Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 11

Sponsored Links

P11

Girgiza kai kawai Abubakar ya yi, ya ja bakinsa ya tsuke.

“Yaya ya na ji kuma kayi shiru?”

“To ruma ba dole na yi shiru ba, kowa yana nemawa kansa mafita a rayuwa, amma ke in da ki ka dosa daban?”

“To wai me na faɗa ba dai-dai ba?”

“Yanzu ke tsakanin ki da Allah, kin taɓa ganin mace a titi tana bada hannu a ƙasar hausa?”

Ta ɗan yi shiru sannan ta girgiza masa kai ta ce “A’a, to mawaƙiya fa ko film?”

Abubakar ya ce “Ba kushe sana’ar wani zan yi ba, amma ki yi tunanin wani abun daban”

“To ba sai a buɗe mini kanti ba”

“Yanzu a unguwar nan gaya mini shagunan da ki ka ga mata ne a ciki suke sayar da abu?”

Ta yi farat ta ce “Ga maman Olu beyerabiya”

“To ke bayerabiya ce?”

“A’a amma dai…..”

“Kin ga, ya isa haka, dama ni a kan career ki nake magana, tun da baki gane me nake nufi ba shikenan” ita sam ba ta ga aibun abin da ta ce tana so ba, dan haka ko a jikinta ta share.

Gwaggo ta fara shirin tafiya, su Yasir suna ta murna, dan dama duk ta ishe su da faɗa da azabar saka ido.
Shi kansa mai sunan Baba murna yake ta tattara ta tafi ta bar musu gida su huta, dan ta saka shi a gaba da yawa, dan ma Allah ya taimaki Abubakar bai fi sati ba ya koma makaranta.
Amma kullum cikin surutu takewa mama “Hauwwa wannan zagada zagadan yaran naki, duk sun isa aure amma kin tare su a gaba kina ado da su a gida, ga ƙauye can muna da mata burjik, amma dan mugunta kin tare su kin hana su motsi’

Mama ta ce “Haba Gwaggo, guda nawa yaran suke, haryanzu su Baba basu haɗa talatin ba fa, duk girman jiki ne, kuma kina ganin irin rayuwar da ake sai godiyar Allah, babu mai ƙwaƙwarar sana’a sai ƙarfin hali, idan suka ɗauko aure da yaya za su riƙe?”

“Ba wani nan, idan mutum yayi aure Allah zai warware, amma kallesu dan Allah tuma-tuman gwauraye ki na ado da su a gida, babu mai mata, kalli dai wannan zagaren, sai dai ya shigo fuska kamar bajimin sa, ya zo ya ɗau abinci ya fita yana zazzare ido kamar wani zaki, ko fara’a ba ya yi, kai haka zaka yi wa matar ma idan an aureka?, ko da yake ma wace macence za ta auri mutum ba fara’a ba komai fuska kamar kunun kanwa ba rahama”
Lomar Abincinsa kawai yake kawai, ko motsi bai yi ba, balle ya nuna ya san da shi take, yana jin ta ya share ta.
Ruma kamar ta kwashe da dariya, jin an ce fuskar yaya Umar kamar kunun kanwa, amma sanin ruwa ba sa’an kwandon ba ne ya sanya ta ja bakinta ta tsuke.

“Umaru da kai fa nake” A hankali ya ɗago idanunsa ya yi mata wani irin kallo, ya mayar da kan sa ya cigaba da cin abinci.

“To Allah ya kyauta, ka ma dai mayar da ni mahaukaciya, ka je ka ƙarata, tattara kayana ma zan yi na bar muku gidan ku, gobe goben nan zan bar garin nan.
A hankali yasir ya ce “Alhamdilillah, Allah ya raka taki gona”
A rikice ruma ta ce “Haba Gwaggo, ni bana son ki tafi, dan Allah ki zauna bamu gaji da ganinki ba”.

Huzaifa ya yi ƙasa da murya ya cewa Abdallah”Ji munafukar ‘yar nan, ko a gidan uban waye bamu gaji da ganin na ta ba, mata duk ta addabi mutane?”

Abdallah ya ce “Ashe ka manta wacece ruma, ai wannan yarinyar tsaf sai ta haɗa yaƙin duniya na uku, duk abin da ta san za ta aikata wanda ba a so shi take yi”‘

Kamar wasa ruma har da kuka, wai kar Gwaggo ta tafi, ji suka yi kamar su yi wa ruma taron dangi su zaneta.

