Hausa NovelsSakayyah Book 2 Complete

Sakayyah Book 2 Page 30

Sponsored Links

*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH book 2… Page 30*

 

         Na

*Aysha Aliyu Garkuwa*

 

*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

 

_Ina kuke Ma’aurata masu sha’awar ganin sun zama taurari
kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen
gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau’ikan sirrin sahihan
magungunan ma’aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta
dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki
ki zamto tauraruwa a idanun mijinki…Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_
:_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin
ilanwaddihi, Gumbar da ba’a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin
al’khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar
ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace
mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni’ima yanada abubuwa
masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa
jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni’imantaccen damshi,
Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi
sadidan, da dai sauransu…Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu’umin ƙamshi
wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba…._  _Shin ko kina da labarin Miskilinci da
ƙasaitar Rayyan  Naaan amma lokaci ɗaya
ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face
sirrinkan gyara da kuma shu’uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu
Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar
bawa_

_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta
zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)…Tabbas Mahmud ya zamto
zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi
da budurwa(Namiji  Baya Kaɗan) ko kinsan
hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu’uman humran Aysha
Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke
dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta
yake tamkar budurwa ‘yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da
Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta
da kuma Ma’aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba’a iya rubutun littafi
ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma’aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun
abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 08069423567 muna iya
tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah ‘yar uwa
idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci…._

🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo.
sayan na gari maida kuɗi gida,

 

 

Abun ya zomata abazata da kuma Mamaki sosai take mamakin
wasu abubuwan da yake mata ahankali ta ɗago Manyan Idanunta masu haske ta
kallesa ganin yadda ya tsare fuska babu alamar wasa atare dashi yasa ta kawar
da kanta.

Cikin tsare fuska yace “buɗe bakin ki”.

Jin yanda yayi magana da kuma yanda fuskarsa ke tsuke yasa
ta buɗe bakinta yasa mata ahankali take tauna tana juya tsokan a bakinta, ido
ya zuba mata har ta cinye wani ya ɗauka ya sake samata ta kuma amsa tana
jujjuyashi kusan one minute kafin ta haɗiye.

Ba tare da ya kalleta ba ya kuma ɗauko wani ya muƙa mata, a
hankali ta  riƙe hannunsa tace.

“To kaima kaci mana”.

Yana ƙoƙarin cire hannunsa dake cikinta yace.

“Me ruwanki cikin ki ko cikina?

aina fiki sanin wahalar cikina ke kici mana”.

Langwaɓar da kai tayi tare da cewa.

“Ni na ƙoshi bana jin yunwa ya isheni haka”.

Fuska ya kuma tsukewa tare da faɗin.

“Sai kinci fa”.

Ya faɗa tare da kai mata bakinta aransa kuwa mamaki yake
yana da tabbaci ita ko ciwo take tana cin abinci amma kuma yau tunda gari ya
waye bataci komai ba ya fahimci hakan baya rasa dalili da tafiyarsu Ummi data
sa aranta ne.

 

Ɗagowa yayi ya kalleta kana yace.

“Tunda gari ya waye bakici komai ba sai kuka da kika tayi
sannan yanzu ma Still Kice min zaki kwanta da yunwa ya za’a yi na yarda? ki
kwanta da yunwa ai yunwar sai ta cutar dake nima ta cutar dani”.

Fuska a narke ta kallesa sai kuma ta langwaɓar da kai tana
cewa.

“To ai bana jin yunwa aƙoshe nake”.

Zamansa ya gyara da faɗin.

“Sai kinci fa ki buɗe baki”.

Bai jira cewartaba ya ɗauko wani tsoka mai laushi yasa mata
abaki lumshe idanunta tayi kafin ta fara tauna ahankali ahaka yaci gaba da bata
taci ɗan dai-dai bada yawa ba.

 

Wata tsokan ya sake ɗauka yakai mata baki tayi saurin
girgiza masa kai tana rau-rau da idanu tace.

“Allah banaso Wallahi na ƙoshi”.

Cikin tsira mata a ya girgiza kai tare da cewa.

“Baki ƙoshi ba”.

Idanunta dake lumshe ta ware tace.

“Allah nikam na ƙoshi cikina ya cika”.

Numfashi ya fesar tare da faɗin.

“Inga cikin?”.

Baki ta tura tare da faɗin.

“To ai ya ƙoshi sai ka gani ne?”.

Kai ya jinjina kana yace.

“Um idan kina so in yarda cikin ya ƙoshi tona ga cikin”.

Ya ƙare maganar yana kallon dogon rigar Abayar dake jikinta
wanda daga ƙasa abuɗe yake daga sama kuma atsuke cikin tura baki tace.

“Ba gashi ba ka gani”.

Tayi maganar batare data ɗaga rigar ba.

 

Idanunsa ya lumshe kana ya buɗe akanta yace.

“Ɗaga rigar na gani”.

Ware ido  tayi sai
kuma ta sake langwaɓar da kai tace.

“In ɗaga riga kuma?”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa

“Eh idan kin tabbatar ɗaga in gani”.

 

Ahankali ta ɗan matsa kana ta fara tattare rigan idanunta
akansa tace.

“Toh ba gashi ba”.

Lumsassun Idanunsa ya zubawa santala-santalan cinyoyinta
dake cikin wani farin skintied kafin ahankali ya maida idanunsa kan cikinta
dake lafe tabbas bata ƙoshi ba kamar yanda yake zato amma ya rasa dalilin da
yasa batason cin abinci.

Ahankali ya matsa gefenta kana ya daura hannunsa na dama kan
cikinta ya shafa a hankali ya cusa ya tsansa cikin ramin cibiyar.

