Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 63

Sponsored Links

Shiru Jiddah tayi ta tallabi chin dinta tana kallonsa lkci daya kuma tana murmushi, Sudais ya hade rai yace “Magana fa nake maki jiddah?” Ta tabe baki tace “Amira na ba ta kai maka daki, kaje ka tambaye ta” wani kallo ya dinga mata yace “Amirar xaki ba files jiddah?” Cikin halin ko in kula tace “Ita, ko bata isa aike bane, Beside if they are that important ai baxa ka bar su yashe a dinning area ba” Girgixa kai yyi ya juya ya fice daga dakin, tayi wani murmushi mai sauti tana girgixa kafarta, lkci daya murmushin yayi fading a fuskarta, da ajinsa, da kyansa, da iliminsa da kudinsa duk fadin duniyar nan ya rasa warce xai kawo mata matsayin kishiya sai warce ta taba cikin shege ta haife yaran… Wani dariya ta kwashe har da kyakyatawa ta mike tana wani murmushi tace “Abomination” daga haka ta fice daga dakin, sai dai fa jin ranta take fess. Har khadijah ta fara bacci Shureim ya shigo dakin, ta dinga kallonsa har ya iso inda take yace “Anty cire min uniform” mikewa xaune tayi ta shiga cire masa uniform din jikinsa tace “Have u eaten?” Ya gyada kai yace “Uncle ya bani cornflakes” Khadijah na kallonsa tace “Are you okay with it?” Ya wara ido yace “Ehh Anty, ai da yawa ya bani, shi kuma ya sha tea” Khadijah bata ce komai ba ta dinga laluba aljihun wandon sa jin akwai abu a ciki ta fiddo Chocolate tana kallonsa tace “Wa ya baka?” ya karba da sauri yace “Aunt din nan ce ta bani, tace min xata siya min puzzles amma bata siya ba she is sick, she is even sleeping at the room” Khadijah ta ajiye kayan bata ce komai ba, ya kamo hannunta yace “Anty will you go and check her?” Wani kallo ta dinga masa strictly tace “If I should slap you….” A hankali ya koma baya yace “Anty kiyi hakuri” tana hararansa ta nuna masa bayi tace “Wuce kayi alwala” ba musu ya wuce da sauri, ta mike don fiddo masa kayan da xai sa, magungunan sa da khaleel ya siyo masa daxu da safe ta basa sannan ta ce yaje parlor yayi assignment dinsa, ta hada socks dinsa xata shiga bayi ta wanke wayarta yayi ring ta dawo tana kallon wayar taga Barrister ke kiranta, ta karasa ta dau wayar ta xauna gefen gado sannan tayi pick din call din ta kai kunne, a hankali yace “Am sorry you called bana kusa Amira” tace “Ba komai, ka isa lafiya?” Yace “Lafiya Alhmdllh dear” tace “Ya Amira fah?” Yace “She’s fine, how about my son” tace “Yana assignment” yace “Ohk ba shi mu gaisa” mikewa tayi ta fita parlor ta ba Shureim wayar tace “Abba yana son maka magana” ya karbi wayar yana kallonta yace “Anty waye Abba?” Harara ta watsa masa tace “C’mon answer ur call…” ya kai kunne a hankali yayi sallama, Barrister dake jin su yayi murmushi yace “How you boy?” Yace “Am fine Abba” Barrister yace “Ka je schl yau?” Ya gyada kai yace “Ehh na je” yace “Good, always aim good grades sai in siya maka Bicycle” ya wara ido yace “My two uncles sun ce xa su siya min bicycle, kaga am having three now, sai in ajiye ma Sudais daya, in ba su fadeel daya, Ni kuma…” Khadijah ta kwace wayar hannunsa ta koma daki, ta kai kunne a hankali tace “You need rest barrister, ya kamata ka huta, hope ka ci abinci?” Yace “Me yasa kika amshe wayar?” Tace “He is talking off hook” yace “Baki son dai in san two uncles din nasa” ta wara ido tace “Aliyu da Dr Ayman yake referring as two uncles fah?” Barrister yayi murmushi yace “Alryt then” ta langwabar da kai tace “Toh ka ci abinci?” Yace “Eh yanxu xan ci” tace “Toh shkkn, kaje ka ci, a shafa min kan Namecy