Ganin ruma na kuka, ya sanya Gwaggo ta ce ba zata tafi yanzu ba, saboda ruma.

*****
Sauri-sauri take yi, tana tafe tana duba agogon hannunta, tana daf da makara zuwa wurin da zata.
Tana ƙarasawa harabar gidan ta ɗan ɗaga murya ta ce “Gali, gani na fito zo mu je na makara”

Cikin girmamawa da murmushi Gali ya taso ya ce “Allah ya taimaki ‘yar gaban goshi, Allah ya ƙara miki lafiya uwar ɗakina, ai tun ɗazu ke nake jira, tun da tun huɗu ki ka ce mini”

“Kai dai bari, na tsaya na yiwa Ammi girkin dare, kar na je ban dawo da wuri ba ka san ba komai take ci ba”

Ya ce “Haka ne, bari na fito da motar” ya yi gaba ita kuma ta tsaya.

‘yan mata ne su huɗu, suka fito ta ƙofar wani sashi na cikin gidan, suka tunkaro in da take wajen harabar gidan, hakan ya yi dai-dai da fito da motar da Gali ya yi.
Kai tsaye suka tinkari motar ba tare da sun kulata ba, suna ƙoƙarin buɗewa su shiga.
Da sauri Iman ta ce “Kai, fita fa zan yi, zai kai ni unguwa ne”

Ɗaya daga cikin su ta kalleta ta ce “Saboda ta ki fitar zamu fasa tamu ne?”

Iman ta ce “A’a ba haka nake nufi ba, na ga kun iya driving, kuma ga wasu motocin, ni Ammi ta hanani tuƙi ne, kuma na yi magana da Gali tuntuni a kan zai kai ni unguwa”

Cikin tsawa ɗaya daga cikin su ta ce “Shut up! Mu ki ke kallo ki ke gayawa haka, kin manta a tuna miki ne?”

“Me ku ke yi haka a tsatstsaye?” Gaba ɗaya suka waiwaya suka kalli mai maganar.
Jikin Iman ne ya yi sanyi, tare da shiga wani yanayi mai wuyar fassara, bayan sanya idanuwanta a cikin nasa.

Fauziyya ta cire glass ɗin fuskarta ta ce “Bro, wannan ƙanwar ta ka ce take yiwa mutane rashin kunya, duk motocin gidan nan ta rasa wadda za ta hau, sai da muka zo muka ce a kai mu unguwa, wai ita ma tilas ita zata hau a fita da ita”
Ya tsuke fuska ya kalli Iman ya ce “Wato ke tsagerancin naki har ya kai ki din ga yiwa na gaba da ke rashin kunya ko? Sa’anninki ne su?”

Jiki a sanyaye ta kallesu, sannan ta mayar da idonta kan sa, sai dai ta kasa magana, sai hawaye da suka cika mata ido.

“Ina magana zaki yi mini kuka, get out from my sight, stupid girl”

Gaba ɗaya ta rasa meya kamata ta yi, jiki a sanyaye ta nufi hanyar fita daga gidan.
“Ke zo nan” ta ji muryarsa ba tare da ta yi tsammanin hakan ba.
Ta juyo ta dawo in da yake tsaye.

“Ina zaki?”

“Napep zan je na hau”

“Wuce ki koma, ba zaki fita ba” yayi maganar cikin bayar da umarni. Ta kalli yadda motar da su Fauziyya suka shiga ta bar gidan. Ba ta ce masa ƙala ba, ta koma sashin su, sai dai duk yadda ta so ta riƙe hawayenta abin ya faskara, tuni hawayen suka wanke mata fuska.

“Subhanallah, abar ƙaunata ya haka? Meyafaru? ya baki tafi ba?” Ammi ta yi mata tambayoyin a jejjare cikin ruɗewa bayan ganinta ta na kuka.

Iman ta share hawayenta ta ce “Bakomai Ammi, kawai fasawa na yi”

No ban yarda ba, gaya mini”

“Ammi su Fauziyya ne da Yaya Mahmud”.

Nan da nan Annurin fuskar Ammi ya ɗauke gaba ɗaya ta ce “Mahmud again? Tura fa ta fara kaiwa bango, meya yi miki?”

Iman ta share hawayenta ta ce “Ammi dan Allah ki bar maganar, kar ranki ya ɓaci, bana son ki damu”

Ammi ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce “Na ji, amma me suka yi miki?”

