Hausa NovelsMatar Makaho Hausa Novel

Matar Makaho 5

Sponsored Links

Page 5️⃣
Dan a irin lokacin da yake tashi sallolin dare,

mikewa yayi ya riga ya gane ma’ajiyin Randa da buta fita yayi a dakin alwala ya daura ya dawo dakin,ya tada sallah sai uku ya koma ya kwanta, Kiran farko na asuba ya farkar dashi, Addu’a tashi daga bacci yaye.

A hankali ya sauka a kujira cikin sanyi ya lalube gadon ya tsaya a bakin don bazai iyya Hawa ba kar a maimaita irin na jiya a hankali yake kiranta

**sumayya!! sumayya!! *

**A hankali na bude idanuna cikin bacci nace “naji habba” baice mini kome ba ya daga kafarsa a hankali da lalube ya bude dakin ya fita **Niko waya na laluba a gefen filo don dakin ba haske na kunna hasken ya haska dakin sauka nayi Nima nayi waje don d’auro Alwala, **fitana yayi daidai da kammala tasa alwalan mikewa yayi Yana laluben sandanrsa,Harna kammala alwala Bai gane sandar ba.

*Ina kammala alwala na shiga daki daukar wayata nayi na fitoh na haska kofar aiko Naga sandar Ashe faduwa yayi a kasa, dauka nayi na zungure sa da sandar a hannu *

da sauri ya mika hannunsa ya amsa cikin sanyi sanyin sa yace nagode,

* batare da nayi magana ba don takaice waini sumy nice yau da miji MAKAHO shap wannan ai abin kunya ne ma Wanda ya sanni ya gansa a matsayin mijina, Tabbas nayi Wasa da Damata a rayuwa, shiyasa Allah ya jarabce ni a lokacin da ban taba tsammani Koh tunanin hakan ba,

**Da sauri nayi istigifari na kauda tunanin a Raina

* Koh amsa Masa banyi ba nayi shege daki na tada sallah, Ina idarwa Qur’an na dauka cikin jakansa Mai kyau na bude,

*nayi azkar in safiya, dana sabayi kullun na mike nabi lfyn gado bacci ya dauke ni,

sai shidda da rabi ya shigo dakin da sallama hannunsa rike da bakar laida na kayan shaye da kayan miya Jin ba’a amsa ba ya lalube kujira ya zauna, numfashi Daya ji kasa kasa hakan ya tabbatar Masa ta koma bacci a hankali ya mike,waje ya fita da lalube ya Isa kitchen aje laidan yayi ,

shanyar kayansa ya dauko a igiya ya nade ya shigo dakin ya lalube Ghana must go in sa Daya aje a lungun kujira da firij yasaka kayan,ya dawo Kan kujiran ya kwanta a hankali wani irin bacci Mai Dadi ya sauke sa,

**Ban tashi ba, sai Takwas na safe shima ihu da ashariya na dandazon mutanen gidan Wanda Koh tantama banayi tambe ake, shiya farkar Dani,mikewa nayi sanye da kayan baccina Wanda na saka jiya da dare riga da wando Mai taushi sosai sai hulan bacci d’uka farare ne tas.

* da sauri na dirko daga Kan gado nafitoh dakin naje na rufe kofar shashen mu don nasha Alwashe yau bamai shigarmin kofa kallo Koh ganin daki bare naji yau da tambe aka tashi* 😂 (Anya ba tsoro ba kuwa?)

*Kitchen na wuce, ganin laidan kayan Miya a kasa,

* dauka nayi na bude kayan miyane su tarugu albasa da tattasai sai dayan kayan shaye ne yau harda Madara, na laida da bouviter, bread, sugar, da Lipton,

ruwa na zuba a kettle nasa Lipton, don yau muntashi da NEPA na jona a socket bude caton indomie, na kayan garana laida biyu na dauka manya shap shap na daura na dau kwai na soya cikin 40 minutes na Gama hada breakfast na Kama shara,

✨ (tabbas aiki a wajen mace ribace babba duk kudin gidan ku duk mulki Koh gata ilimi da kyau in har mace Bata iyya girki ba gtoh Bata cika macen da za’a kira Tauraruwa ba Yan Mata a Kara bada himma karki xamantu baki da aiki sai adafa a baki kici ki kwanta kina Danna waya.koh makaranta kike zuwa at lest ki ware wasu lokutan a Rana kina Taya ma’aifiyarki,

aikin da kika tsana kina ga ana matsamiki ana bautar dake wallahih ribarta na zuwa don bakisan inda Allah zai kaiki ba)✨ *shawarace*

 

**Tun sa’ilin da aka fara Yar Hali watoh dambe, a tsakar gidansu ya farka Amma Bai Mike ba har **fitanta da rufe kofar duk akan kunnensa duk yanaji Yana kwance ,

a hankali ya mike ya fitoh cikin sanyin halinsa da nutsuwa ya bude baki yake gai Dani,

**shuru na Masa naki amsawa *

baiyi fushi ba ya kara tambaya ta, Koh Zan Kama Miki wani aiki ? Abin nasa harda rainin wayyo kenan, Wai ya kamamin aiki? da wani idon Amma saina maze nace “wanke-wanke nakeso kamin” ba musu ya lalube sandarsa da takalminsa shinyayye ya saka
Da lalube harya lalube boket, ya dauka ruwa ya Iba a Randa ya aje a gefe da laluba har yakai cikin kitchen nidai Ina binsa da ido kawai, ganin garajen sa,

cikin tsawa nace “kaiiii aje kulanan abincine a ciki”

” tsaya na nuna maka kwanukan da zaka wanke”

” Wai baka ganewa ne?