na” yace “Ohk, will do that in sha Allah, thanks love” daga haka ya katse wayar, tayi murmushi ta ajiye ta kwashi socks din Shureim ta shiga bayi don wanke su. Washegari gaba daya bata da lectures ranan, da wuri ta shirya Shureim ta tafi kai sa makaranta don bata son khaleel ya xo yace xai kai sa, tana dawowa ta rufe kofar ta ta wuce bedroom ta kwanta, sai kusan sha daya ta tashi daga baccin da tayi, yunwan da take ji yasa ta wuce kitchen don neman abinda xata ci, ta kunna gas ta daura ruwa ta dauko indomie da kwai taji kamar motsi a baya, ta isa gun window ta tsaya kafin ta leka a hankali, tsaye ta ga Jawahir… khaleel na bayanta ya rungumota fuskarsa dai dai nata, yana d’aga karamin weight da hannu daya, Khadijah ta sauke idonta a hankali ta juya ta bar wajen, kashe gas din tayi ta fice kitchen din gaba daya ta wuce daki ta kulle ta fada kan gado. Ta fi awa uku a haka, har lkcn sllh yayi ta kasa tashi, cike da karfin hali ta mike daga karshe tana runtse ido ta shiga bathroom ta dauro alwala ta fito, tana idar da sllh ta sa hijab ta dau karamar jakarta da waya ta fita, tana kokarin rufe apartment dinta Khaleel ya fito, bata kalli inda yake ba ta gama rufewa ta juya xata wuce yana kallonta yace “What’s wrong with you Khadijah, are u sick….” da kyar tace “No, i am okay” daga haka ta wuce waje ya bi ta da kallo, cab ta tsayar a waje ta shiga, kawai gani tayi ya ajiye ta schl, ita dai bata san ya aka yi ta ce masa can xata ba, ta fito ta basa kudinsa ta wuce ciki, cafteria ta nufa direct tana shiga ta xauna ta hade kai da table jin numfashinta na sama, ba a dau lkci ba Maryam ta shigo cafterian da frnds dinta xa su ci abinci, tana ganin Khadijah ta gane ta duk da kanta a kife yake har lkcn, ta isa kusa da ita tace “Hi Khadijah are u okay?” Da kyar Khadijah ta dago kanta, Maryam ta dinga kallonta ganin yanda idonta ya kada tace “Subhanallah baki da lafiya ne?” Kasa bata amsa Khadijah tayi, kana ganinta kasan she is in pain, Maryam ta fiddo wayarta a jaka da sauri ta shiga kiran Aliyu sanin yana within area din makarantar, Yana dauka tace “Ya Aliyu kana kusa ne plss, yanxu na shigo cafteria naga Khadijah kamar bata da lafiya, and she is not even responding, ko xaka taho yanxu plss….” Bata gama maganar ba Aliyu ya katse wayar, ta ja kujera ta xauna kusa da Khadijah tana kallonta da damuwa tace “Sannu Khadijah” frnds dinta turawa sai sannun suke mata su ma, Aliyu ne ya shigo cafterian ya karaso kusa da ita da sauri yana kallonta yace “Iman…. what’s wrong, are you okay?” Tun Khadijah ma ganinsa bibbiyu a gabanta har daga karshe ta daina ganinsa kwata kwata, Bata sake bude ido ba Kuma sai can kusan magrib ta ganta kwance kan gadon asibiti, dafe kirjinta tayi ta dinga bin dakin da kallo, a hankali idonta ya sauka kan Aliyu dake xaune kusa da ita ya jinginar kansa da kujerar da yake kai idonsa a lumshe, kokarin tashi ta shiga yi hakan ya sa shi bude ido, da sauri ya mike ya dawo kusa da ita da damuwa yace “Stay still Iman kinga ruwa ne a hannun ki, how are you feeling now?” ta kalli drip din hannunta har sannan tana rike da kirjinta da kyar tace “It’s hurting me” yayi kasa da murya yace “Kiyi hakuri xai daina Iman you are still under medication, koma ki kwanta plss” taki kwanciya ta hade kai da gadon, hawaye ne ya shiga sakko mata, a hankali yace “Iman?” Ta ki dagowa, hakan yasa ya tsaya yana kallonta cike da tausayi, cike da karfin hali ya ji tace “What about shureim….” Yana kallonta murya can kasa yace “I went to