Cikin sauƙe numfashi ta lumshe idanunta tare da sakin ajiyar
zuciya cikin wata sanyayyar murya ta motsa laɓɓanta tare da cewa.

“Kaji na ƙoshi ko?”.

Sanyayyan ajiyar zuciya ya sauke tare da girgiza mata kai
kana yace.

“Um-um baki ƙoshi ba, Baki ƙoshi bafa, Baki ƙoshi ba, Baki
ƙoshi bafa³”.

Kallonsa tayi jin yanda yake ta maimaita maganar ba
ƙaƙƙautawa numfashi ta fesar tare da faɗin.

“Toh ai naci kai ne fa bakaci komai ba”.

Kai ya girgiza yana yawo da hannunsa ashafeffen cikinta
yace.

”Ni a ƙoshi nake, kin gani ɗazu da yamma naci abinci”.

Tana ɗan sakin ajiyar zuciya akai-akai tace.

“Kuma kace na ƙwaƙule maka ciki?”.

Kai ya jinjina yana ɗan lasan lips ɗin sa yace.

“Eh kin ƙwaƙule min ciki mana baki san cewa duk tattalin
lafiya da cin abinci mai kyau da gina jiki da na miji yayi na kwana bakwa guda
a dare ɗaya matarsa take zuƙeshi ba.

yanzu ma gudun Nasan zaki ƙara ƙwaƙulemin cikine yasa zan
sake ci”.

Rau-rau tayi da idanu kana tace.

“Wallahi ba ruwana da kai”.

Bai ce komai ba ya sake ɗauko naman yakai mata baki aƙalla
ya ƙara mata kusan tsoka biyar kafin yace.

“Bari na haɗa miki tea kisha”.

Kasancwar Flaks ɗin tea na gefe.

 

Kofin ya jawo da Gongomin madara dana milo cikin sauri tace.

“Ayya kaɗan zaka samun kuma kar kasa min madara ka bani
Empty zansha ”.

Kai ya gyaɗa kana ya zuba mata ya mika mata  ya ɗan ci naman.

Bayan ya gama ya jawota jikinsa ya rungumeta ajikinsa ita ma
lafewa tayi ajikinsa yayin da wani irin daɗi da nutsuwa da Salama dake bin ko
wani magudanan jinin jikinta muddin zata kasance atare dashi haka takeji.

Irin dai nitsuwar nan da duk macen duniya takeji muddin tana
manne da mijinta nitsuwace da nasani kun sani yana samawa ko wacce mace aminci
da yaƙini ayayinda take manne da jikin mijinta.

 

Shiru sukayi ajikin juna ko wannensu yana shaƙan numfashi ɗan  uwansa shi kansa bai san wani irin yanayi
yake ciki ba idan yana tare da ita.

Cikin shirun ne ta tsinkayo muryansa na cewa.

“Allah yayi wa J albarka Allah ya masa Rahma Allah ya
gafarta masa”.

Cikin sanyi da nutsuwa tace.

“Ameen ya Allah”.

Sunkuyo kanta yayi tare da cewa.

“Kina masa addu’a?”

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Eh ina masa”.

Kai ya jinjina tare da hura mata iskar bakinsa akan idanunta
wanda yasa ta ƙyaf-ƙyafta ido sai kuma yace.

“Toh kina masa godiya?”.

Ɗagowa tayi ta kallesa tare da faɗin.

“Godiyan me?”.

Murmushi yayi tare da ɗage mata hira ɗaya yace.

“Godiyar baki ni da yayi mana”.

Ware idanunta tayi sai kuma tayi murmushi tace.

“Baka ni kai ko kuma dai bani kai?”.

Shima murmushin yayi jin yanda tayi maganar kamar mai raɗa
da alamu in tana jikinshi haka muryarta ke narkewa.

Cikin tsareta da ido yace.

“Bakini dai?,ke ai kinyi Sa’a da J ya baki babban Amininsa
mafi tsada”.

Da sauri tace

“Hmmm wlh kai dai kayi Sa’a daka sameni”.

Yana murmushi yace.

“Allah ko?”.

Kai ta ta gyaɗa tace.

“Eh mana”.

Murmushi yayi tare da lakace mata hanci yace.

“Baki, Baki, Bakinki baya mutuwa toh na yarda”.

Cinno baki gaba tayi kafin tace wani abu ya tallafo kanta ya
haɗe lips ɗin su ahankali ya kamo lips ɗinta na ƙasa ya fara tsotsa .

Sishhhhhhh taja yaji tana sakin ajiyar zuciya.

Sake Lips ɗin yayi tare da kallon yanda idanunta suka koma
cikin cikin raɗa yace.

“Fitinanniya”.

Sai kuma yaja hannunta tare da cewa.

“Tashi muje mu kwanta”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Bana jin bacci”.

Ahankali yace.

“Nima bana jin bacci ai kwanciya nace muyi ba bacci nace
zamuyi ba”.

Tana ƙoƙarin miƙewa ta furta.

“Toh”.

Hannunta ya riƙe acikin nasa suka nufi bedroom ɗin ta suna
shiga ya kalleta tare da faɗin.

“Jeki yi Alwala”.

Kai ta gyaɗa kana ta shiga Bathroom tayi alwalan tana fitowa
shima yashiga yayi yana fitowa ya sameta zaune gaban dreesing mirrow.

 

Yana yarfe ruwan dake sajensa yace.

“Muje mu kwanta mana”.

Ya ƙare maganar yana fesa musu turare a jikinsu.

 

Kallonsa tayi sai kuma tace..

“Toh ai banajin bacci”.

Yana gyara tsayuwar sa yace.

“Na sani bakya jin bacci kizo nace”.

Ahankali ta miƙe lallausan tafin hannunsa yasa ya riƙo nata
kana ya jawo ta suka zo bisa gado, kana ya kwantar da ita agefensa.

