Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 81

Sponsored Links

Da asuba khadijah na jin Aliyu ya fita masallaci ta mike xaune a hankali, gabanta ne ya dinga faduwa from experience, duk da dai wannan karan ko ciwon kai bata ji ba balle na jiki amma tsoro ne fal xuciyarta, ganin lkci na wucewa ta mike cike da karfin hali, the pain wasn’t as much as she was expecting… Ta lallaba ta fita dakin ta koma nata ta sa makulli, wanka ta fara yi ta dauro alwala ta fito, tana ta xaune kan darduma tana azkar bayan ta idar taji an murda kofa, kallon kofar tayi sai dai bata motsa daga inda take ba, a hankali yayi knocking yace “Iman, are you alryt…” Shiru tayi bata ce komai ba, tana ji ya bude kofar dakinsa ya shiga, bayan wani lkci ya fito, hade kai tayi da gwiwa jin yana bude kofarta da makulli, bayan ya bude ya tsaya daga bakin kofa yana kallonta, a hankali ya karasa dakin ya duka kusa da ita xai dago kanta ta ki yarda, da damuwa yace “Look at me plss Iman, are you okay…” ganin ba yarda xata yi ta dago ba ya mike ya dagota, ihu ta fasa masa ta boye fuskarta jikinsa tace “Ni dai bana soo” Dariya ta basa yana rungume da ita yace “Meye baki so Ummu Shureim” a hankali tace “Ka fita” murya can kasa yace “Kunya ta kike ji?” Kai ta gyada masa a hankali, sosai ta basa dariya ya nufi gadonta da ita, ya kwantar da ita ta rufe fuskarta da pillow, Xaunawa yayi gefenta yana murmushi yace “Sai ma mun yi wanka tare anjima xaki san meye kunya” Bata san lokacin da ta dago ba ta xaro ido tana kallonsa tace “What???” Sai kuma ta maida kanta da sauri tana murmushi wai ita kunya…. Wani salon soyayya na daban Aliyu ya dinga gwada ma Iman kamar xai maida ta ciki, ko da yaushe suna manne da juna, Khadijah bata taba tunanin haka Aliyu yake ba shi da kunya ko na taro ba, idan aka ce mata xai iya abinda yake mata baxata yarda ba, coz he look so innocent in the face, tun tana kunya tana noke masa har daga karshe tayi give up ita ma a gidan ta sakar masa kanta, gida ya koma kamar na India, kunyan da take ma da daddare shi ma duk ta ajiye sa gefe amma fa cikin duhu, ita kanta bata taba sanin tana da soft spot ma Aliyu ba sai a yanxu, har ranta take jin sa, sannan ko na minti daya bata son ya bar ta duk inda xa su tare suke xuwa. Ranan da suka cika sati biyu gidan tana kwance jikinsa a parlor yana operating laptop, a hankali tace “Abban shureim…” Yana kallonta yayi pecking cheeks dinta yace “Ummu Shureim” ta turo baki tace “kaga mun koma makaranta fa” yace “I thought as much, dama in two days time xa mu koma can ai” Tace “Toh Allah ya kai mu” yana shafa fuskarta yace “Ameen baby” a ranan suka tafi yi ma Mumy sallama da yamma, Khadijah na xaune tare da Baby a dakinta taga Barrister ya kirata yayi sau uku, ita dai bata ce mata komai ba, amma sai suka bata dariya, karfe biyar saura suka shiga dakin Mumy xa su mata sallama don har gidan Umma da umman su jawahir xa su je, Mumy tace “Toh Allah ya kai ku lafiya, ya kiyaye hanya” Khadijah dake durkushe kusa da ita tace “Ameen Mumy” Mumy tace “Toh sai kun dawo biki nan da few months” Aliyu yace “Wani bikin Mumy” sai da Mumy ta fara dariya sannan tace “Na kanwar ka mana” Khadijah tace “Mumy baby?” Mumy tace “Ehh” xaro ido tayi tace “Lahh Mumy ba mu sani ba” Aliyu ya xauna yace “Mumy da Ahmad din?” Mumy tayi murmushi tace “Wannan bada ta kawai Abban ku yayi, ba Ahmad bane, an basa hakuri shi” Aliyu ya d’an hade rai yace “Bada ta kuma? To who?” Mumy tace “Barrister Aliyu” da khadijah ta fara dariya sai da Mumy da Aliyu suka tsaya kallonta, ta mike da sauri ta fita xuwa dakin baby tace “Wato abun har da munafurci koh Baby, ni din ne baxa ki gaya ma ba koh?” Baby tayi murmushi don tasan kwanan xancen, a hankali tace “Shi yace ba sai na gaya maki ba, xai je har gida as a mother ya same ki ya gaya maki” khadijah na murmushi tace “Am soo happy wllh, Allah ya sanya alkhairi, ya nuna mana lokacin lafiya” Har bakin mota baby ta raka su, suka wuce gidan Umma, bayan Umma sun gaisa da Aliyu ta bi bayan khadijah da ta wuce ciki, Ganin yanda tayi kyau ta cicciko Ummu tayi murmushi tace “Ko ke fa da kika kwantar da hankalin ki daughter” murmushi kawai khadijah tayi ta sunkuyar da kanta, Umma ta xauna kusa da ita tace “In ji dai ba matsala?” Khadijah tace “Babu Umma dama sallama muka xo maki xa mu tafi can Uk” Umma tace “Maa Sha Allah, ai hutun ya kare, Allah ya kai ku lafiya my daughter” Khadijah tace “Ameen Ummata” Umma tace “Amma ku je har Umman su jawahir ku yi mata sallama” khadijah tace “Eh dama xa mu je Umma” Umma tace “Toh hakan na da kyau, kin san kawun ki yana yawan kira mu gaisa” Khadijah ta kalleta da sauri tace “Abbansu Safeenah?” Umma tace “A’a ba shi ba, mai bi masa” xaro ido khadijah tayi sai kuma tayi dariya tace “Umma Abban su Maimoon ne, dama umman su ta rasu 3 years back suka gaya min” Umma tace “Toh ya aka yi don Umman su ta rasu, Allah ya ji kanta” Dariya kawai khadijah take, Umma dai sai kallonta take, can ta turo baki tace “Umma ni dai don Allah kar ki ce masa A’a” buda ido Umma tayi, sai tayi dariya tace “Amma baki da kunya yarinyar nan” Khadijah ta mike ta fita tana dariya, minti talatin suka yi a gidan, xa su wuce umma ta ja khadijah xuwa daki tace “Daughter, ya kamata ku je can katsina da Aliyu ki gaida yayan Mahaifin ki” shiru khadijah tayi da farko, sai kuma a hankali tace “Toh Umma xa mu je” Umma tace “Good, Allah ya kiyaye hanya, ki kula da mijin ki fiye da yanda xa ki iya, ki kuma rike tsaftar ki don nasan kina da ita, Allah ya maki albarka” khadijah na murmushi tace “Ameen Umma” da haka suka bar gidan suka dau hanyar gidansu jawahir, can ma basu dade ba bayan sun yi ma Umman jawahir sallama suka koma gida. Da daddare ganin Aliyu xai takurata ta dinga turo baki tana kwace kanta jikinsa, ya kai bakinsa kunnenta murya can kasa yace “Baki son mu tafi da babynmu daga nan Iman” ta marairaice masa tace “Ni dai ka kyaleni bacci nake ji” yace “Plss” kukan shagwaba ta fara masa wanda hakan ya rikita sa, bai kyaleta ba sai da yaga ta fara bacci da gaske, ya fi awa daya kankame da ita, ko da yaushe jin abarsa yake intact, murmushi yayi ya manna mata kiss a lips daga karshe ya kwantar da ita ya shiga bathroom. Washegari suna breakfast tana kallonsa tace “Abban Shureim, Ina son mu je katsina mu gaida