pick him in the evening na tarar neighbor din ki ya je ya dauke sa” Bata ce komai ba kuma bata dago ba yace “Let me call a nurse… Ina xuwa” daga haka ya fita dakin, ita dai har sannan bata dago ba hawaye kawai take kamar an bude tap, tare da wata baturiyar nurse ya dawo, ta duddubata ta fita, a hankali Aliyu yace “Iman kukan me kike plss?” ta kallesa hawaye na ci gaba da sakko mata ta kasa cewa komai, rikicewa yayi ya dawo kusa da ita sosai, yace “Don Allah Iman tell me whats wrong, me ya faru, me ne ke damun ki? Ur Bp isn’t encouraging, ur condition don’t need this, Tell me what ur problem is Plsss, ko an maki wani abu ne” ta goge idonta a hankali bata ce komai ba, Bude kofar ward din aka yi Maryam ta shigo tare da mum dinta, Hajiya Mariya ta karaso da damuwa tace “Sannu Khadijah, ya jikin naki yanxu?” a hankali cikin sanyi tace “Da sauki Mumy, Ina yini” Hajiya Mariya tace “Lafiya lau, Ina Shureim din” Aliyu yace “Neighbor dinta ya dauke sa schl daxu” Maryam ta ajiye basket din abincin hannunta tana kallonta tace “Allah ya sauwake murya can kasa Khadijah tace “Nagode Maryam” Hajiya Mariya tace “Nan xata kwana, ko xa su yi discharging dinta?” Aliyu yace “Sai gobe da safe” Hajiya Mariya tace “Toh shkkn sai Maryam ta kwana tare da ita” Shiru Aliyu yayi ya rasa me xai ce don bai so haka ba, Hajiya Mariya ta ja kujera ya xauna ta bude basket din don debar ma Khadijah abinci, sai kusan karfe takwas ta bar asibitin tare da Aliyu ba don ya so ba, suna fita babu dadewa wayar Maryam ya fara ring, dauka tayi ganin Jawahir ke kiranta ta d’an wara ido ta daga kafin ta ce komai taji muryar khaleel, xaro ido tayi tace “Ina yini Dr?” Yace “Lafiya lau ya kike, I want to ask plss Maryam, Kun hadu da Khadijah schl yau?” Maryam tace “Gata nan ai muna asibiti bata da lafiya, she collapsed daxu a cafteria but da sauki yanxu she’s recovering” khaleel bai san lkcn da ya mike ba, jawahir dake kwance Shureim a gefenta dai sai kallonsa take, ya jira har Maryam tayi shiru kafin a hankali yace “Wani asibitin ku ke?” Ta fada masa sunan asibitin yace “Toh xan xo yanxu” daga haka ya katse wayar, yana kallon jawahir yace “Xan je duba Khadijah clinic yanxu she is sick, I will be back soon” jawahir dai bata ce komai ba ya nufi kofa, Shureim ya sauka daga kan gadon da sauri yace “Uncle ni xan bi ka” jawahir ta jawo sa jikinta tace “Don’t worry yanxu xai dawo” a parlor khaleel ya dau makullin motarsa ya bar gidan ya nufi asibitn da Maryam ta gaya masa, yana parking a haraban hospital din ya fito ya kira Maryam don da wayar jawahir ya taho, Maryam na daga kiran yace “Ina waje Maryam” ward number ta fada masa yace “Thanks” daga haka ya katse wayar ya shiga asibitin, ya fi seconds talatin a bakin kofar ya kasa budewa, can ya murda a hankali ya shiga ward din, Kwance Khadijah take idonta lumshe, Maryam ta mike ganinsa tace “Sannu da xuwa Dr” yace “Yauwa Thanks” karasowa yayi bakin gadon yana kallonta, Maryam tace “Ina jin ta koma bacci” shiru yayi bai ce komai ba yana kallonta har lokacin don yasan ba bacci take ba, he really want Maryam to excuse them but he don’t know how to make the approach, kamar kuwa Maryam tasan abinda ke ransa ta mike ta dau wayarta tace “Doctor bari inyi making wani call in dawo yanxu” ya kalleta yace “Alryt” daga haka ta nufi kofa ta fita ta rufe kofar, ya lumshe ido ya bude ya xauna gefen gadon ya kamo hannunta ya kai fuskarsa dai dai nata a hankali yace “I know you are awake Khadijah, look at me plss”

Back to top button