Tana ɗan tura baki gaba tace.

“Yah Mu’allim wai ni kam lefin me Zip ɗina ya maka?”.

Cikin ɗan tsira mata ido ta cikin hasken Deam light ɗin
yace.

“Zip ɗin kine zakice lefin me yamin?”.

Idanunta ta lumshe tare da gyada masa kai ta furta.

“Um”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Zip ɗinki yamin shamaƙi yashiga hakkina, ya shiga
rayuwata”.

Langwaɓar da kai tayi tace.

“Kamar ya?”.

Muryansa akasalance ya fesar da numfashi tare da cewa.

“Shiya min katanga da mallakina”.

Numfashi ta fesar tare da faɗin.

“Nikam sanyi nake ji dan Allah kar ka cire min rigata”.

Wuyanta ya shafa kana yace.

“Kada ki damu ba zakiji sanyi ba zan rufeki”.

Langwaɓar da kai tayi tare da cewa.

“Da me zaka rufeni”.

Bakinsa ya kai saitin kunnenta yace.

“Zakiji ɗumin jikina”.

Khausar kam duk wani abu da yake mata sannan yake faɗa
mamaki take yayin da duk wani sautin muryarsa da zai fita yake haifar mata da
kasala da tashin tsikar jikinta sosai take ji mmkin lakuransa…

Ahaka ya zare mata rigar jikinta ya haɗe lips ɗinsu.

Haka dai  awannan
daren ma Moddibo bai bar Khausar ta sarara ba ya riƙe mata wutane sosai saboda
so yake ya saba mata ya kuma tabbatar da ita cikakkiyar mace ta yanda zata saba
dashi ta daina gudun kasancewa dashi ta fara mararin tarayarsu. 

Sai da ya ɗauki kimanin minti arba’in kafin ya ɗan ɗago ya
koma gefenta ya kwanta yana maida numfashi sai kuma ya rungumeta tsam ajikinsa
yana sauƙe numfashi so yake ya ɗan hutu kamar minti biyu zuwa uku sai suyi
wanka kafin su kwanta ahaka kuma bacci me nauyi ya ɗauke su…

 


*Gembila*

Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajja Nana da Hajja Umma ce kwance
akan gadon Momy yayin da Aunty Aunty Ruƙayya da Ummi ke kwance tsakiyar bedroom
kan katifa data shimfiɗa musu Momy dake zaune gefen katifa ta kalli Ummi tare
da cewa.

“Ummin Jameel ku kwanta kun ɗebo gajiyar hanya”.

Murmushi Ummi tayi kana tace.

“Ai Momyn Khausar bazan iya bacci ba yau sai na baki
labari”.

Murmushi Momy tayi tana gyara zamanta tace.

“Allah ko?”.

Ɗagowa Aunty Ruƙayya tayi tare da faɗin.

“Ai dai kam Momyn Khausar sai mun baki labari ,Muna tafe da
labarai kala-kala munga alfarma, Isa, Wadata, Kawaici, kara, Mutuntaka, Munga
iyayen Moddibo, Mahaifinsa, Mahaifiyar sa,Yayunsa, Ƙannensa, Kakarsa, munaga
baki ɗaya Family sa masu mutunci kamala da kawaici”.

Zama Momy ta gyara tare da cewa.

“Abin al’ajabi yaron nan suka zo suka rayu da Innayi anan
babu wanda ya taɓa tunanin yana da dangi”.

Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.

“Kin ganni nan Momyn Khausar koni kaina ban taɓa sani ba
Jameel dai kusan rasuwarsa ya fara cemin ya samu labarin inda ƴan Uwan Moddibo
suke amma be faɗa min ba ni kaina na shiga mamaki”.

Juyawa Momy tayi tare da kallon Ummi tace.

“Allah Ubangji ya rufa asiri Allah ya basu zaman lafiya,
amma yau hankalina gaba ɗaya ya tashi yanda naji Khausar nata kuka, kawai
daurewa nayi na rufeta da faɗa saboda Kukanta yana son sakani kuka”.

Sai kuma ta sauƙe Numfashi fuskarta ɗauke da damuwa ta
cigaba da cewa.

“Bare kuma acan bata da kowa sannan Mijinta ba sonta yake ba
ita ta daurawa kanta da kanta Ni abinda yake tayar min da hankali kenan Moddibo
bawai son Khausar yake ba”.

Cikin sauri Hajja Nana da bacci ya fara fusgarta ta miƙe
zaune idanunta akan Momy tace.

“Waya ce miki baya sonta in faɗa miki Aysha kiyi shuru da
bakinki babu Munafukai aduniya sama da wannan yarinyar da yaron bata nuna mana
saboda Jameelu zata Auresa ba to ƙarya take suna soyayya wannan abin nasu
ƙaryane ace babu soyayya ke kinga abinda suke wlh ita kanta Khausar tana
matuƙar sonshi so na gaskema kuwa bare shi uban gayya kam ai ko tattabara sai
haka”.

Cikin mamakin maganarta Ummu ta zuba mata idanu sai kuma ta
juya ta kalli Aunty Ruƙayya da take cewa.

“Kai gaskiya Momyn Khausar al’amarin Moddibo ya sunce min
ƙwaƙwalwata da tunani idan kinga abinda Moddibo ke yiwa Khausar wallahi ³ gaba ɗaya
sai kin faɗa Duniyar da bakiyi zato da tunani ba”.

Cikin mamakin kalamanta Momy ta gyara zama tana sauraren ta
Aunty Ruƙayya kuwa cikin farin cikin yanda Moddibo ya karɓi Khausar hannu
bibbiyu ta cigaba da faɗin.

