Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 79

Sponsored Links

Murmushi kawai Aliyu yayi bai ce komai ba, ya dau wayarsa dake ring ya daga ya kai kunne tare da yin sallama yace “Muna hanya Dr, soon xa mu iso” ajiye wayar yayi, yana maida hankalinsa gaba daya kan driving da yake, bayan tafiya mai tsawo suka shigo wani anguwa, yayi parking dai dai wani gida, kalle kallen anguwar yake to make sure address din da aka turo masa daxu ne, ya dau wayarsa ya bude yana kallon number gidan, tada motar yayi yana driving a hankali har ya isa wani babban gida yayi parking, khadijah da ke ta kallonsa tace “Baka ma san inda xa mu ba kenan” ya kalleta ya wara manyan idonsa yana murmushi yace “Na sani mana, ba gashi mun xo ba” Dialing number Dr Ayman yayi yace “Ga mu a waje” Ba a dau lkci ba Khaleel ya fito daga babban gidan, duk a tunanin khadijah gidansa suka xo, Ya bude side din Aliyu ya basa hannu suka gaisa yana kallon khadijah yace “Good morning Madam” d’an murmushi tayi a hankali tace “Ina kwana Doctor” yace “Lafiya lau ya gida” tace “Alhmdllh” yana kallon Aliyu yace “Alryt, ku shiga ciki ni ana jirana xan wuce yanxu, sai na dawo anjima” Aliyu ya fito daga cikin motar yace “But…” Murmushi Khaleel yayi yace “You don’t worry Umma ma na ciki with Shureim” Aliyu yace “Ohk then” Daga haka Khaleel ya nufi motarsa dake waje yayi parking, Aliyu ya kalli khadijah yace “Come down Iman” bude motar tayi ta fito tana mamakin me Umma kuma ta xo yi nan tare da Shureim, ta xagayo inda yake tace “Where is this please, and why are we here?” Yana shafa kansa yace “Xumunci muka xo…” gate ya nufa ta bi bayansa har suka shiga babban gidan, a tare suke tafiyar har suka iso entrance din babban gidan, haka kawai khadijah taji gabanta na faduwa, Aliyu ya juya yana kallonta ya sakar mata murmushi yace “Gidan ku ne nan Iman, gidan yayar mahaifiyar ki” Wani kallo ta dinga masa tace “Wace mahaifiyar tawa?” Ya sauke idonsa yace “Ur late Mum” daga haka ya shiga parlorn da sallama ta bi sa da kallon mamaki, juyawa yayi ganin bata shigo ba tana tsaye bakin kofar yayi kasa da murya yace “Come in plss Iman” yana fadin haka ya juya yana kallon mutanen dake xaune parlorn, very many of them, iyaye da yara, da kyar khadijah ta iya daga kafa ta shiga parlorn abinda ya fada na sinking kanta, Wai yayar mahaifiyar ta, how is that bayan ko Umma ma bata san dangin mum dinta ba? Kan jawahir dake xaune kasa kusa da Mahaifiyarta idonta ya fara sauka, Jawahir ta yi saurin sauke idonta kasa, Khadijah ta dinga bin mutanen dake xaune parlorn da kallo har idonta ya sauka kan Umma, Shureim dake jikin wani dattijon mutum ya taho da gudu ya rungume ta yana murmushi yace “Antyna” buda ido khadijah tayi ganin Safeenah da su Deejah, Safeenah ta mike da sauri ta iso inda khadijah take tana murmushi ta rungumeta hawaye cike idonta tace “Welcome sister” murmushi kawai khadijah ta iya yi bata ce mata komai ba xuciyarta na bugawa, Safeenah ta ja ta har xuwa cikin parlon, bin bayansu Aliyu yayi ya durkusa nan gefen wani guy da baxai wuce sa ba ya gaida mutanen dake parlorn, suka amsa duk a sanyaye, gaba daya occupant din parlorn kallon khadijah kawai suke, lkci daya Mahaifiyar Jawahir ta fara kuka, jikin khadijah yayi sanyi, ta isa gun Umma ta durkusa, Umma na murmushi a hankali ta kamo hannunta tace “Greet them khadijah, iyayen ki ne nan gaba daya xaune parlorn” Hawaye ya cika idon khadijah tana sake kallon mutanen parlorn, Umma tayi kasa da murya tace “Yes daughter, they are ur families” mahaifiyar Safeenah ta mike trying hard to control her tears tace “Come over daughter, come to me” mikewa khadijah tayi ta nufeta, matar