Amatulmaleek Hausa NovelHausa NovelsHausa Novels

Amatulmaleek 37

Sponsored Links

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

37
*_REALTASTE 247 CATERING SERVICES_*

*_ASLM ALAIKM_*
*_Yan uwa abokan arziki yan gayu masu bikin alfarma na manyan mutane da son fita kunyar kowane kalar luxury abincin larabawa da qasashen qetare, kuzo ga number 1 best catering services damuke dashi a arewa,_*
*_REALTASTE 247 CATERING SERVICES shine best Abinda muke buqata a gurin hidimar biki da duka Wani occasions na girma da tsari tareda fita kunya indai gurin girki masu tsafta da tsarin ne tareda verities masu dadi,_*
Bikin aure
Bikin haihuwa
Bikin birthday
Picnics
Parties
Walima
Receptions
Hatta a cikin gidanka idan baka buqatan girki zakai ordern abinci daga garesu a kawo Maka har gida cikin tsari da burgewa.

Hakama kalolin abincinsu da services dinsu sun hada da;

Indian biryani rice
Mandy rice
Chinese fried rice
Stir fried spagetti
Chinese noodles
Fried rice
Party jollop rice
Chicken kebab
Beef kebab
Grilled chicken
Chicken cutlet
Kafta
Shredded sauce
Salads

Hatta bangaren snacks masu kyau da dandano da tsari babu Wanda basayi muku kalan Wanda ranka yakeso.

Realtaste 247catering services
08034425662

Instagram@Realtaste 247 catering services

Location:kano,Kaduna and Abuja.
Ga masu buqata su tuntubemu a 08034425662
Mungode.
Karku bari ayi babu ku.

*************
Abincin bakinta ne ya tsaya mata cak a maqoshi yakasa wucewa ta dago tana kallansu da matsanancin mamaki da tashin hankali tana sake hadiye abincin Amma yaqi wucewa Dan haka a shaqure ta Bude Baki tace

“Wane Naufal din?
Nawa?
Yaushe?
Garin Yaya?
Ta Yaya?

Ruwa farida ta dauka da sauri ta Bata
Ta bugesu da hannu tana sake jero tambayoyin a wahale.

Cikin tsoro suka fada mata abinda yafaru suna kaiwa inda akaiwa ‘danta ruwan bullet a qafa abincin ya dawo mata ta Baki gaba Daya idanuwanta na fitowa waje gaba Daya cikin matsanancin tashin hankali da rawar jikin Daya Saka su Farida yin baya suna sake shiga tsoro.

Mum Aishan kuwa jininta ne ya Haye take Dan haka jikinta ya dauki kyarma tana fidda idanuwanta Dake Neman fadowa tace

“Naufal dinne aka harbewa qafafuwan?
Naufal din?
Naufal din aka kashe akan matarda kilan karya take masa da sharri,
Waye yagansa?
Waye yace shine ya shiga a Daren kafin ranar?

Rawa jikinta keyi sosai idanuwanta na rufewa da Wani wutan tashin hankali da zafi zuciyarta na tsalle da tashin hankalin Danta ya mutu Dan kuwa Harbin bindiga ba wasa bane.

Magana su karima zasuyi ta Saka hannunwanta biyu ta turesu gaba Daya Bata Gani rawan tashin hankalin da jikinta yakeyi ya sa su karima rudewa cikin tsoro
Ta fito cikin ihu tana cewa inane dakin Amatun ta nufi hanyar saman tini duk suka fito suka tsatsaya hankali tashe khaltume ce kawai ta iya bin bayanta tana Bata hakuri su kuwa gaba Daya rudewa sukai.

Saman ta nufa tana Kiran sunan Amatun cikin qarfi da mummunan tashin hankalin datake ciki.

AmatulMaleek kuwa wanka ta fito sbd Daman rashin kuzarin data tashi dashi na period ne,
Tagama saka undies kenan daga ita sai towel da bra a jikinta tana kokarin dauko kayan sakawa aka Bude kofan dakin da karfi tay juyo da sauri cikin mamaki da fargaba kafin tayi Wani motsin mum Aisha din Tayo kanta tana cewa tasa ASH ya kashe mata yaro.