Uncle dina” ya kalleta yace “When, Kin san gobe da safe xa mu wuce” Tace “Toh idan mun dawo bikin su baby sai mu je?” Yace “A’a idan kin ce mu je yanxu ma sai mu je ai” ta langwabar da kai a hankali tace “Mu je plss” yace “Alryt then” karfe sha daya suka bar gidan, suka dau flight xuwa kano, daga can yayi masu charter na taxi da xai kai su har kt, tun da suka shigo kt misalin karfe daya da rabi na rana gaban khadijah ke ta faduwa, taxin ya ajiye su dai dai gidan kawunta, ita kanta tayi mamakin yanda ta gane gidan, Aliyu ya fito ita ma ta fito tana kallonsa tace “Mu shiga” Bin bayanta yayi suka shiga gidan, Babu kowa compound din da ya xama wani iri kamar gidan da yayi shekara hamsin, Har parlor ta isa da sallama Aliyu ya tsaya daga bayanta, kallon kawun nata dake xaune k’asa a one side of the parlor yana fama da ciwon kafa sosai tayi, ta kalli Hajiya maimuna da ta fito kitchen jin sallama ta gaisheta a sanyaye, daga ita har yaran dake parlorn kallonta suka dinga yi kamar basu santa ba, ita dai tasan basu gane ta bane, Ta isa har kusa da ita a hankali tace “Mama Khadijah ce” bude baki Hajiya Maimuna tayi tana kallonta da wani irin mamaki, Khadijah ta sauke idonta kasa, ba ita ba har kawu Jibril shi ma bude baki yyi lkci daya hanjin cikinsa ya kada don kullum da threat din Barrister Sudais yake kwana yake tashi, Aliyu ya xauna kusa da shi yace “Ina yini kawu?” Kawu ya kallesa yana maxurai yace “Lafiya lau daga ina, wa ku ke nema” Aliyu yayi kasa da murya yace “Ni ne mijin khadijah, mun xo gaishe ku ne kawai kawu” da sauri yace “Toh madalla… Gaisuwa ce kawai koh” Aliyu ya gyada masa kai yace “Eh kawu” khadijah ta karaso har gabansa ta durkusa kanta a kasa tace “Ina yini kawu?” Yace “Lafiya lau” Kai kana ganin yanda yake maxurai kasan duk a tsorace yake, Aliyu yayi murmushi yace “Ka kwantar da hankalin ka kawu, xumunci kawai ta sa ni in kawo ta tayi” Yana gyada Kai kamar kadangare yace “Madallah” Khadijah dai ta kasa cewa komai, bata taba xaton ganin Kawunta da iyalensa a halin da ta samesu ba, ganin gaba daya mutumin is uncomfortable Aliyu yace “Kawu xa mu koma yanxu, don gobe da safe xa mu wuce uk shine tace in kawo ta…” Kawu ya kasa kallon khadijah sai gyada kai yake yana cewa Madallah Kamar xararre, Dubu hamsin Aliyu ya ajiye gabansa, Kawu ya dauka yana kallonsa, lkci daya idanuwansa suka kada yace “Maa sha Allah, nagode nagode nagode Allah yayi albarka” Aliyu yace “Ameen” a sanyaye Khadijah tace “Allah ya baka lafiya kawu” hawaye ta gani idonsa amma yana ta boyewa bai son su gani yace “Toh Amin, sai a yayyafe….” murmushin karfin hali tayi tace “Nima ku yafe min kawu, Allah ya yafe mana baki daya” hatta Maimuna sai da tace da khadijah a yayyafe da xasu wuce, ganin bata ga kishiyarta ba tace “Mama Ina mamansu Usman?” Maimuna tace “Ta amshi takardar ta ta wuce kusan shekara kenan” khadijah bata ce komai ba duk jikinta yayi sanyi har suka bar gidan xuwa inda xa su samu mota xuwa kano. Sai bayan la’asar suka shigo kano, Khadijah sai bata fuska take irin ita ta gaji din nan, ya langwabar da kai yace “Toh ai we still have 3 more hours journey kike bata fuska madam” ta