ta rungumeta hawaye na sakko mata tace “Allah ya ji kan Maryam ya yafe mata kura kurenta, you are truly a carbon copy of her daughter… Allah ya albarkace ki, mun ji dadi da Allah ya sada mu da ke tun a duniya, it’s really sad sai yanxu muke sanin ‘yar kanwarmu, jinin kanwar mu, duk da ba laifinmu bane ba haka muka so ba, amma there is always a reason behind everything, it’s great meeting you daughter” ita dai khadijah bata ce komai ba jikinta yayi sanyi sosai, Hajiya Rahmah ta xauna ta xaunar da ita kusa da ita tana share hawayen ta, jawahir dai ta kasa dago kanta ganin yanda mahaifiyar ta ke kuka yasa ita ma hawaye ya dinga xuba idonta, sai dai duk kukan mahaifiyar jawahir bai kai na mahaifiyar Maimoon ba immediate din Mum din khadijah, kuka take kamar a lokacin taji mutuwar kanwartata, komai ya dawo mata sabo, a karo na farko Alhaji Abbakar mahaifinsu Safeenah kuma babban yayansu late mahaifiyar khadijah gaba daya… yyi gyaran murya ya bude wajen da addu’a, yana murmushi yace “Alhamdulillah for the gift of life, Alhmdllh for a day like this, Alhmdllh for everything… Sure it’s a privilege meeting with our daughter again after so many years…” kallon Khadijah yayi yace “Come over dear” Tashi tayi daga kusa da Umman su Safeenah ta dawo kusa da shi a sanyaye ta xauna kasa, da farko kasa cewa komai yayi kuma hakan na da nasaba da kamannin khadijah na mahaifiyar ta, bayan wani lkci yayi karfin halin yin murmushi yace “Khadijah kina yar shekara biyu rabon mu dake, sai yanxu bayan shekara ashirin Allah ya sake hada mu, kwarai kuwa babu wanda kika sani cikin mu kamar yanda mu ma bamu san ki ba, da xa mu hadu a hanya sai dai ki wuce mu wuce, which is a great shame” ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba, nuna mata sauran maxan da ke parlorn su kusan uku xaune kusa da shi yayi da wanda yake kan one seater yace “Kin ga wa en nan gaba daya” ta daga kai a hankali tana kallonsu gaba daya, yace “Duk iyayen ki ne khadijah, they are all ur parent, and they are all here because of you, duk mun bar abubuwan da muke muka taho daga garruwa daban daban domin ki, gaba daya nan da kika ganmu yayyin marigayiya Maryam ne, mahaifiyar ki, ke din mai gata ce khadijah, kina da gatan ki” cikin rawar murya tace “Toh me yasa ni ban san ku ba, me yasa ba a nuna min ku ba, me yasa ba ku nemeni ba” tana fadin haka ta hade kai da kujera tana kuka sosai, Ya dafata cikin sanyi yace “Mahaifin ki Allah ya masa rahama shi ya raba mu da ke tun bayan rasuwar mahaifiyar ki khadijah, mun so rike ki ganin ba shi da yan uwa mata, amma sai yayi tunanin rabasa da ke muke son yi, Allah ya gafarta masa, mun samu matsala a kan hakan da shi, which contributed to his keeping u away from us for many years, a Abuja suka xauna da mahaifiyar ki, bayan rasuwar ta ne ya siyar da gidansa na Abuja ya dawo kano without even our knowledge, kin ji dalilin da yasa baki san mu ba khadijah, Kuma da mun san inda familyn mahaifin ki suke da babu abinda xai hana mu xuwa gare ki, sai dai yau ta dalilin mijin jawahir mun yi reuniting da ke….” Khadijah bata dago kanta ba hawaye na ta xuba idonta, Alhaji Usman yace “Wannan baiwar Allah da ta rike ki bisa amana tamkar yar da ta haifa cikinta Allah ya saka mata da gidan aljanna…. Mun ji duk kalubalen da kika fuskanta a rayuwa saboda maraici, bayin Allahn da suka tsaya maki through all the hardship Allah ya biya su da aljanna, it’s really sad daughter, don kina da gatan ki, Amma ba komai haka Allah ya kaddara, Allah ya jin kan iyayen ki ya gafarta masa, ya kuma raya maki yaron ki, ya albarkace auren ki…. In sha Allah gatan da baki samu ba da yarintar ki xaki samu da