Duk KarfinIzzata Book 2Hausa NovelsHausa Novels

Duk Karfin Izzata Book 2 Page 9

Sponsored Links

Book 2

*Episode 9*

Uk

….wurgi yayi da ita kasan dutsen ya juya abun sa,ya shiga mota chike da tsanar hiyana ya ja motar da gudu ya bar wajen dai dai lokacin lokachin motar Khalid ya iso wajen yana kashe motar suka fito da sauri, a sukwane Fahad ya chiro wayar sa dake aljihun sa tare da balle agogon diamond dake hannun sa ya miƙawa yaya Khalid yayi tsalle ya faɗa kasan dutsen ya ce bi bayan hiyana, ta sauri yaya Ahmad ya karisa wajen yana kokarin faɗawa yaya Khalid ya riƙe sa yana faɗin “muje mu sauka kasan dutsen mu tare su a chan, a tare suka koma chikin mota yaya Khalid ya jasu juya kan motar yayi suka bar waje.

Suna karisawa kasan dutse daga bakin rafin suka ga motar yaya Yusuf a wajen, kashe motar yaya Khalid yayi a tare suka fito suka nufi wajen da yaya Yusuf yayi parking motar sa, da mamaki suke bin motar da kallo, ga mota dai motar Yusuf ne amma baya chiki, ɗaga kai sukayi suka fara dube dube ta in da zasu ga Yusuf, amma basu ga ko mai kama da Shiba, almost 5mins suna tsaye sunyi shiru sai karan tsuntsaye da ke tashi da sautin zuban ruwa.

Chan suka hango Fahad saɓe da hiyana a saman kafaɗar sa yaya Yusuf na biye dasu a baya dukkan su sunjiƙe sharkaf ruwa sai zuba yake daga jikinsu, hiyana kuwa ko motsi bata yi, da sauri yaya Khalid da yaya Ahmad suka karisa wajen su, a hankali Fahad ya kwantar da hiyana a kasa ta gefen rafin, zuba mata ido sukayi, fiskar ta yi falau ta kara haske sosai

hannu Fahad yasa ya chire face mark dake fuskantar ta ba karamin razana sukayi da ganin yadda tayi haske sosai kamar babu jini a jiki ta, kasa kasa Fahad yace “daman haka kamannin fuskar ta yake? Ai wan nan ba in da ta bar yaya prince a kamanni, wlh tama fishi kyau” dogon tsaki yaya Khalid yaja chike da ɓachin rai ya fara magana “wai kai Fahad ta fuskar ta ma kake ko? Baka tunanin abun da Bgs ya mata bai kyau taba kashe ta fa yaso yayi ba dan Allah yasa muna nan ba” “No yaya Khalid wlh ni ina da tabbacin dan yaya prince yasan muna nan ne kuma yasan bazamu taɓa barin ta mutu ba shiyasa yayi hakan amma wlh da yasan babu kowa ba zai mata haka ba, ai shi ba mahaukaci bane, yasan me yake yi” da sauri yaya Yusuf ya karɓi zanchen da chewa “kana da gaskiya Fahad wlh idan Bgs yasan bamu nan ba zai yi kuskuren jefata chikin ruwan nan ba, tabbas yana da zuchiya kuma yana za zafin rai sosai kuma ya tsani mace amma ai shi ba mahaukaci bane ya san idan ya kuskura wani abi ya sami sister wlh Ammi zata iya tsine masa akan hakan, yana sane da duk abun da yake, inaga fa ya mata hakane domin gobe karta sake kwatan ta kashe kanta da kanta” chiki tsawa yaya Ahmad yace “dalla kuma mutane shiru koma me kusani idan da wan nan abun da yayi wa sister yazo da karan kwana da ta mutu ku ɗaga kan ku fa ku kalli daga in da ya jefota wlh idan da wata mai karamin zuchiyar ne tun kafin ta iso chikin ruwan nan zata mutu dan tsoro, than God sister iya suma tayi” chike da confidence yaya Khalid ya fara magana “kana da gaskiya Ahmad wlh ya zama dole yau mu gwadawa Bgs kuskuren sa ai dan yaga muna tsoran sa sosai ne shiyasa yake duk iskanchin da ya ga dama kuna gani fa yana jefata ya juya ya shiga mota abun sa da bamu zo da wuri bafa wlh mutuwa zatayi amma dan baku san gaskiya kun tsaya kuna wani chewa yana son gwada mata kuskuren tane, toma duk abun da sister tayi ba shi ya ja tayi ba yanzu me laifin sister da Bgs zai tsane ta saboda Allah dai ku gayawa kan ku gaskiya haka kwanaki ya zabgawa friend ɗin Aunty farida nan da take saudiya mari a gaban ɗan mijin ta,haka kuka take gaskiya ku ka che wai matan ne tayi laifi, me laifin ta dan ta masa nasiha akan ya rage zafin rai? to yau dai ko shine ya aifi zuchiya sai mun faɗa masa kuskuren sa” “yaya Khalid kai da waye zakuje faɗa masa kuskuren nasa!? Chewar yaya Ahmad yayi Maganar yana zaro manya manyan fararen idon sa ” ku mana ai ni ba zan tun kare sa ba ku zaku je” da sauri yaya Yusuf yace “wlh ban da ni sai dai Fahad” Mikewa tsaye Fahad yayi yana faɗin “kai idan kun ganni a lahira kai ni akayi me haɗina da yaya prince ba shiyasa nache muku abun da yayi, yayi dai dai ba ba wai dan yayi dai dai ɗin bane yasa nace hakan ai, kawai dan kar akai ga zanchen tun karar sane amma sai da kuka ja akazo wajen to ni kunga tafiya ta babu ruwana daku”