“Dan Allah kar ki damu Ammi, bakomai ki yi haƙuri”

Jinjina kai Ammi ta yi sannan ta ce “Yanzu shikenan, kin fasa fitar kenan?”

Iman ta ɗaga mata kai alamar eh. Ta ja hannun Iman suka bar falon.

****

Cikin rarrashi mama take magana, “Ruma, aiken ki nake son yi, amma bana son ki je ki yi mini shirme, ko ki tsaya a in da ban aike ki ba”

“In sha Allah mama, ba zan tsaya a ko ina ba, fiii zan ware dogayen ƙafafuwana da bala’in gudu na je na dawo”
Mama ta ce “Wane irin gudu kuma? Kalen ki watasar mini da kayan aiken, ki tafi a hankali, ki yi sauri ki je ki dawo”

“In sha Allah zan yi sauri, na je na dawo”

Mama ta gaya mata in da take so ta je, tare da abin da za ta kai, ruma ta sauya kaya ta saka hijjabi, ta fita yi wa mama aike, ta ƙuduri aniyar za ta je ta yi sauri ta dawo ko dan ta farantawa maman.
Tashin farko ta bi ta cikin unguwa, tana tafe tana kalle-kallenta, duk wani lungu da saƙo idan ta bi sai an kira sunanta, dan kusan kowa ya santa.

A ƙofar wani shagon aski ta ga keken Huzaifa, hakan ya tabattar mata da yana cikin shagon.
Murmushi ta yi ta nufi ƙofar shagon askin, da sallama ta buɗe ta shiga cikin shagon.
Duk maza ne a ciki, ga Huzaifa ya zauna a kan kujera za ayi masa aski, jin sallamar mace ya sanya dukkansu suka juya suna kallonta.

“Ohh Huzaifa yau Allah ya yi zaka cire wannan sumar kenan? Kuma wallahi aka yi maka askin ‘yan iska kai da mai sunan Baba”

A ƙule Huzaifa ya ce “Ke uban me ya kawo ki nan? Ba ki ga shagon aski bane?”

“To ni ina ruwana da wani shagon aski, ba dai mutane ne a ciki ba, keken ka na gani a waje na san kana nan, na ce bari na leƙo na ganka”

“To na ji na gode, fita ki bar wurin nan”

“To sai ka tsaya na gama kallon kalandar askin nan, sai na tafi ” tayi maganar tana riƙe ƙugu, tare da zubawa kalandar ido.

“Ni wannan yarinyar ba ke na taɓa rabaku faɗa da wasu yara ba, kun dawo daga makaranta?” Cewar wani da yake zaune shima yana jiran askin.

“Eh nice, me na yi kuma?”

Ya ce “A’a gane ki kawai na yi”

“To yanzu da ka gane ni lada nawa aka baka?”

Mai aski ya ce “Deluwa, dan Allah ki yi haƙuri, wurin nan duk maza ne, ki je aiken da aka yi miki, ko kuma in saka a riƙe mini ke na yi miki aski”

“Aikuwa da sai ka kasa zaman Ɗorayi, sai na saka yayyena sun kakkaryaka sun zubar, ni zaka yiwa aski?”

Huzaifa ya miƙe tsaye rai a ɓace ya ce “Bi ƙofar da ki ka shigo ki fita”

Ta ɗan kwaɓe baki ta ce “Huzaifa ba ayi maka gwaninta, daga ziyara?”

“Ki fita na ce, wallahi na zo in da ki ke sai na gwara kan ki” ja ta yi ta tsaya cike da taurin kai tana kallon idonsa, hakan ya ƙara tunzura shi, yayi kanta amma suka riƙe shi, ta fita da gudu daga shagon.

Tana fita ta yi ƙwafa, ta tura keken sa ta ji bai rufe ba, keken ya fi ƙarfinta, amma ta haye ta yi gaba.

Wani ya leƙa shagon askin ya ce “Huzaifa ƙanwarka ta ɗau keken ka fa ta tafi”

Da sauri ya miƙe ya leƙo, ai tuni ta kusa ƙarshen layin, ya san ko da ya bita ba zai cimma ta ba.
Kawai yayi tsaki ya koma ya zauna, zuciyarsa na tafasa, ‘yan cikin shagon suka din ga dariya, kowa na tofa albarkacin sa a kan halayar ruma.