Hannuwanta biyu ta miqa zata janyo Amatun ASH ya miqa hannunsa ya riga nata sauka ya janye AmatulMaleek din zuwa garesa Wanda Hakan ya Saka mum Aisha din shiga shock harma da khaltume sbd basusan dashi ba,
Basu ma San Da Yana gidanba shi kansa ihun Kiran Amatun datakeyi ne ya sakashi zuwa Dan fitowansa kenan zai zauna cin abinci.

Ita kanta Amatun da batasan da Shiba ganinsa ya Sanyata boye tashin hankalinta na ganin abin mamakin.

Mum Aishan ya kalla fuskarsa Babu inda Rahama ko sauki take a cikinta Kai tsaye yace

“Kina tinanin dukanta ne ko me?
Dukan matan aure Kuma?
Nine na harbe Naufal din ba ita ba ki sameni da damuwanki idan da gaske kikeyi din banason hayaniya a gidan nan”

Daga Hakan Bai qara ko Kalma Daya ba ya juya da Amatun a hannunsa ya fice itama Kuma Amatun Bata firgita sosaiba sbd Bata taba dauka dukanta mum Aishan zataiba Tim farko.

Kai tsaye hanyar palonsa suka nufa suna zuwa har bedroom dinsa ya jata Saida suka tsaya a tsakiyar bedroom din suka tsaya ya saukar da idanuwansa akanta sai alokacin yaga iya abinda yake jikinta itama juyawa tayi ahankali tareda basa baya ya zubawa farin bayanta idanuwansa yaga Dan sauran tabon konuwarta Daya kusa gogewa.

Juyawa yayi ya bar bedroom din.

Yana ficewa itama kofar ta nufo tana son fitowa sai Kuma ta dakata tareda Jan towel dinta sama ta Bude kofar ta fito.

Baya palon Dan haka ta nufi kofa ta fito Dan dole tana buqatan kayan sakawa a jikinta.

Tana fitowa mum Aisha Bata dakin ta sauka cikin matsanancin kuka Dan kuwa tasan inda Danta yake ma ASH bazai fada mata Dan haka kuka me tsananin baqin ciki da ciwo takeyi tana tsinewa Wanda ya haifi Asmau harta haifi Amatun da Danta yagani ya Hadu da wannan halakar hakama zayyan Daya bari Naufal dinma ya dawo gidan tsine masa ta ringa yi tana cewa duk sai kowa yaji abinda taji wlh.

Kaya Amatun ta Saka ta lafe a dakinta zuciyarta cikeda sabon tashin hankalin Wani bayan Wani.

Kaman gidan makoki haka gidan yayi tsit kowa Rai a tsorace da abinda Kuma zai bullo,

Duk roko da magiya da kukan son Jim inda Naufal yake mum Aisha tayi Amma Sam ASH ko ganinsa yaqi Bata damar tayi yana sama Kuma babu me iKon ko dosar hanyarsa bare.

Har dare Babu me dogon motsi.

AmatulMaleek daqyar ta iya saukowa ta dafa masa tea ta koma sama harta aje a dining saigashi sakon txt kawai ta Gani na cewan takai masa dinner dinsa palonsa bazai fito ba.
Tana ganin txt din ta gane shine

Itama Daman bazata iya zama cin abincinba tinda tasan mum Aisha zata iya zama cin abincin batada niyar zaunawa shigewa zatayi da wuri Dan haka ta hada komai ta dauka ta nufi hanyar dakinsa.

Ko data shiga kaman koyaushe shiru Babu hayaniya ba motsi Kwanciyar hankali ce kawai a duk inda yake din.

A C table Dake palon ta ajiye trey din tana miqewa ta koma ta dauko ruwa mara sanyi tana dawowa Yana fitowa daga bedroom dinsa yabita da kallo ita Kuma Jin idanuwansa akanta ya hanata dagowa ta ajiye ruwan a sanyaye ta Bude Baki cikin sanyi ta gaidasa.

Bai amsaba sbd karantar yanayinta na sanyi da fargaban dayake ranta a boye Dan haka Yana zaunawa harta Kai kofa cikin sanyi
Ya Bude Baki ya ambaci sunan Daya Sakata tsayawa cak a bakin kofar wato “Abeedah”

Tinda take a rayuwarta Babu Wanda ya taba ambatarta da asalin wannan sunan nata Dan kuwa har a takardunta da komai nata AmatulMaleek ne Se a yanzu din.