Tsaki yaya Khalid yaja kafin yace “to sai ka ɗauki ta mu tafi ai, duƙawa yaya Ahmad yayi yasa hannu zai ɗauke ta chikin sauri yaya Khalid yace “aa Ahmad ka bari dai Fahad ɗin ya ɗauke ta” da mamaki Ahmad ya ɗago yana kallon Khalid irin kallon nan na karin bayani nikeso “kana da gaskiya Khalid na farko ita matar Aure ce kuma koba matar Aure ba daman Fahad ɗin ne ya dace daya ɗauke ta dan shine muharraminta” chewar Yusuf yayi maganar yana kokarin wuchewa ya shiga motarsa, dawowa Fahad yayi ya ɗuƙa ya ɗauki ta chak ya saɓa ta a kafaɗar sa ya nufi motar, Yusuf

A gidan baya ya kwantar da ita san nan ya shiga gidan gaba, Yusuf ya shaga mazaunin driver, Khalid da Ahmad suka shiga nasu motar a tare suka tayar suka bar wajen suka nufi gida

Suna shiga gida tun basu gama parking ba yaya Khalid ya fito chikin sauri ya faɗa chikin gida yadda suka bar su Zahra haka ya shigo ya same su sai kuka suke, suna ganin sa suka miƙe tsaye da gudu Zahra ta nufoshi a ruɗe take tambayar ina hiyana “yaya Khalid ina Aunty Hiyana” riko kafaɗar ta yayi yace “Auta kiyi shiru sister tana lfy kinji yanzu dai ina yaya prince ya dawo ne? “Eh yana ɗakin sa” “ok to ku jirani ina zuwa yayi maganar tare da sakin ta ya nufi stair ɗin.

Ko da ya kisha ɗakin Bgs kwanche ya isko shi saman katafaren gadon sa, yana waya da Ammi shiru Khalid ya tsaya har sai da ya kammala wayar chike da ɓachin rai da jin haushi ya fara magana “yanzu dan Allah abun da kayi wa yarinyar nan ka kyau ta? Karka manta fa amana aka baka ita ai wlh kamata yayi ache kafi kowa tausayin yarinyar nan da kuma kaunar ta, saboda kasan Ammi ba abun da takeso a duniyar yanzu daya wuche ƴaƴa ɗan uwan ta ɗaya tilo, yara ba uwa ba uba sun taso chikin ukuba da wahalar rayuwa amma duk da kasan haka babu ko ɗan ɗigon tausayin su a rayuwar ka, anya Bgs kai mutun ne kuwa? Kai ni dai gaskiya na fara tantama a kan chewa kai mutun ne, koba mutun ba, to idan ma kai mutunne na fara tantama akan musulunci ka, domin duk wani chikakken musulmi yana da imani da tausayi, amma kai ko kaɗan babu,
A waje ɗaya mukayi rayuwa da kai bare nache ko zama chikin turawane yasa tausanyin ka da imanin ka suka ragu amma gaskiya ya kamata ka gyara wlh ko dan neman lahiran ka, ni ko zaka kasheni sai na faɗa maka gaskiya dan ina son ka ina kaunar ka inason mu shiga aljanna tare bayan mun mutu” dakatawa yayi da Magana yana kallon BGS da idon sa ke lumshe,

hayewa saman gadon yayi tare da ɗan bubbuga kafaɗar Bgs waro manya manyan green eyes nashi yayi kan face ɗin Khalid, chike da izza yace “au har ka gama surutun ne ai na ɗauka kwana zakayi kanayi” dunkule hannu Khalid yayi chike da jin haushi ya kaiwa Bgs naushi da sauri Bgs ya riƙe hannun sa yana faɗin “a lallai yau Khalid ka fusata sosai wai ma to me ya fusata kane? Tsaki Khalid yaja tare da gyara zaman sa a gefen Bgs dan ya lura idan mutun yace zai bi wa Bgs ta karfi tofa babu abun da zai sauya gwara subi shi ta lalama