Haka nan tun da ruma ta fita, mama ta kasa nutsuwa, kawai dai gata nan ne dai, ta fara dana sanin dalilin ma da ya sanya ta aiketa.

Tun tana saka ran ta ga ta ina za ta shigo gidan, har ta fara fidda rai, yanzu ba ta fiye ɗaga hankalinta ba, idan ruma ta fita makaranta ko aike ba ta dawo da wuri ba, sai dai fargabar mai za azo ace mata ruman ta aikata.

Aikuwa ilai, tana cikin wasi-wasi sai ga sallamar wata matashiyar budurwa da wata yarinya, yarinyar bakinta a fashe, jikinta duk kwata ga fasashshiyar roba, da sauran gari a cikin ta, yarinyar sai kuka take, yawu da jini yana zuba daga bakinta.

Cikin kaɗuwa mama suka gaisa da matashiyar yarinyar, mama ta hau tambayar ba’asi.

Babbar ta ce “Dama cewa aka yi na zo gidan su na faɗa, ruma ce ta taho a kan wani ƙaton keke kashe gardi, ta taho da gudu, ƙanwata ta karɓo niƙa, ta bugeta da keken ta faɗa kwata, ita ma ta faɗi a gefe, ta tashi ta karkaɗe jikinta ta hau keken ta gudu, kuma ba iya ƙanwata ta buge ba, tun da tana tafe tana faɗuwa a kan keken”

“Innalillahi wa Innalillahi raji’un, ya Allah kai ka jarrabeni, Allah ka dube ni, ka bani ikon cin wannan jarrabawa” mama ta kamo hannun yarinyar da aka jefa kwatar, ta wanke mata jiki, ta basu dubu ɗaya tare da basu haƙuri ta ce zata zo har gida ta basu haƙuri.

Gwaggo kuwa ta hau masifa “Wallahi mutanen maraya ba ku da kara a kan ɗa, yanzu saboda wannan ɗin aka wani aiko yawon kan ƙara, ai ɗa na kowa ne, kuma fitinar maraya ai daban take”

Kamar mama za ta yi kuka ta ce “Ba wnai fitinar maraya, dama can haka ake fama da ita, a ina ta samu keken da ta hau ni da na aiketa wuri daban, kullum sai ruma ta sakani asarar kuɗi da yawon ban haƙuri, nan gaba idan ba ayi wasa ba, sai wasu sun kai ƙararmu ga hukuma”

“A’uzubil’ahi kina uwa ba zaki faɗi alkhairi a kan yarinyar ki ba, ƙuruciya ce, kowa da irin ta sa” mama ba ta kuma cewa komai ba, idan ta biyewa zuciya, za ta iya musayar yawu da Gwaggo, wanda ba za ta so hakan ba.

Huzaifa ya shigo a kumbure yana bala’i “Mama! Ina ruma take wallahi yau sai na tattakata, sai na ci mutuncinta”
Mama da take a ƙule ta kalle shi ta ce “A ina ka ganta?”

“Mama shagon aski fa ta bini, na koreta shi ne ta ɗauke keke na ta gudu, ni sa’an wasanta ne ita duk wani halin zubar da mutunci ta iya”

Mama ta safe kai ta ce “A ina da ta samu keken kenan? Za ta gane ba ta da wayo da Baba zan haɗata bari ta dawo”

“A’a ke wace irin uwa ce, wannan mugun ɗan na ki, haka kawai ya kassarata a’a ban lamunta ba ”

Huzaifa ya harari Gwaggo ya ce “Wallahi ko ba a gaya masa ba, da hannun nawa zan ci ubanta, sai na girgiza ƙashin haƙarƙarinta ”

Har gefin magariba babu ruma babu alamarta, tun mama tana jurewa, har ta saka aje a nemo mata ruma.

Aliyu Allah ya bawa sa’a, ya ganota a wata tawagar ‘yan d.j, ana biki an kunna d.j, ta shige tsakiyar manyan mata, ana rawar sabada, ta gantsare sai rawa take, tana wani juye-juye sai ka ce an saka mata batir, ga ta a shafe ba gaba ba baya ama sai karkaɗa jiki take.
Cikin ‘ya’yan Mama, Aliyu Ustaz ne, ba shi da ra’ayin wannan abubuwan, amma yau a saboda ruma, sai gashi a tsakiyar mata, ya samu bayan ruma da take ta juyi, ya tsula mata tsumagiya.
A zafafe ta ƙandare ta juyo, a zaton ta yaron mai D.J ne ya daketa, dan dama yana ta korar yara daga cikin filin rawar taƙi tafiya. Ba kuma rawar kawai take yi ba, har da satar kuɗin liƙi tana sakawa a cikin hijjabinta, sai ta gantsare tana rawa idan aka liƙo sai ta wayance ta ɗauke kuɗin.