Juyowa tayi ahankali tareda kasa riqe idanuwanta daga kallansa ta kallesa a kasalance Shima ita ya kalla din.

Babu inda yakeda kuzari a jikinta ta dago ta dawo ahankali zuwa inda yake har lokacin idanuwansa na kanta sanyinta na bawa zuciyarsa mamaki Koda yaushe.

Tana isowa abincin data kawo masa ya kalla ya dawo da kallansa kanta da alama itama Bataci ba Kuma yasan fargaba zai iya hanata ci.

A karo na farko Daya ce mata ta zauna.

Zaunawa tayi ya sake kallanta yace Baya buqatan abincin tea kawai zesha ita taci abincin.

Babu musu sbd batada tinanin kanta alokacin ta zuba masa tea din ta miqa masa ta dauki spoon sedai bataiwa abincin ci uku ba ta koshi.

Tea yaci gaba dashi batareda yace ta tafi ba karshe aka bugo masa waya ya dauka Yana yin wayarsa hankali kwance.

Tin tana jiran ya gama har ta cire Rai da gama wayar tasa fargabanta Yana qaruwa Dan so tayi ta shige da wuri ta rufewarta Amma a yanzu data kai wannan lokacin na dare baa sakintaba tana fargaban fitowan gashi kaman yanda ita tasani Shima ya sani mum Aisha bazata iya rintsawa ba batareda ta gansa ba a tsananin buqatan ganinsa take Amma yaqi Bada damar.

Bai gama wayoyinsa ba sai guraren 1 daren dayake bama da Wanda yake qasar yake magana ba.

Waiwayowa yayi ahankali ya zuba mata idanuwansa gaba Daya Yana mata Wani irin kallan nutsuwa,

Bacci takeyi kaman baby duk da a takure tayi baccin Amma komai nata a natse takeyinsa har baccin ma,

Qananun kukan darenta ya Tina ko ta Dena tinda ta warke Kuma ta dawo gida.

Numfashi ya sauke ahankali tareda miqewa yazo inda take kwancen ya dauketa Kai tsaye ya nufi bedroom dinsa da ita har tsakiyan gadonsa ya kwantar da ita.

Yana kwantar da ita tana Bude idanuwanta ahankali cikin bacci ta saukesu a fuskarsa hannuwansa Daya sauketa baima Riga ya janye daga qarqashinta ba.

Dagowa tayi Dan ya janye hannuwan nasa daga bayanta kirjinta da nasa ya Hadu Wanda ya sanyasa Jin tidin kirjinta sosai a kirjinsa take ya zuba mata idanuwansa tayi rufe nata idanuwan ahankali Dan batasan cewan yajita sosai ba.

Ita kuwa qamshinsane dayake shigar hancinta direct yake Neman illata bugun zuciyarta Dan haka ta sake dagowa a karo na biyu tareda Dora tafin hannunta kan nasa Dan janyewa.

Kafin ta motsa ya janye hannunsa daga bayan nata ya juya ya shige toilet.

Yana shigewa kasa motsawa tayi sbd Batasan Yaya zatayiba bayan rufe idanuwanta tana komawa baccin da batasan ko zai dauketaba.

Yana fitowa hasken dakin ya fara ragewa gaba Daman sanye yake da pyjamas dinsa gadon ya nufo Kai tsaye ya kwanta.

Alarm na lokacin sallan asuba ne ya fara ringing a hankali ba wata hayaniya,
Dan haka ya Dan motsa kadan tareda miqa hannu ya kunna hasken dakin kadan kafin ya Bude idanuwansa ahankali daidai fuskarta data gap da tasa tana San fidda numfashi ahankali haka kawai zazzabi ya Dan dameta a lokacin Wanda kusan na firgicin data Kwana dashi ne.

Hannunsa Daya yakai ya wuyanta yaji da zafi sosai
Saukan hannunsa a wuyanta ya Sanyata Bude idanuwanta a Dan wahale ta kallesa ta mayar ta rufe cikin wani irin sanyi da sakala.

Hakan datai ya sanyashi lumshe idanuwansa tareda sake Kai hannunsa cikin wuyan nata ya tabo zafinsa.

Ta Dan sake rufe idanuwanta a karo na biyu tana motsawa,

Kaman tafiyan ruwa ahankali taji saukan muryarsa cikin kunnanta babu qarfi ba hayaniya ya furta

“Kin kwana da fever ne??