“prince dan Allah ka rage zafin zuchiyar nan taka kaji ko? da kasa mu farinciki wlh kana yawan jefamu chikin tashin hankali da damuwa, ni nasan kana sanmu kuma nasan haka halinka yake amma pls karinƙa sassautawa dan farinchikin mu zakayi hakan” dogon numfashi yaja tare da sauƙe ajiyar zuchiya kafin yace “duk abun da ka faɗa Khalid naji from A to Z so i will try my best amma ina son kasan wani abu ni ba wai nayi niyar kashe yarinyar nan bane na mata hakane dan gobe kada tayi ganganchin kokarin kashe kanta yanzu kaga ta ɗan ɗani yadda akeji idan akazo mutuwa, gobe ba zata sake yunkurin kashe kan taba “aa prince yanzu da bamu je wajen bafa mutuwan gaske fa zatayi “ai nasan dole zakuje wajen ne shiyasa na jefata “to amma lokachin da ka jefata bakayi tunanin kafin ta isa kasa zata iya buguwa da jikin dutsen ba? “Haba Khalid ya kake min tambaya kamar ba da Brigadier General Safras kake magana bane ni da idan na kalli abu sau ɗaya to zan iya rufe ido komai nisan abu in sai ta shi in harbeshi da gun, kuma ya harbu, karka manta dukka wani wanda yake riƙe da wata mukami a chikin sojoji ko mai girman mukamin to a karkashin Brigadier General yake daga mukami na babu wani kowani soja a kasana yake to kana tunanin a banza na taka wan nan matsayin ne, na san ta yadda zan jefata, kuma idan ka lura a mun rigaku isa wajen amma ban gefata da wuriba sai da na tabbatar kun kusa isowa san nan na kefata ina faɗa maka hakan ne ba dan na kare kai na ba sai dan kuyi farinciki kuma ku dai na dangan tani da mara imani”

“eh hakane amma dai duk da hakan ka rinƙa rage zafin zuchiyar taka” “ka san me yasa na tsaya nake magana da kai Khalid? Girgiza kai Khalid yayi alamar a’a “to ina magana da kai ne dan naga yau kaɗau zafi dayawa duk chikin mu kai ne kaɗai wanda baya ɓata rai baya fushi kullun kana chikin farinciki kullun fiskar ka ɗauke da murmushi So ba zan so ganin face naka babu wan nan farin ciki ba gaskiya that why na tsaya nake maka wan nan dogon bayani amma yanzu zaka iya tafiya ka chigaba da farinchi ki” “Maganar bata kare ba ai Bgs bare kache na tafi” “ok to ina jinka saura me kuma” “me yasa kayi blocked na Aunty farida? “Wan nan bai shafeka ba Khalid tsanina da ita ne! “Ok naji bai shafeni ba amma zan rokeka wata alfatma dan girman Allah idan kamin hakan ka gama min komai aduniya” zubawa Khalid green eyes nashi yayi batare da yayi Magana ba “pls my Brigadier General dan Allah ban che ka ansa sister a matsayin mata ba ka ansheta a matsayin sister, ka dai na tsoratata ka daina daka mata tsawa pls idan ta gaishe ka karinƙa amsawa idan ta kawomaka abinci ka bari tarinka zuba maka pls wan nan alfarman kawai nake nema” “ok i will try my best, shike nan kaji daɗi? Murmushi Khalid yayi kafin yace “naji daɗi sosai shiyasa nake son ka my blood” “da kasan ka chucheni ba dole kace kana sona mana” dariya Khalid yayi ya sauka gadon ya nufi hanyar fita yana faɗin “ba wata chuta ya za’ayi na chuchi my blood ai hakan ba zai yuwu ba, ya kai karshen maganar tare da ficewa daga ɗakin ya nufi palon kasa.