 “Abinda Moddibo ke
yiwa Khausar ya wuce akirasa da so sai dai Ƙauna kai baza ma kasan da me zaka
Misalta shiba saboda ko kallon Khausar yake yi kallone da yake cike da tsantsar
soyayya,kulawa da tausayi Momyn Khausar ki cire tunanin da kike yi ba cewa wai
Moddibo baya son Khausar ni inaga akwai abinda M Jameel ya sani shiyasa yace a
haɗa Auren khausar da Moddibo”.

Ummi ce ta gyara zama tare da cewa.

“Nima abinda nayi tunani kenan ina ga tabbas Jameel yaga
Moddibo nasan Khausar ne Shiyasa ya haɗa abin domin gaskiya abinda Aliyu ke
yiwa Khausar soyayya ce mai zafi da zurfi atare dashi”.

Baki sake Momy ke kallonta cikin mamaki tace.

“Moddibon yake son Khausar?”.

Cikin tabbatar Ummi ta gyaɗa mata kai tace.

“Babu shakka babu tantama babu Haufi acikin wannan al’amarin
wallahi akwai soyayya mai ƙarfi tsakaninsa da yarinyar nan ita kanta bata sani
ba shi kuma bai fito fili ya faɗa mata ba al’amarin su soyayyace mai ƙarfi”.

Ajiyar zuciya Momy ta sauƙe kana tace.

“Ikon Allah amma abinda Mamaki”.

Hajja Umma dake kwance tayi murmushi tare da faɗin.

“A akwai soyayya kam dan lamarinsu  yafi ƙarfin ace wanzar da wasiyyane kawai
bama so bane soyayya ce ta gefe duka biyu”.

Cikin sauri Ummi tace.

“To ai shi Aliyu idan yasan wasiyyar ma daga baya ya sani don
har aka ɗaura Auren nan har muka je baisan da batun wasiyyar ba”.

Kai Aunty Ruƙayya ta jinjina tare da faɗin.

“Kinga kuwa ran farko da yaga Khausar irin rungumar daya
mata?”.

Murmushi Momy tayi tare da sunkuyar da kai tana jin wani
irin sanyi nutsuwa da Salama.

Aunty Ruƙayya Kuwa ahankali tace.

“Wallahi rungumar daya mata sai da gaba ɗaya falon ya ɗauki
tafi zaki rantse da Allah uwace da ɗan ta ya ɓace tsawon shekaru ta gane sa
haka ta rungumeta kamar ma ya manta da akwai mutane acikin Falon itama Khausar
ni har taban kunya yadda ta lafe a jikinshi kai kace furanninesu”.

Fuska ɗauke da farin ciki Momy tace.

“Moddibon?”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.

“Tabbas kuwa Moddibon shi ɗin dai”.

Hajja Nana dake jinsu tace.

“Tabbas Moddibon kuwa bakisan fitsaran yaron bane ya tsefe
idanunsa yo wannan ƙasurgumin tuzurun ai sai abinda Allah yayi”.

Zama suka gyara suka cigaba da bata labarin abinda ya faru
Hajja Nana ma cikin gyara zama ta riƙa basu labarin yanda yaje dining ya same
su da Khausar filla-fillah duk abubuwan da suka faru acan sai da suka bata.

Haka nan Momy taji wani irin nutsuwa da Salama har misalin
ƙarfe biyu suna zaune suna hira juyawa Ummi tayi tare da kallon Momy tace.

“Nikam Momyn Khausar kina zaune Lamiɗo fa kin barshi shi
kadai”.

Dariya tayi tare da faɗin.

“A’a haba yau kam ai nace masa Hajiya Bunayya taje ta
sameshi nikam ai ina tare da baƙi”.

Da mamaki Aunty Ruƙayya tace.

“Kamar ya Hajiya Bunayya taje ta sameshi ba tare sukayi
tafiyar ba?”.

Still Murmushi tayi kana tace.

“Inma tare da ita akayi tafiyar ba ai bata gan shiba bai gan
taba ko?”.

Haɓa Ummi ta riƙe tare da cewa.

“To ai kema baki ganshi ba”.

Momy na dariya tace.

“A’a duk da haka dai suje na turata ni kuma inji da baƙina
mana”.

Ƴar dariya Ummu tayi tare da faɗin.

“Eh lallai kam hakane”.

Daren wannan ranan haka suka rabata cikin hira.

 

Acan Side ɗin Haiydar kuwa kwance suke da Sulaiman yana ta
bashi labarin Morocco da kuma Family Moddibo da irin abubuwan da aka gabatar
acikin Masarautar.

 

Acan ɓangaren su Asma’u kuwa bayan ta gama waya da Dr Jameel
ne ta juya ta kalli Asiya dake waya da Zakariyya sai kuma ta maida idanunta kan
Dija dake kwance ba tayi bacci ba cikin sanyin murya tace.

“Nayi kewan Khausar bari In kirata inji”.

Ajiyar zuciya Dija ta sauke tana gyara kwanciyar ta tace.

“Wallahi kuwa nima nayi kewarta kira mana ita muji”.

Ɗaukar waya Asma’u tayi tare da dearling Number Khausar har
tayi ringing biyu ta gama bata ɗauka ba kallon Dija tayi kana tace.

“Ki gani fa har kira biyu bata ɗaga ba”.

Wayar Dija ta ɗauka ta duba lokaci ɗan ware idanunta tayi
tace.

“Kina gani ƙarfe biyu na dare nefa ya za’a yi ki sameta kina
ganin wannan mijin nata maƙale mata mam-man-ne mata ai da wuya idan ba suna can
suna maƙale da juna ba”.

Asma’u kuwa kirji ta dafe tare da ɗan zaro ido sai kuma tayi
saurin cewa.

“Haka fa”.

Sai kuma ta janyo wayar ta kashe tare da kallon Dija tace.

