallama ba.
Usman ne a kwance yana waya, kuma da alama da mace yake wayar.
Buɗe baki tayi, ta tsaya tana kallonsa. Zumbur ya tashi zaune, ya katse wayar ya ajiye ya haɗe rai ya ce “Zo nan” ba musu ta ƙarasa in da yake.

“Me ki ka ji?”

Ta ce “A ina?”

“Ina tambayarki kina tambayata? Nace me ki ka ji?”

“Wallahi ban ji komai ba, kawai dai na ji ka ce…..” Sai kuma ta yi shiru.

“Ba zaki faɗa ba sai na taka ki?”

Ta tura baki sannan ta ce “Na ji ka ce, wai kwalliyar ta tayi kyau, kamar farin wata”.

“Sai kuma me?”

“Shikenan na ji wallahi ”

“To na rantse da girman Allah, idan ki ka sake ki ka faɗa, wallahi sai na yi miki dukan tsiya, ƙanwar abokina ce ba wata ba”

“To ai ni dama ban ce zan faɗa ba, mama ce ta aikoni” daga haka ta shiga duddubawa mama kwanukanta.

Aikuwa ruma ta fito da kwanuka a hannuta tana faɗin mama “Kin ga kofin ki, an sha fura a ciki sha zumamu ya siɗe miki kofi tas, har ɓera ya fara ci. Kin ga plate ɗin ki har da sauran alalar da ki ka yi tun sati biyu da suka wuce”.

Yasir ya ce “To munafuka, uban waye ya saka ki wannan sharhin?”

Mama ta ce”Ai ba ƙarya ta yi ba, ku yi ta kwasar mini kwanuka kuna kaiwa ɗakin ku, sai na bi na tsinto abina, ƙazaman banza kawai”

Mama na tsaka da mitar sai ga Aliyu ya shigo, ya ce “Ina ruma”

Ta ce “Gani”

“Yo sauri, abokaina ne na filin ball suke tambayata kina ina, shi ne suka biyo ku gaisa, saura kiyi wani haukan da zaki zubar mini da mutunci “.

Murmushi ta yi ta ce”A’a ba zan zubar maka da mutunci ba, bari na sako gyalena”

Yana maganar ya fice, Huzaifa ya ce “Mama ke ba a zo gaishe ki ba, sai wannan yarinyar lallai ruma”.

Ta fito daga ɗakin mama da sauri, ta kalli Huzaifa ta ce “Ka yi mini Addu6, Allah ya sa su bani kuɗi” tana gaya masa ta kwasa da gudu ta fita waje.

Da fari gaishe su tayi kamar nutsatsiya, suka amsa mata cikin mutuntawa.

“Ya makaranta ya rikici2?”

Ta ce “Makaranta lafiya ƙalau, amma ni bana rikici” suka din ga jan ruma da hira ita kuma tana zuba, Aliyu sai hararta yake amma ta cigaba da zuba.

Dariya suka dinga yi mata, suka babbata barka da salla, ko ɗan cewa ba zata karɓa ɗin nan ba tayi ba, zuruf ta miƙa hannu ta karɓe tana godiya.
Wani mugun kallo yake wa ruma, amma ko saurararsa ba tayi ba.

Ta duba a cikin kuɗin da aka bata, akwai ɗari biyu da ta tsufa sosai, ta kalli wanda ya bata ya ce “Ɗan uwanmu ɗan canza mini wannan, ba zata karɓu ba” buɗe baki Aliyu ya yi yana bin ruma da kallo.

Aikuwa ya karɓa ya canza mata wata, ta ce ta gode ta shige gida.

“Mama kin ga abokan yaya Aliyu sun bani, kuma sun ce suna gaishe ki”

Mama ta ce “To madalla”

“Mama gashi ki ajiye mini, ki ɗora da lissafi, idan kin manta ni ina sane da lissafin, dan Allah mama kar na zo karɓar kuɗina ki fara ce mini, abubuwan da ki ke mini ba da kuɗina ki ke yi mini ba, wallahi mama da za ayi lissafi ban san iya adadin kuɗin da nake bin ki ba”

Cikin gatse mama ta ce “To Anty ruma, ki zauna ki lissafa duk kuɗin da ki ke bina, na biyaki”

“Dan Allah mama da gaske ki ke?”

“Eh mana” murna ta dinga yi tana cewa ‘Ai mama kuɗin da nake binki, sai ma zauna musamman na yi lissafi, tsaf sai na zama attajira da kuɗin nan, unguwar da muke zuwa a bani kuɗi ai da yawa”

Yasir ya ce “Ba zaki taɓa hankali ba”.

Aliyu ne ya shigo rai a ɓace yana hararar ruma.
Kawar da kanta tayi gefe taƙi kallonsa.

“Dole ki kawar da kai mana, yarinyar nan ana bata kuɗi ta karɓe, wai har da cewa wai wata ba zata karɓu ba, da yake ke ki ka basu ajiya”

“Yaya ba kyau mayar da hannun kyauta baya fa”

“Zaki mini shiru, ko sai na mareki, mara kai kawai”

A ranta ta ce “Ohoo dai, tun da Allah ya sa na karɓa”.

Bayan sallar isha’i yaya Umar ya dawo, duk sun daddawo suna gida, ana ta hira.
Ruma tayi gyaran murya, ta kalli Yaya Usman ta ce “Mama kin san me?”

Mama ta ce “A’a”.

Usman ya zubo mata ido, kowa ya yi shiru yana sauraron wani shirmen zata faɗa.

Ayshercool
08081012243

(INCLUDE ME IN YOUR PRAYERS PLEASE 🙏)
[05/07, 5:40 pm] JAKADIYAR AREWA:                     ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER’S ASSOCIATES

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ku yi subscribing  YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.

Back to top button