Cak ta tsaya tana kallon Aliyu, ta ɗaga kai ta kalli yadda gari ya yi duhu.
“Sannu ‘yar makaɗa, aike da aka yi miki kenan ko? Fita ki wuce mu tafi”

Kasa magana tayi, a take tayi saranda, da jin za ta iya ɗaukar kowane hukunci, saboda ita kanta ta san ta tafka ta’asa.
Ta janyo keken Huzaifa, da Allah ya sa ba a sace ba, ta hau turawa, Aliyu ya haske keken, tayoyi duk sun sace, dan ɗayar ma fashewa ta yi, ga kaca ta zube keken duk wani gurin ya lotse, adon fitulun da ya yiwa keken kuwa, suma wasu duk sun fashe.
Yana tafe yana kallon ruma, yana tunanin anya ruma mutum ce, fitinarta ko su da suna kamarta ba su yi haka ba, su dai akwai dambe kamar zakaru, kamar su cinye juna, amma rashin ji a gida, rashin ji a unguwa rashin ji a makaranta wannan sai Ruma ƘANWAR MAZA.

A ƙofar gida suka tarar da Uamar, yana tsaye yana waya, tana ganinsa ta fara kuka, tana cewa “Kashina ya bushe”
Aliyu ya ingiza ƙeyarta zuwa cikin gidan, da sauri Huzaifa ya taso, dan ta kekenaa yake yi, sai dai yana kallon keken ya san ko a wurin ‘yan gwan-gwan wannan keke ba zai daraja ba, kamar yayi shekara da shekaru.
A ka rasa wanda zai ce mata komai, duk suka zubo mata ido.

Mama ta ce “A ina ka ganota?”

“Ga ta nan ku tambayeta”

Cikin muryarsa mai razanata musamman idan ba ta da gaskiya ya ce “Daga ina ki ke?”

Jikinta ya hau rawa ta ce “Dan Allah mai sunan Baba……

“Daga ina ki ke fa kawai na ce?”

Gwaggo ta ce”Ya zaka razanata da wannan muryar ta ka, ka tambaye ta cikin nutsuwa mana”

Huzaifa ya daɗe bai ji abin da yake shirin sanya shi kuka ba irin yau, ya kasa ko tari tun bayan tozali da kekensa.

Rarraba ido kawai take tana kokowa da numfashi, ganin yadda kowa ita yake kallo yana jiran amsarta.

Wata irin gigitacciyar danƙa Uamar ya yiwa kunnenta, ta kurma ihu, ya janyota har tsakiyar tsakar gidan, ya dungurar da ita, ya naɗe hannun rigarsa cikin tsawa ya ce”Ina ki ka je da aka aike ki?”

Cikin kiɗima da razani, ruma ta wassafa komai, ba ta ɓoye ba ciki har da zuwa wurin aski da yadda ta ɗau keke tana tafe tana faɗuwa, duk ta gurje gwiwa, da yadda bayan ta dawo daga aike ta tsaya wurin ‘yan bikin da ba ta san suwaye ba ma, tana rawa tana satar kuɗin liƙi.
Sai a lokacin ta faɗi har faɗa suka yi da yaron dj yana ce mata shegiya ɓarauniya.
“Yanzu ina kuɗin da ki ka ɗebo ɗin?” Yayi maganar yana miƙa mata hannu.
Aikuwa ta zura hannu a rigarta, sai ga kuɗi, a ƙalla idan aka ƙirga sun kai dubu uku da ɗoriya.

 

(SORRY FOR THE LATE UPDATE, AYYUKA SUN YI YAWA NE, INA GODIYA DA TARIN ADDUOI DA ƘAUNAR DA KU KE WA BOOK ƊIN ƘANWAR MAZA)

Ayshercool
08081012143
[13/07, 9:01 pm] JAKADIYAR AREWA: ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER’S ASSOCIATES

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ku yi subscribing  YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.

 

Back to top button