“Ai Yah Moddibo duniya ne wani irin kallon da yake yiwa
Khausar kamar zai mai da ita cikin zuciyarsa”.

Dija na gyara kwanciyar ta tace.

“Aikuwa Soyayya ce mai ƙarfi Moddibo Namijin Duniya ne”.

A wannan daren haka suka kwana hira.

Acan ɓangaren su Khausar ma suka kwana maƙale da juna.

 

 

 

        Washe gari da
safe

 

     *Abujan Nigeria*

Bayan fitar Uncle Naseer da kimanin minti talatin Amina ta
fara jiyo gurnanin macijin na fitowa tana zaune Jingine jikin kushin wanda tun
jiya daya shata jikinta ke mace ta kasa da faɗawa kowa aranta tana ji tana so
ta faɗawa Ummanta amma ta gagara tayi waya da Samira Sani ma tayi niyyar faɗa
mata amma sai taji bakinta yayi nauyi ta kasa sanar mata tana kwance taji
gurnanin Macijin  kusa da ita cikin sauri
ta miƙe daga kwance ta zubawa Micijin Ido yana isowa kusa da ita kamar jiya ya
shiga rigarta ya kamo kan Nipples ɗin ta ya-shash-sha  kafin ya kama hanya ya fita tun jiya daya sha
bata sake dawowa dai-dai ba tana jin kasala bata da kuzari yanzu ma daya sake
tsotsa sai taji gaba ɗaya jikinta ya sake mutuwa ahankali ta kalli bakin
Nononta na dama kana ta kalli na hagun taga ɗigon jini kamar na jiya wani irin
nauyi jikinta yayi mata ahankali ta sulale ta kwanta wani irin bacci ya ɗauketa…

 

Acan gidan Lamiɗo kuwa Abualeey, Waziri, Galadima Baban
Zakariyya tun da sassafe  aka kai musu
abinci da komai na buƙata na alfarma kuwa su Asma’u ne suka kai musu Breakfast
da komai ba buƙata.

 

Bayan sun kammala Breakfast Ummi ta kalli Momy tare da cewa.

“Momyn Khausar mufa zamu tafi”.

Da sauri Momy tace.

“Da wuri haka Ummin Jameel?”.

Ummi na murmushi tace.

“Gidan ba kowa nayi missing ɗin ɗan Autana Bashiruna Nasan
tun jiya yake tsammanin zan koma yaji shiru yayi ta kirana ma ban ɗauka ba nafi
so ma sai naje ya ganni”.

Kai Momy ta jinjina tare da cewa.

“Ayyah Asma’u am ki riƙa ɗan leƙoni kafin kema a ɗauke mana
ke kinga ƙawarki kam an ɗauke ta zakuje can ku haɗu”.

Asma’u kam kanta ta sunkuyar ƙasa tana murmushi tace.

“Momy gobe ma zanzo in Sha Allah”.

Cikin sanyi Momy tace.

“Allah ya kaimu”.

 

Miƙewa Aunty Ruƙayya tayi tana kallon Momy tace.

“Toh nima zan tafi”.

Kai Momy ta gyaɗa kafin duk sukayi mata Sallama suka tafi
bayan ta basu komai na biki.

Acan ɓangaren Mazan bayan sun kammala Breakfast Lamiɗo yai
musu jagora suka tafi gidan su Malam Ahmad sukayi tambayar Auren Asma’u wa
Jameel gaba ɗaya malam Ahmad da yaji lbrin Jameel sai da yashiga ruɗu da tashin
hankali jin tsananin kamarsa da Jameel bayan sunyi tambaya sun dawo da tabbacin
Anbasu kasancewar Lamiɗo ne ya musu Jagoranci.

Bayan sun dawo Hajja Nana, Hajja Umma Baffa Jimeta suka tafi
Jauro Yaya daidai lokacin da Motarsu Hajja Nana ya fita akuma dai-dai lokacin

Text ɗin Yah Ali ya shigo wayar Dija, cikin tsananin mamaki
take karanta sakon nasa.

“Tun jiya da dare jikina da zuciyata suke gaya min kun dawo
Nigeria kun shigo jihar Adamawa sabida wani irin ni’imtaccen ƙamshi da isaka
mai sanyi da nakejin wanda ya tabbatar min kin kusa dani, shiyasa nake fata da
burin in ɗaukeki daga Jauro yaya in dawo dake kusa dani a matsayin matar aurena
in kin amince Dija”.

Wasu irin tagwayen murmushi take saki ba ƙaƙƙautawa ta
karanta sakon a karo na uku kana ta turawa Khausar tare dayi mata bayanin wanda
ya turo saƙon da kuma neman shawara, haka dai sukaci gaba da tafiya.

 

Motarsu Hajiya Lami da Samira Sani yayi Parking sunzo wajen
Hajiya Bunayya dan jin cikekken bayanin da tsara batun tafiyarsu.

 

 Zuwa lokacin su
Abualeey sun gama komai Lamiɗo ya musu Jagoranci zuwa gidan Abban Jameel Lokacin
da Hajiya Turai da Hajiya Karima suka kalli hoton Dr Jameel dasu Abban Jameel
da kuma lbrun kakannisu da Jameel da kuma lbrin dangin Modibbo sosai suka shiga
mamaki, musamman kamannin Dr Jameel da kuma M Jameel abin yayi masifar basu
mamaki ya kuma girgiza su a washe gari suka je Juuro yaya suka gaida Hajja
Nana.

 

Kwanan su biyu acikin Taraba suka koma Adamawa kwana ɗaya
sukayi a Adamawa ya zama kwanan su uku sukayi suka shirya komawa Morocco…

 

  A Morocco kuwa
rayuwa ta fara tafiya Khausar da Moddibo sun fara samun shaƙuwa na musamman
wanda su kansu basu fahimci haka ba aranan dasu Abualeey zasu dawo Khausar ce
zaune a falon Didi bayan sun gama girki wanda bisa alamu sun yiwa baƙi da zasu
dawo ne sun gama komai sun shirya a dining.