Saman duguwar kujera mai zaman mutun 3 Fahad ya kwantar da hiyana dake jike sharkaf, da sauri su Zahra suka matso kusa da ita, ko motsi batayi da alama ta sha ruwa sosai, a hankali Fahad yasa hannu ya fara danna mata kan chikin ta, kaɗan kaɗan ruwa na fitowa daga bakin ta, har ya fara fita sosai kuka su Zahra suke sosai yaya Ahmad na basu hakuri, chike da jin haushi kukan nasu Fahad yace “zaku min shiru ne ko sai na kakkarya ku” tsit sukayi suna goge hawayen.

Sai da hiyana ta amayar da ruwan chikin ta gaba ɗaya san nan ta fara tari, ganin ta farfaɗo ne yasa Fahad ya chire hannun sa daga kan chikin nata ya nufi ɗakin su dan chanza kayan jikinsa. Matsowa su kayi baga ɗayan su kusa da ita har da su Yusuf dai dai lokacin yaya Khalid ya sauko kasa ya fito daga ɗakin Bgs, wajen su ya kariso suka zubawa hiyana ido.

a hankali ta waro blue eyes nata da suka sha ruwa suka koma jaa sosai, yunkurawa tayi zata mike zaune da sauri Zahra ta sa hannu ta tai maka mata suna mata sannu, kuka mai tsuma zuchiya ta fashe da shi.

zama yaya Khalid yayi kusa da ita yana rarrashin ta chikin kuka ta fara magana “yaya khalid dan Allah ka faɗamin shin kaga wani abune ajikina wadda zai sa kowa ya tsaneni duk in da naje baa sona, a kauyen mu kowa ya tsaneni a gidan Ammi, Abba da Ammi sai kai da yaya Ahmad da Aunty Zahra Aunty Farida ne kaɗai kuke sona dan Allah ni me nayiwa mutane ne kowa bai sona” “ya isa haka sister kowa yana son ki kinji ki chigaba da hakuri zaki chi riba yanzu kije kiyi wanka ku shirya kuzo muje shopping domin saya muku kaya da wasu abubuwan da zaku bukata, karki damu da kowa mujema na saya miki waya ki fita harkan kowa kiyi abun dake gaban ki kinji? Dawo da kallon sa yayi kan Zahra “auta tai maka mata ki kai ta ɗaki tayi wanka bari na ɗauko mata jallabiyar Bgs, waro ido waje hiyana tayi chike da tsoro tace “wlh bana so bana son duk wani abu da ya shafi yaya prince Allah bana son ko sake kallon face nashi a rayuwa ta” matsowa Yusuf yayi kusa da ita chikin sanyin murya ya fara magana “sister na san ke macece mai ilimin addini kuma wadda take amfani da ilimin ta kin yarda da kaddara ko ba hakaba? Dan haka kiyi hakuri ki daure ki chigaba da yakin da kika fara gaba ɗayan mun nan har da su Abba da Ammi muna bayan ki kuma muna tayaki da addu’a, ina son ki sani sarkin yawa yafi sarkin karfi bi izzinillahi taala zamuyi na sara akan Bgs, ina son ki sani gaba ɗaya mu har da su Ammi mun dora yakinin mu a kanki ne mun sa ran ata da lilinki Bgs zai iya sauyawa, kada ki watsa mana kasa a ido pls sister mun miki alkawarin kome zai faru ba zamu taɓa bari Bgs ya chutar da keba ki yar da damu ki chigaba da hakuri kina masa duk abun da ya dache a matsayin sa na mijinki kinji? Shiru tayi ta sunkuyar da kai kasa dan gaskiya ba zata iya yiwa su Yusuf musu ba ko ba komai sun gwada mata halacci kuma Yusuf shine mutun na farko da ya fara share mata hawaye a duniya bazata taɓa mantawa da kyautatawar sa agare taba, murya na rawa yaya Ahmad ya fara magana dan shi har gobe yana son hiyana kuma yana tausayin ta sosai amma ba yadda zai yi “sister ki kara hakuri kinji? karki yanke kauna da samun rahman Ubangiji kiyi abun da muka chemiki zakiyi nasara In Sha Allah” ba karamin kunya hiyana ta jiba ache yanzu kamar su yaya khalid suke rukanta abu kai yazama dole tayi musu koda hakan zai zama sanadiyar rasa rayuwanta, ɗago kanta tayi chikin nitsuwa da sanyin muraya ta fara magana “na muku alqawarin zanyi iya kokarina a matsayina na ya mace ko da kuwa hakan che zatayi sanadiyar mutuwa ta to zanyi kuma zanyi alfahari idan na mutu ina bautawa miji daga yau zan ɗaura ɗamaran yaki da jiji da kan yaya prince” har suna haɗa baki wajen faɗin “good sister Allah ya dafa miki” kasa kasa ta amsa da “Amin” “Auta tai maka mata ki kaita ɗaki sai ki dawo ki je daki kema ki shirya .