girman ki, we will always be there for you daughter, uwar mu daya ubanmu daya da Mahaifiyar ki… Allah ya ji kanta” Khadijah ta dago tana share idonta a hankali tace “Ameen, nagode Abba” Gaba daya sai da aka mata introducing din cousins dinta da niece a parlorn, yawanci duk suna yanayi barin da matan, Safeenah da Maimoon kuwa kamanninsu ba a magana dama, har sannan Jawahir ta ki dago kanta daga karshe ma wucewa sama tayi, it was really a happy day for Khadijah jin ta cikin yan uwanta gaba daya, kuma a ranan ta fara ganin hoton mahaifiyar ta, bata taba sanin haka relatives ke da dadi ba sai ranan, da tun farko tasan da su tasan baxata wahala a rayuwa ba but that’s her fate and she is happy with it, Aliyu bai jima gidan ba ya wuce ya bar ta, Umma kuma sai kusan azahar ta wuce ta bar Shureim ma gidan, Khadijah na daki tare da su Safeenah da deeja dake ta labari tayi tagumi tana kallonsu tana murmushi jawahir ta shigo dakin, suna hada ido ta sunkuyar da kai a hankali tace “Khadijah ki xo ku gaisa da Doctor xa mu wuce yanxu” Mikewa khadijah tayi tace “Toh” ta dau hijab tace ma su Safeenah tana xuwa sannan ta fita, Dr Ayman na xaune parlor tare da Shureim dake jikinsa ta shigo tana kallonsa murmushi dauke fuskarta tace “Ina yini Doctor” murmushin ya mayar mata yace “Alhmdllh khadijah” ta isa har gefensa ta xauna a kasa tana kallonsa cikin sanyi tace “I am very happy for ur effort in uniting me with my relatives doctor, Allah ya saka da alkhairi, I will never forget you in my life…” Kasa ci gaba tayi ta sunkuyar da kai hawaye na sakko mata, ya dinga kallonta a sanyaye, ta dago da kyar bayan ta goge idonta don bata son Shureim ya gani tana dubansa tace “This is among the greatest thing that have ever happened too me doctor, I really owe both you and Barrister, Kun haskaka min rayuwata kun taimakeni a lokacin da nake bukatan hakan, I don’t know how to pay you both” ya d’an yi murmushi yace “May be that was why God brought you into my life, just to unite you with ur late mum’s family, There is always a reason for everything you knw… Don haka kawai ki gode Allah ba ni ba” Kai ta gyada masa tana share hawayen da ya ki tsaya mata, ita dai jawahir na tsaye gefe a sanyaye bata ce komai ba, yace “Amma nan xaki kwana yau koh” A hankali tace “Ban sani ba tukun” yace “Alryt then, mu xa mu koma yanxu, and in sha Allah gobe xa mu koma Uk” ta kallesa a sanyaye tace “Toh Allah ya kai ku lafiya” mikewa yayi ya daga Shureim dake kallo yace “Sweetheart xa mu tafi yanxu je wajen Anty” ya bata fuska yace “Uncle ni xan bika plss” jawosa khadijah tayi tace “A’a xa su je da nisa” kuka ya fara yi ya koma gun Khaleel yace “Uncle plss” sai a sannan jawahir tace “Mu tafi da shi mana don Allah” Khaleel ya kalleta sannan ya kalli khadijah yace “Can we?” Shiru ta d’an yi sai Kuma a hankali tace “But his…” Sai kuma tayi shiru, Khaleel na murmushi yace “His dad bai sani ba koh?” kasa cewa komai tayi kuma bata dago ba, yace “Toh kira sa ki gaya masa nasan baxai hana ba” ba musu ta dau wayarta dake jikinta ta shiga kiran Aliyu, bayan wani lkci ya daga yace “Iman…” Tace “Wai Dr Ayman xa su tafi da shureim can they?” Murmushi Aliyu yayi yace “Sure” tace “Toh” daga haka ta katse wayar tana kallon Khaleel tace “Yace toh” Murmushi Khaleel yayi yace “Alryt then, sai mun hade a uk, sai ki gaya ma grandparents dinsa mun tafi da shi, I mean all his grannies cos he have a lot…” daga haka ya dau Shureim dake murmushi yana daga mata hannu suka fita da jawahir dake bin su a baya don ta sallami iyayenta, khadijah ta bi su da kallo har suka fita, kafin tayi murmushi ta mike a hankali ta wuce sama…..

Back to top button