Ahankali Didi ta kalli Khausar tare da cewa kizo ki zauna
kici abinci”.

Anutse Khausar ta ɗago Idanunta tare da shafa cikinta kana
tace.

“Didi na ƙoshi bana jin yunwa”.

Juyawa Didi tayi tare da kallon Moddibo dake zaune gefe da
system a gaban shi bisa alamu aikin da ya shafi campanny Abba ne yake duba,
cikin kula tace.

“Taci abinci tunda gari ya waye?”.

Kai ya girgiza cikin alamun damuwa ya kalli Didi kana ya
maida kallonsa kan Didi yace.

“Babu abinda taci ni kaina bansan meyesa bata son cin abinci
ba kuma ba haka take ba”.

Langwaɓar da kai tayi tare da cewa.

“Nifa bana jin yunwa nasha tea ɗaxu”.

Didi na girgiza kai tace.

“Toh tea Abinci ne? Khausar ai tea ba Abinci bane.

Rahama maza ɗebo min abinci a plate”.

Miƙewa Rahama tayi ta ɗebo abincin ta kawo mata aplate karɓan
abinci tayi tare da kallon Khausar tace.

“Sa hannu kici”.

Kai ta girgiza tare da faɗin.

“Allah Didi banjin yuwa cikina aƙoshe yake”.

Kai Didi ta girgiza kana tace.

“Bana son zamanki da yunwa Khausar koda bakya jin yunwa ki
karɓa kici”.

Kai ta sunkuyar ta ɗauki cokali saboda batason yiwa Didi
gardama.

Moddibo kuwa ahankali ya ɗago ya kalleta tare da faɗin.

“Wallahi Didi tunda gari ya waye bata ci abinci ba idan
kinga taci abinci sai na matsa mata dole² bansan meyesa ba”.

Dai-dai lokacin Ibraahim dake shigowa yace.

“Toh ko dai bata da lafiya ne?,Idan baki da lafiya ne mu
kaiki asibiti aje aduba ki”.

Tana cakalan abincin tace.

“Wallahi lafiyata ƙalau bana jin komai abinci kuma ina ci
ina yawan shan Fruit nake gama shine yake hanani cin abinci”.

Ajiyar zuciya Didi ta sauƙe tare da cewa.

“Toh yanzu dai kici bari kuma akawo miki fruit ɗin”.

Cokali biyu zuwa uku ta sake tsakura kana ta tura plate ɗin
gaban Rahama tace.

“Toh muci mana”.

Ɗan ware Idanu Rahama tayi tare da faɗin.

“Ai kina gani ɗazu naci”.

Sake langwaɓar da kai tayi tace.

“Ni ma Wallahi na ƙoshi”.

Cikin sauƙe numfashi Didi tace.

“Kici mana Khausar am”.

Ahankali ta sunkuyar da kanta tare da faɗin.

“Allah Didi na ƙoshi”.

Kai Didi ta gyaɗa kana tace.

“Toh shikenan Rahama jeki ɗauko mata fruits”.

Kai Rahama ta gyaɗa sai kuma ta miƙe ta dauko mata wani
kekyawan Bowl wanda ke cike da

 Inabi, Apple, Banana,
Pineapple, Water millo wanda yake a yayyanki an yarayarɗa madara akai.

A hankali ta gyara
zamanta tare da ɗaukan fork ɗin jin Didi na cewa.

“Bismillah”. A hankali tai Bismillah tare da soka yankan
kankana kana ta buɗe bakinta a hankali tasa, lumshe udanunta tayi sabida zaƙi
da garɗin madarar da ya game mata baki, a hankali take taunan kankanan tare da
haɗiyewa, sai kuma tattare ƴaƴan kankanan ta haɗesu gefen bakinta.

Shi kuwa Modibbo ta gefen idonshi yake kallonta,

yanka na biyu ta kuma kaiwa bakinta ba tare da ta haɗiye
ƴaƴan kankanan ba, sai kuma ta sake harhaɗe ƴaƴan kankanan ta tarasu gefen
bakinta sabida bata iya haɗiyesu, sai kuma ta jujjuya kwayar idanunta alamun
tana neman wurin da zata zuba ƴaƴan kankanan ne.

A hankali ya miƙo mata hannunshi tare da buɗe mata tafin
hannunshi, cikin fidda idanunta waje ta ɗan jujjuyasu alamun tambaya.

“In zuba?”.

A hankali ya ɗan juyo ya ɗan kalleta tare da ɗaga mata girarsa
ɗaya alamun yess zuba ya ƙare ɗaga girar da ƙara manna hannunsa ƙasan bakinta
kaɗan a hankali ta tattarosu tare da ɗan sunkuyowa ta zuba mishi su cikin tafin
hannunshi.

 

Cike da mamaki Rahama ta buɗe baki da hanci tana kallon su
kamar wasu tattabaru.

Ibraahim ma ido ya zuba musu, ita kuwa Rahama kai ta kuma
juyawa ta kalli Didi data kauda kanta gefe tana mgnar zuci.

“Uhmmm ai in dai ya ɗauki mahaifinku zai yi abinda yafi
hakama”.

ta ƙare mgnar zuci da kallon Ibraahim da ya saki baki yana
kallon Modibbo ganin ya afa ƴaƴan kankanan cikin bakinsa tare dasa hannunsa ya
tsinki inabi guda ɗaya ya haɗa da ƴaƴan kankanan ya ci.

 

Ita kuwa Didi murmushin tayi tare da maida kanta kan TV.