A tare suka mike gaba ɗayan su har da su amrat Lamrat kuwa tana mikewa ta fara ihu dan azaban zafin da take ji dazun ma da kyar ta iya mikewa taje ɗakin hiyana to yanzu ta manta da chiwon shiyasa ta mike da karfin ta “sisters meke damun ki? Chewar yaya khalid shiru tayi ta sunkuyar da kai kasa karisowa in da take Yusuf yayi ya duka ya saɓeta a kafadar sa ya nufi part nashi da ita yana faɗin “ai daman ke bai kamata ki bisu ba kamata yayi mu tafi ɗaki naje na miki wanka na shiryaki da kai na, kinsu da kallo Khalid yayi a zuchiyar’sa yana faɗin “kai amma gaskiya Yusuf baka da dama yanzu ka kasa hakuri kabar yar mutane ta huta, shine ka rigani lallai nima ba zan yar daba am sorry Auta gaskiya a yau ba sai gobe ba zaki karɓi bakon lamari, dan ba zan yarda Yusuf ya rigani samun baby ba” yayi nisa cikin tunanin sa sai yaji an taɓashi firgigit yayi yana kallon ta “yaya Khalid me yasa ka tsaya a nan? Wai gawa yayi yana faɗin “Auta ina Ahmad dake tsaye a nan “yaya Khalid ai lokachin da na shigo palon nan babu kowa sai kai kaɗai “ok to jeki ɗaki ina zuwa bari naje na ɗaukowa hiyana jallabiyar Bgs in kawo miki ki kai mata idan tayi wanka ta sanya” bai jira amsar taba yayi sama ya nufi ɗakin Bgs ita kuma ta wuche part nasu.

Zaune gaban mirrow ya same sa yana faman haɗa wani allaura suna video call da Aryan gefen sa yazo ya tsaya yana karewa Aryan kallo, lokachin guda yaji wani mugumugun tausayin Aryan ya kara dira masa a zuchiya gaba ɗaya Aryan ya sauya kamar ba shiba yayi baki ya rame, daga chikin wayar Aryan yace “Khalid ya Auta? Kakalo murmushi Khalid yayi yace “Auta tana lfy ya karfin jiki? “Jiki Alhamdulillah” Khalid yana son ya tambayi Aryan lbr diyana amma yana tsoron kara tayar masa da hankali dan haka sai yayi shiru

Ɗaure hannun sa Bgs yayi yana neman jijiya dan yayiwa kan sa alluran da ya haɗa “me zakayi kake ɗaure hannun ka haka ko dai baka da lfy ne? Aryan ya tambaya yana karewa Bgs kallo, shiru Bgs yayi bai tanka Aryan ba, zuba masa ido Khalid yayi yana jiran yaji amsar da zai bayar, dago alluran yayi zai yiwa kansa Aryan na ganin Alluran da Bgs ke kokarin yiwa kansa chikin sauri yace “haba Bgs bai kama ta a che har yanzu kana ɗirkawa kan ka wan nan alluraba, yanzu fa kana da mata pls my blood ka bari haka kar yaje ya taɓa lfy kafa ka rungumi matar ka kawai a wuche wajen, ɗayan hannun sa Bgs yasa ya katse Video Call ɗin tare da wurgawa Khalid harara ta chikin mirrow, juyawa Khalid yayi yana guntse dariya ya nufi dressing room nashi, bakar jallabiya ya ɗauko ya fito ya fice daga ɗakin.

 

NEW TEAM💖
💖THE TALENT TROUPE WRITER’💖

*LITTATTAFAN SUNE KAMAR HAKA*
👇👇👇👇

*1,DUK ƘARFIN IZZATA*
by(Star Lady)

*2,GIDAN AUNTY*
by(mss lee)

*3,SARKI SAMEER*
by(xeemat….love)

*4, JINI DAYA*
by(mrs bbk)

💖The Talent Troupe Writer’s 💖

*DUK ƘARFIN IZZATA*

💖Story And Written💖
⬇️
*Star lady*

Duk mai buƙatar littafin Duk Karfin Izzata daga farko har ƙarshe to yamin magana ta wan nan num ɗin 09162620621 ban da kira iya whatSapp kawai

Back to top button