xaro ido tana kallonsa tace “Ni dai na gaji wllh” murmushi yayi yace “Just reserve this comment, xa su maki amfani anjima idan mun isa gida da daddare” Kallonsa kawai take kamar mai son gane ma’anar abinda yace, can tace “Kamar ya?” instructing din mai adai daitan da ya tsayar masu yyi yace “Airport xa ka kai mu” Khadijah ta turo baki ta shiga shima ya shiga yana matsa cinyarta a hankali, tayi kara tana kallonsa, dauke kai yayi da sauri yana murmushi, har suka isa airport idonsa na kan wayarsa da yake dannawa, ya siyar masu tickets na kaduna, hudu da rabi jirgin ya tashi, cikin few minutes suka sauka kaduna. A gajiye ta shiga parlor ta wuce dakinta direct ta fada kan gado, bayan kusan minti biyar ya bude kofar dakin yana kallonta yace “Sallahn fa?” Kallonsa tayi a hankali tace “Xan yi” yace “Toh tashi kiyi” Sai da ya idar da sllhn shi ma sannan ya fita eatry siyo masu abinci, yana dawowa ya shigo dakinta, xaune ya sameta kan darduma yace “Come down mu ci abinci” Tace “Sai na fara wanka” yace “Toh jira ni in xo muyi” mikewa tayi da sauri ta shige bathroom din ta sa makulli, yana dariya ya juya ya fita dakin. Karfe goma na dare tana kwance parlor kan 3 seater har bacci ya dauketa taji an dauketa kamar baby, ta bude ido a hankali tana kallonsa, ya manna mata kiss a lips dinta ya shiga bedroom dinsa ya kwantar da ita saman gado, ya kwanta shi ma ya shige jikinta… Kamar xata yi kuka tace “Bacci fa nake ji” yayi kasa da murya yace “Wai baki son mu tafi da tsaraban baby mai kama da ke UK ne?” Hararansa tayi ta juya masa baya tana turo baki, ya marairaice mata yace “Plsss Ummu Shureim” kukan shagwaba ta fara masa as usual, nan ta kara rikitar da shi, ita ma dai kamar jira take ta bada kai bori ya hau, they couldn’t just get enough of each other, ta kankamesa kamar xata koma jikinsa su xama daya, ya kai bakinsa kunnenta cikin sanyin murya yace “I love you Iman…” Shiru tayi idonta a lumshe, bayan wani lokaci ta kwanta kan kirjinsa a hankali tace “I love you more Abu Shureim” kissing dinta ya shiga yi, and that really turn her on. Da asuba tare suka yi wanka ya ja su sallah a dakin, a hankali ta dawo kusa da shi ta durkusa murya can kasa tace “Good morning Abu Shureim” ya jawota jikinsa yace “Morning Ummu Shureim….” Murmushi tayi tace “I am missing him” yace “You better don’t, shi din me iyaye ne da yawa, so kar ma ki wani sa shi a rai” shiru tayi bata ce komai ba, yace “Ki hada abubuwan da kika san xa ki bukata, anjima xa mu wuce airport” tace “But I have everything back there, a can gidana…” Kallonta ya dinga yi kafin yyi murmushi yace “Kina tunanin xan je gidan ki in xauna wife?” Shiru tayi tana kallonsa, yyi yar dariya yace “Lallai, I rather rent a new flat, balle ma muna da apartment can din, kawai I prefer staying a gun aunt dina ne saboda kadaici” murmushi tayi bata dai ce komai ba, sai dai ita ma hakan ya mata, coz she don’t think xata iya xama gida daya da su Khaleel, it’s just not possible, lakutan hancinta yyi yace “Kin fi son can ne saboda yar uwar ki” da sauri tace “Not at all, ur wish is my command sir….” Rungume ta yayi yace “That’s sweet of you baby”