Hala banda rashin gani ma? harda rashin basira? zaka dauki kula kaje da nauye basiranka bazai baka abincine a ciki ba zaka zungumu??

Kala baice mini ba ya ajiye kawai ya jingina a gefen kitchen ya tsaya,

Zuwa nayi na dauki kwanukan nakai masa gefe na hada ruwan kunfa na aje kwando da kujira na tsaya agefe cikin masifa masifa nace gashinan Bismillah sai kazo ka wanke jiki a sanyaye yazo da lalube harya zauna Niko Ina saye a gefe ina ganin ikon Allah wanke kwanuka yake Kamar Mai ido tas suke fita Yana kifewa Kai Koh Mai ido albarka, mamakine y kamani Amma ban nuna Masa ba,

**Shara na kammala na gera daki na na jona kask’wan lantarki na zuba Turarukan wuta a dakin fita nayi Naga har yanzun Yana Kan wanke wanke

Kwanukan akwai Dan yawa na abincin jiya da yara sukaci ban samu na wanke ba Harda na dare,

*Wanka na shiga Ina fitowa na tarar ya kammala Yana zaune a kujiran tsugunne,

” Koh Mai ban shafa ba na zura kaya atamfa super Mai kyau siket da riga Mai k’wala da hannun roba* dinkin zamani

*abinci na zuba ina ci daidai lokacin shima wankan ya shiga yana fitowa wanka ya shigo dakin, Alhamdulillah Koh ba kome na Lura Yana da tsafta duk da bana rayawa a Raina Koh da Wasa zanyi rayuwar aure dashi Mai tsayi dole ya sake ni yaje ya nemi miskiniya irinsa Amma kafun lokacin bazan cutu da wari ba tunda Yana wanka ( lol😅uhmm muje zuwa zakiyi bayani )

*Fita nayi na basa waje*

Kaya ya saka wani jimemmen t-shirt da wando jeas duk da tsofene Amma sunyi Masa kyau sosai ya laluben kujira yayi ya zauna,

Ina waje ban kulasa ba naci gaba da cin abinci na kammala zamana nayi A wajen naki basa abinci shi kuma Bai tambaye ni ba Danna waya nayitaye sai kusan goma na safe na iba Masa a plt da shaye a Kofi na shiga dakin na aje Masa na koma Kan gado na kwanta,

ya jawo plt in yayi Bismillah ya fara ci

Yana tsaka dacin abinci muka ji bugun kofar shashen mu mikewa yayi zaiji ya bude na dirko daka kan gado cikin fada fada nace “bazafa ka bude kofar nan ba don yau bamai shiga kofar nan ehen kaji na gaya maka don Naga alama Yan gidanku basuje islamiyya ba”

Baice mini kome ba ya koma ya zauna

Jin Mai bugun yaki barin kunne na ya huta,

hijab na dauka na zura na fita ,don gani wani isheshshine,

Bude kofar naye idona y sauka akan wata yarinya kyakkyawa sosai farace Mai Kama da MAKAHO sak banbancin ita mace Mai karancin shikaru 18 zuwa 19 she Kuma namiji ne sanye take cikin riga na kodadd’in shadda sai hijab wuyan duk ya sabule gashinta har ya leko ta gaban goshi,

*Tunda aka kawoni wanna kaddararerren gida ban ganta cikin yaran gidan da suka zo kofana ba,

Aunty Ina kwana tace

hanya na Bata cikin dakewa nace “lafiya shigo”

Shigowa tayi daidai lokacin shi kuma ya fitoh cikin dakin murmushe dauke a fuskarsa itama murmushin take da sauri tazo ta amshi kwanukan hannunsa hade da gaishe sa ya amsa,Yana tambayar ta ya su Goggo Aminar,

Ta basa amsa

Tace in nazo nace tana gaida Amarya,ta fada tana kallona

Amsa Mata nayi ba yabo ba fallasa “Ina amsawa”

Fita zaiyi hade da tambaya ta Koh akwai abinda za’a saya Kai tsaye nace “babu “sa Kai yaye ya fita hade da cewa Khadija in Zaki tafi ki biya ta guna, da toh ta amsa Masa

Nidai daki na wuce naje na kwanta sai da Naji fitarsa tukum na kwala Mata Kira ” Khadija shigo daki Mana kina tsaye a waje” don haka kawai naji yarinyan ta kwantamin sosai a Rai duk da bansan Alakarsu ba amma nasan akwai alakar jini a tsakanin su,

Da sallama ta shigo dakin na amsa Mata tana kukarin zama a kasa nayi saurin cewa tahau kujira Amma Taki da kerta zauna, firij na bude na dauko mangoron jiya da yayanta ya kawo na hada Mata da drinks harda ruwa na aje mata hira take mini Kamar na saba da ganin akwai ta da surutu sosai tun Ina amsa Mata har bacci ya dauke ni,

Ban farka ba sai 1:30 na Rana shima kiraye kirayen sallane ya tashe ni sai a lokacin na tuna Ashe fa Ina da bakuwa,
A hankali na sauke idona akan kujiran da na barta akai da mamaki sai Naga wayam ba kome,

Sauka nayi a gadon na fita a dakin cike da mamaki nake bin kofar da kallo har idona ya sauka akanta cikin sabon mamaki ganin ta a cikin………………..

Good morning fan’s 🌥️

An gaishiku Yan free books💃🏼💃🏼💃🏼💃🏼

🍀MATAR MAKAHO FAN’S GROUP 🍀
Naga comments naku naji Dadi Kuma Ya karfafa mini gwwa

🪀My WhatsApp number
08084453785
[9/27, 4:10 PM] +234 806 983 1049: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 *
~ Na ~

🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌
Free book🤧

😒 *More comments*
😏 *More post*

Back to top button