Shi kuwa Modibbo hannunshi ya kuma miƙa mata a karo na biyu
ta kuma sa mishi ƴaƴan kankanan.

A nutse taci gaba da ci, a hankali ta juya ta kalli Ibraahim
dake cewa.

“Yah Aleey in Sha Allah nima gobe zan koma Turkey”.

Kallonsa Moddibo yayi kana yace.

“Ha’a har zaka koma kuma?”.

Ya ƙare maganar da sawa Khausar tafin hannunshi ƙasan bakinta
sabida ganin ta kuma tara wasu ƴaƴan kankanan, zuba mishi su tayi tare da zuba
mishi idanu,

Shi kuma shu’umin murmushin gefen baki yayi tare da watsa
ƴaƴan kankanan a baki domin shi yasan amfanin ƴaƴan kankanan a jikin namiji,
domin babu wani abu cikin fruits dake ƙarawa wa maza ƙarfin kamar ƴaƴann
kankanan shiyasa duk wani mgnin ƙarfin tattalin lafiya mazantaka zaka samu da
sinadarin ƴaƴan kankanan a ciki.

Ya tabbatar bata san amfanin da zasuyi mishi a jikinsa bane
da bazata bashi ba.

Yoh shida ko azumin rage ƙarfin sha’awa yayi muddin ya
kuskura yayi buɗa baki da kankana to ranar ba bacci, bare ba azumin yayi ba,
kuma gata kusa dashi.

Shi kuwa Ibraahim cikin kallon yadda yayan nashi ke amsar
ƴaƴan kankanan daga bakin matarsa yana ci ya ɗan gyara zama yace.

“Eh wasu kaya zan sake kaiwa kasan ban cika zama anan ba
saboda yanayin kasuwanci na”

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Yaro Ƙarami da neman kuɗi”.

Yaaje mgnar yana kallon Khausar data tura baki alamun ya
kawo hannunshi ya amshi ƴaƴan kankanan, miƙa mata hannun yayi tare da lasar
gefen lip inshi na sama.

Didi dake sauraron tace.

“Wallahi fa kadai faɗa masa kayi masa faɗa ko zai rage
Ibraahim da zirga-zirga firr yaron nan yaƙi zama sai jaraban son Kuɗi”.

Murmushi Ibraahim yayi yana mai lallon salon so mai zafi da
darasi a wurin ustzun yayansa da ya dasa mai son aure farat ɗaya cikin fesar da
numfashi  yace.

“Toh Didi Idan ban nemi kuɗi ba mai zanyi nayi karatu na
gama kuma Ni ba ayi min Aure ba sannan kuma abubuwan nan abune daya kamata
asame su a inda babu tunda dabino ne mutane da dama suna bukatar shi acan
shiyasa muke kai musu”.

Kai Didi ta girgiza tana gyara zamanta tace.

“Toh lallai kam wato ba’ayi ma aurena ba?”.

Kanshi ya ɗan sosai tare da sunkuyar da kai dan baisan mgn
ta subce mishi ba.

Ita kuwa Didi cikin kulawa tace.

“Toh Amman ai bashi kaɗai kake yi ba inka dawo nan ɗinma
komai na hotel ɗin Mouldy ka ciki”.

Ƴar dariya yayi tare da faɗin.

“Toh Didi ba dole inne mi kuɗi ba sune abokan rayuwa”.

Murmushi tayi tace.

“Yanzu kayi magana”.

Cikin sauƙe numfashi yace.

“Da Yauma nayi niyyar tafiya amma ina jira su Abualeey
su dawo ne Shiyasa”.

“Allah ya dawo dasu lafiya”.

Cewar Moddibo.

Da ya kuma miƙa Khausar hannun a karo na barkai ita bashi
ƴaƴan kankanan da sai yanzu ta cinye sai kuma ta kalli bowl ɗin tuni ya cinye
mata inabi.

 

Zama Didi ta gyara tare da faɗin.

“Aima In Sha Allah nan da awa biyu zasu iso”.

Atare suka hada baki wajen cewa.

“Masha Allah Allah ya kawo su lafiya”. Kana sukaci gaba da
hirarsu Rahama kam zama ta gyara tana bin Modibbo da Khausar da kallo domin Ita
dai darasi take ɗauka.

 

Aranan su Abualeey suka dawo sun dawo kuma da labari mai daɗi
cewa Mahaifin Asma’u ya bawa Dr Jameel Aurenta sannan Mahaifin Asiya ma ya bawa
Zakariyya wanda ansa bikin  Auren nanda
wata uku ne masu zuwa.

 

A daren ranar misalin ƙarfe biyu da rabi.

A hankali Khausar ta saki wani irin raunataccen kuka mai
cike da gajiya kasala gamida fara galabaitar da ita da Modibbo yayi.

Wanda tun sha ɗaya ya rsitsata, hutun awa ɗaya ya bata tana
cikin bacci ta kuma jin ya kwaƙumeta.

Shine har yanzu bai sararamata ba kusa 50 minutes kenan,
cikin yarfe hannun ta kuma saki sassayan kuka bawai dan zafiba sai dan gajiya
duk da kuma cikekkiyar nitsuwa da yake samar nata.

“Wasshhhhhhhhh Yah Mu’allim na gaji”.

Cikin tsananin farin ciki gamsuwa salama da wadatacciyar
ni’amarta ya tallabota jikinshi tare da fara sa mata albarka da yiwa J ɗinsa
addu’a da Abbanta.

“Wow Minha vidaa Jazakillahu khairan wa yatta ƙinallahu
jami’an kin  bani dukkan jin daɗi da na
miji kema, Allah yayi miki albarka Yayiwa Mommy gafara duniya da ƙiyama ya
killace mata farin ciki ta kamar yadda ta killace min budurcinki Allah yayi
mata tukuici da jannatul firdausi”.