Yanda yayi mata maganan ya Sakata Bude idanuwanta Ashe nasa idanuwan akanta suke take idanuwansu suka shiga cikin na juna
Kallansa ya Sakata kasa Bude Baki ta gyada masa Kai ahankali tareda motsa hannunta ahankali ta nun cikinta amatsayin shine yake mata ciwo tinda bazata iya cewa mararta ba duk da ba Wani ciwo bane me tsanani.

Rashin maganar datai ya Sakasa tinanin sosai takejin ciwon Dan haka da ido ya mata alaman cikin na ciwo take nufi?

Gyada Kai tayi ahankali cikin sanyi.

Ba zata hannunsa ya sauka kan cikinta Daya Sakata dauke numfashi lokaci Daya tana qanqame hannunsa.

Hakan datai shine ya Sakasa sake zuba mata ido da mamakin har sosai haka cikin ke Mata ciwo.

Zamewa tayi tareda kokarin tashi zaune sedai hannunsa Dake cikinta ya Sakata dawowa Baya sedai akan jikinsa ta Baya ta dawo daidai shikuma ya taso Dan haka ta fado tsakiyan kirjinsa hannunsa daya na zagaye da ita kan cikinta.

Shiru sukai dukkaninsu kafin ya qarasa zagayota da Dayan hannun jikinsu na mannuwa da kyau.

Ajiyan zuciya me sanyi ta sauke sabanin shi dayaji Wani irin sanyin yanayi ya shigesa na nutsuwa.

Basu jima ahakan ba qamshin dayake wuyanta ya ringa shigan hancinsa Kai tsaye yana tinatar dashi yanda qamshin mace yake a hancinsa Wanda bazai iya Tina Yaya mace take qamshi bayan tsawon lokaci Sai yanzu din.

Ahankali yayi mata kyakkyawar rungumar data Sanyata Bude idanuwanta a kasalance ta duk da ta Baya ne yake rungume da ita din haduwa me kyau jikinsu yayi.

Saukan kansa cikin wuyanta ya Sanyata mayar da idanuwanta ta rufe ahankali bugun zuciyarta na qaruwa.

Qamshinta ne yake sake shigarsa Yana Saka Jin Wani irin yanayin daya kasa gane na Menene ma,
Hannuwansa Dake kan cikinta zagaye ya dago Daya ya shafi wuyan nata ahankali tayi saurin dago hannunta a kasalance ta Dora akan nasa Dan riqewa Amma ta kasa sai Hakan ya sakashi juyo da ita gaba Daya ya manne kirjinsa da nata yana lumshe idanuwansa da baccin cikinsu suka fita gaba Daya.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

*_REALTASTE 247 CATERING SERVICES_*

*_ASLM ALAIKM_*
*_Yan uwa abokan arziki yan gayu masu bikin alfarma na manyan mutane da son fita kunyar kowane kalar luxury abincin larabawa da qasashen qetare, kuzo ga number 1 best catering services damuke dashi a arewa,_*
*_REALTASTE 247 CATERING SERVICES shine best Abinda muke buqata a gurin hidimar biki da duka Wani occasions na girma da tsari tareda fita kunya indai gurin girki masu tsafta da tsarin ne tareda verities masu dadi,_*
Bikin aure
Bikin haihuwa
Bikin birthday
Picnics
Parties
Walima
Receptions
Hatta a cikin gidanka idan baka buqatan girki zakai ordern abinci daga garesu a kawo Maka har gida cikin tsari da burgewa.

Hakama kalolin abincinsu da services dinsu sun hada da;

Indian biryani rice
Mandy rice
Chinese fried rice
Stir fried spagetti
Chinese noodles
Fried rice
Party jollop rice
Chicken kebab
Beef kebab
Grilled chicken
Chicken cutlet
Kafta
Shredded sauce
Salads

Hatta bangaren snacks masu kyau da dandano da tsari babu Wanda basayi muku kalan Wanda ranka yakeso.

Realtaste 247catering services
08034425662

Instagram@Realtaste 247 catering services

Location:kano,Kaduna and Abuja.
Ga masu buqata su tuntubemu a 08034425662
Mungode.
Karku bari ayi babu ku.

Leave a Reply

Back to top button