A year and a half later….

Tun da khadijah ta tashi yau take ta girke girke iri iri duk da xaxxabin da ta dinga yi kwana biyu da suka wuce, kana ganinta ka ga mai karamin ciki, yanxun ma daurewa take girkin da take yi, don aroma din na hawa mata kai but she have no option, Aliyu ne ya shigo kitchen din yana rungume da little Fatima, yarinya da baxata wuce shekara daya da few months ba, she is just a duplicate of her mother, babu inda ta bar khadijah, kyakkyawa ce ta karshe yarinyar, Khadijah ta kallesu tace “Dear kasan yanxu xata ce sai na dauketa kuma ni ba taya ni aiki xaka yi ba” Yar dariya yayi yace “Tsoro nake kar in fita da ita tayi ta min ihu a mota, xan je airport dauko Umma, same flight kuma suka bi da su Baby” Khadijah tace “Lahh da gaske?” Yace “Sure, Aryan ma ba yarda xai yi ya bi ni ba da sai mu tafi tare da su…” Tace “Ae tun daxu na gane gida yake son wucewa ya gaji da mu” dariya Aliyu yyi yace “Aa miskilanci ne kawai, ya ki yarda in dauke sa ma” Ta dauraye hannunta ta amshi Noor ta mana masa kiss a lips dinsa tace “Toh Allah ya tsare babyna….” Yace “Uhn you are looking for trouble koh” yar dariya tayi ta kashe masa ido tace “Don ma ban maka french one ba” Ya wara ido yace “Toh mu je daki ki min” ta hararesa tace “Naki wayon” juyawa yayi ya fita yana murmushi, yau ranan farin ciki ne gareta don a ranan xata sama qualified pharmacist, a ranan xa ayi convocating din su, kafin Aliyu su shigo gidan ta gama komai tana jiran Ummarta da yanxu take auren yayan mahaifiyarta wato dad din su Maimoon, tare da Baby uwar gida ga Barrister Sudais, fitowa parlor tayi jin shirun Aryan yayi yawa, xaune ta ga little balaraben kan kujera kiris yake jira ya fara kuka, ta karasa gun sa tana murmushi ta ajiye Noor, ta daukesa ta rungumesa tace “Haba sweetheart, in dafa maka indomie xaka ci?” Kitchen ta koma tana rike da shi ta daura ruwan indomie sanin abinda yake ci kenan, tana tsaye har ya dahu ta juye a plate ta dawo parlor ta xaunar da shi ita ma ta xauna ta shiga basa, Babu inda ya bar ubansa tun daga kyau har gashin kansa, hatta idonsa irin na babansa ne, murmushi tayi tana ci gaba da ba sa indomien yana ci, tana gama basa ta wuce daki da shi ta sauya masa kayan jikinsa duk da ba su yi komai ba ta dauko masa favourite toy dinsa ta basa ya amsa ta kunna masa cartoon ta xaunar da shi kusa da Noor da ta kwanta kan kujera, sannan ta shiga daki don yin wanka, tana shiryawa bayan ta fito ta ji shigowar mota, ta gama saka kayan da sauri ta fito, Aryan na ganin xata fita ya sauka saman kujera xai fara kuka, ganin haka ta dawo ta daukesa, Noor ta fashe da kuka ita ma, dariya tayi ta dauketa ita ma, tana rike da su ta fita compound, tsaye tayi tana murmushi ganin motar Khaleel ne, jawahir ta fito daga motar, Aryan na ganinta ya fara murna, khadijah ta saukesa yaje da gudu ya rungume uwarsa ta daga sa tana dariya tace “Kai lallai khadijah, dubi yanda kika maida min yaro kato, wani irin abinci kike basa haka” dariya khadijah tayi tace “Bayan ma ya rame, duk kwanan nan a dole yake xaune gidan, naga alamar kewar ki yake” Khaleel ya fito daga mota yana murmushi ya nufo ta yace “Oum shureim good morning” tana murmushi ita ma tace “Morning doctor….” ya amshi Noor yana shafa dogon gashinta idonsa a kan khadijah yace “Congrat once more, Allah ya sanya alkhairi, our pharmacist…” Tace “Ameen Thumma Ameen, thanks much Abu Aryan” Bata rufe baki ba motar Aliyu ya shigo gidan, Baby ce ta fara fitowa daga motar tare da little Amira, khadijah ta wara ido tana kallonsu ta nufe su da sauri, Barrister Sudais ya fito daga gaban motar with Shureim, sannan Umma da ta fito ita ma rike da little Farouq yaron da baxai wuce wata bakwai ba da baby take goyo, khadijah ta rungume baby cike da murnan ganinta suka dinga babbaka dariya, lkci daya ta tafi gun Ummarta ta rungume ta ita ma, tsabar murna ta kasa cewa komai, ta rasa me xata ce, tana sake Umma ta daga handsome yaronta sama ta rungume sa ya dinga kissing fuskarta very happy seeing her….. Aliyu ya fito ya jingina da mota ya rungume hannunsa yana kallonsu, Kamar yanda Barrister Aliyu da Dr Ayman ke kallonsu suna murmushi su ma….