Cikin gajiya da narkewa a jikinsa da jin daɗin addu’ar da
yake wa iyayenta tace.

“Amin Yah Mu’allim”.

Sai kuma ya tallabota suka shiga bathroom sukayi wanka kana
suka fito liƙe da juna.

 

Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya wani shaƙuwa na musamman
ne yashiga tsakanin Khausar da Rahama wacce ta zame mata kamar Asma’u, sannan
Didi na nuna mata soyayya na musamman mai nutsarwa da kwantadar da hankali
Hakama Niyna, Innayi kuwa tuni ta dawo ɗaya daga cikin ɗakunan dake falonta,
kana an kawo mata komai na girki tare da hadimai uku, biyu masu girki ɗaya kuma
maiyi mata dan gyaran ɗaki.

 

A banƙaren Modibbo kuwa sosai yake baza hutun amarcin da
aka  bashi, sai dai time to time yana
leƙa fada, domin Abualeey nada burin yin murabus nan kusa shiyasa yake nuna
mishin komai na masarautar Alhamdulillah kuma yana gane komai sosai.

 

Alhamdulillah Abban Jameel kuwa ya ɗauki Yah Ali aiki a
Company sa wanda yakeso shi zai maye mishi gurbin Modibbo, sosai karar da Abban
Jameel yayiwa su Bappa jimate ya sasu farin ciki ya kuma ƙara dangon zumunci

 

Aɓangaren Amina haka rayuwa ta cigaba da tafiya tsakaninta
da Macijin nan kullum zai fito yasha Nononta wanda zuwa yanzu ta fahimci
jininta yake ɗan zuka kasancewar duk sanda yasha nono taɓa ganin jinin kaɗan
tana so ta faɗa amma ta kasa idan ta fadawa Uncle Naseer cewa tana ganin
jininta yake zuƙa sai cewa yayi ai da jininki yake zuƙa da tuntuni kin mutu
kawai yana tayani shan abu nane, ahaka yake sha-shantar da ita.

 

Haka tsakanin Dr Jameel da Asma’u soyayyarsu ke tafiya
gwanin ban sha’awa.

Haka ma Dr Zakariyya da Asiya soyayyarsu ke tafiya cikin
kwanciyar hankali.

 

Hakama Yah Ali da Dija.

Wanda tuni mgnar ta isa ga Bappa jimate.

 

Tuni shirye-shiryen aure ya kankama sosai dan Abualeey da
kanshi yace ya ɗauki nauyin gidan Jen angawaye da komai na amare Abban Jameel
kuwa shine ya ɗauki nauyin komai na auren Yah Ali da Dija tuni yasa an fara
gyara gidan cikin sama kuwa Yah ɗauki Yah Abba ma aikin sabida shima CB inshi
sunyi kyau.

 

Aɓangaren Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ma sun shirya zuwa
Niger wajen sabon bokan da suka samu…

 

Yau kwanan su Ummi goma sha biyu  kenan da tafiya.

Ahankali Khausar ta tura ƙofan Falon Moddibo ta shiga saboda
tana so tayi wasu da Ummi dan tunda suka tafi ba tayi waya da kowa ba
kasancewar Moddibo ya riƙe wayarta shiyasa ta shiga ahankali saboda tana so
zata roƙesa ya bata wayarta ta kira Ummi Momyn ta harma da Hajja Nana in tayi
sa’a ta sameta.

 

A hankali ta shiga tsakiyar Falon sai kuma ta ɗan jujjuya
idanunta ganin ba kowa,

ha yasa ta nufi cikin bedroom ɗinsa tana shiga ta hango
wayoyinsa da nata akan dreesing mirrow cikin sanɗa ta ƙarasa jikin dreesing
mirrow jin alamun yana wanka a ban ɗaki.

 

Da sauri ta ɗan sunkuya
ta ɗauki wayar dai-dai lokacin kuma, ya buɗe ƙofar tare da fito ƙugunsa ɗaure
da towel cak ya tsaya yana kallonta ganin yanda take sanɗan ɗaukar wayar tana
juyawa ta ganshi tsaye a gabanta,

 cikin sauri ta runtse
idanunta ganin faffaɗan ƙirjinsa awaje cikin wata sanyayyar murya yace.

“Mene?”.

Cikin tura baki tace.

“Baka da riga”.

Da mamaki ya kalli yanda ta runtse idanunta ya lura ganinshi
na tsokanon kuran karfenta cikin yin murmushin gefen baki yace.

“Yau kika fara ganina bani da riga ne?”.

Muryanta na rawa tace.

“Ni dai ka rufe jikinka”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ok na rufe”.

Ya ƙarashe maganar tare da since towel ɗin ta ya ɗan
murzashi ƙasa kaɗan har sai da jikinshi ya bayyana.

Da sauri tace.

“Da gaske?”.

Cikin tsareta da ido yace.

“Yess da gaske buɗe idonki ki gani”.

Cikin sanyi ta buɗe Idanunta a hankali, wani irin tsalle
tayi tare da fara yarfa hannunta tana ihu.

 

 Lokacin da ta buɗe
idon,

Gaba ɗaya ta zazzaro idanunta waje tamkar zasu zubo ƙasa,
sai kuma tasako ihu kana ta juya da sauri alamun zata gudu.

ya janyota tare da rungumeta ahankali yace.

“Ba jiya guduwa kika yiba, kika ƙi kwana a nan ba, kika
kwana aɗakin Didi ba, toh gashi yanzu kin shigo hannuna”.

Ya ida maganar yana jawota jikinshi tare  da rungumeta a jikinshi….

 READ BOOK 3 HERE

 

Leave a Reply

Back to top button