 

*ALHAMDULILLAH*

A nan na sauke littafina mai taken *Noor-Al-Hayat* kurakuren da nayi a ciki Allah ubangiji ya yafe min….👏🏻 Darussukan dake ciki Allah yasa mu amfana da su Amin. Ina mika sakon gaisuwata xuwa ga mahaifiyata Hajiya Hajarah… She is my first love, my role model, my momma, my world, my everything… Allah bar min ke Hajjaju Yaya❤ My sweet Anty Didi ur daughter Jiddo is greeting with respect, tnx for being there for me during this book, Allah ya raya su Aneesah… And my second role model Anty Rukaiyya…😍 am so grateful for the encouragement from the beginning of this novel till the end, I always gat ur back small mum ur daughter Khaleesat Haiydar is saying a big thank you, Allah bar mu tare ya raya Little Khaleesat Haiydar, Baby and Jaheed…
Na sadaukar da littafin *Noor-Al-Hayat* xuwa ga lovely sister na, my Blood… Khadijah M Bello (Amira/Baby) nd my sweet cousin like no other Khadijah Sadi Yusuf (Baby) Allah ya albarkace rayuwar ku ya raya mani ku bisa imani, ya baku ilimi mai albarka da amfani. Sakon gaisuwa ta na musamman xuwa ga wa enda for sure ba siyan littafin Noorul Hayat suka yi ba, ihisani kawai suka min, duk ina sane da ku kuma na so contacting din ku but I lost my contacts, ban san ya xan yi in same ku ba, Amma ku sani I will for ever be grateful, Allah ya biya maku bukatun ku na alkhairi duniya da lahira, nagode nagode…. And finally my fans, ban taba xaton yea da gaske I have fans ba sai a littafin nan, you guys really patronized me fiye da tunani na, you all made me feel loved😥 words alone can’t express how happy I am, ku sani… Billah Khaleesat na ji da ku har ranta, Ina son ku, Ina alfahari da ku, Ina maku fatan alkahiri, Ina maku fatan rabuwa da iyayen ku lafiya, Ina maku fatan daukaka, Ina maku fatan gamawa da duniya lafiya, ina maku fatan samun aljanna, I wish you all the very very very best in life, nagode nagode nagode… Allah ya sa mu cika da imani ya yafe mana kura kuran mu…👏🏻

Taku har kullum Hauwa Bello Jiddah (Khaleesat Haiydar) 📚✍🏻

Thanks once more for patronizing my book fans… For those still wanting to buy the complete document it’s just 300 Via transfer 👉🏻 3276052019 Hauwa Jiddah Bello, fcmb.

07087865788.

Back to top button