Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 54

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

54
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

************
Ko data Isa asibitin room number din dake tareda sunan asibitin cikin text din mum Aisha ta nufa gabanta na Dan faduwa tana Kuma fatan mum Aisha dince tayi hadarin motan da bama zata iya magana ba bare fadawa Dad dinta abinda takeson fadan.

Tana tsayawa kofan dakin Kai tsaye knocking tayi tareda Bude kofan dakin ta tura ta shiga idanuwanta na fara sauka kan Naufal Dake zaune Shima kofan yake kalla idanuwansa jajir da zafin zuciya da baqin cikin ganinta kaman zai tashi ya raba da ranta yakeji.

Rawa hannuwanta suka fara ta shigo tareda rufe kofar tana kallan Naufal jikinta na sake daukan rawan tashin hankalin ganinsa da qafa Daya.

Tsoro ne me qarfin gaske ya kamata ganin qafarsa Daya yanda take din Dan haka tayi saurin juyawa bazata iya kalla ba tsoro me tsananin gaske takeji Dan bata Saba ganin irin wannan tashin hankalinba.

Damqota mum Aisha tayi cikin zafin Rai tareda dawo da ita ta jefata gadon Naufal din gurin qafar Dan ta Gani da kyau.

Hawaye Husnah tafara jikin na sake daukan rawa sosai hakama bugun zuciyarta na tsananta har cikin zuciyarta tsoron ganin qafar takeyi hankalinta ya tashi sosai har ta kasa magana sai cewa tayi

“Mum Aisha banason Gani Ina tsoron ganin qafar uncle Naufal,tsoro nakeji banson Gani,Ina qafarsa Daya take Dan Allah karki…….

Cikin zafinta daya kasa dannuwa da tsananin bacin Rai Mai hade da baqin ciki mum Aisha ta falla mata Wani gigitaccen Marin Daya Saka Husnah fadawa kan qafar Naufal din jikinta na rawa tayi saurin janyewa daga qafar a rikice da azabar Marin sedai kafin ta qarasa janyewa mum Aisha ta sake dafe kanta a gurin kafar tana cewa

“Ki Kalli qafar da kyau yanda tsoro ze juyar Miki da qaramar qwaqwalwanki kafin ki fuskanci hukuncin abinda kikai daga Wanda ya Yanke masa qafa akan abinda kece kika haddasa komai”

Rawar masifaffen tashin hankali da firgici jikin Husnah ya dauka tana hawaye tana rintse idanuwanta daga kallan dungun qafar Naufal din dake fuskarta ta fashe da Wani irin kuka tana cewa

“Mum Aisha Dan Allah kiyi hakuri wlh zan Suma idan Ina ganin wannan qafar Dan Allah ki barni na tafi gida”

Cikin baqin ciki da takaici Naufal ya motsa qafar ya tura mata a fuska Yana buge bakinta da dungun duk da Yana Dan Jin zafi Amma baqin ciki ya hanasa Jin zafin sosai.

Kuka sosai Husnah keyi tana Neman shaqewa kafin mum Aisha ta dagota ta zubar qasa tana kallanta cikin zafin zuciya tace

“Yanda kika ga ya rasa qafarsa Daya akan abinda yayi to idan ASH din yaji kece kika turasa me kike tinanin ze Miki?
Kinsan ASH ne da kansa ya yankewa Naufal din kafa akan zuwansa mansion gurin Amatu kawai,
To idan shi ya Yanke kafarsa Dan yaje mata ke da kika aikasa kika ringa kiransa kina cewa yaje gidan me zaayi Miki?
Ke harma rigimar farko ta zuwan Naufal din dakinsu Amatun kece kikai mixing drink dinsa ma Dan yajewa Amatun……..

Cikin masifaffen tashin hankali Husnah ta dago jajayen idanuwanta ta Kalli mum din muryanta na rawa tace

“Wallahi tallahi banyi Hakan ba,ba nice ba,ban…..

“Kece kikasan ba kece ba mu bamu San Hakanba, ASH ma baisan Hakan ba…”

Rawa jikinta ya sake dauka hawayenta na qafewa tace

“Mum Aisha wlh banyi Hakan ba, Dad dina ba bazai taba yarda da zanyi Hakan ba,
Wannan na bayan ne kawai nasan na cewa uncle Naufal din yaje mansion ba kowa Se Amatun ya mata abinda yakeso….

Muryarta taji tana maimaita abinda ta fada yanzu a wayar Naufal din yayi playing recording din maganar tata.

Juyowa tayi ta kallesa idanuwanta na sake cikowa da wasu hawayen jikinta na mutuwa gaba Daya,
Kan mum Aisha ta dawo da kallanta hawayenta na saukowa ta Bude Baki a sanyaye tace

“Mum Aisha Dad dina bazai yarda da na aikata Hakanba,
Dad dina bazai iya yanka qafana ba kaman na uncle Naufal,
Dad dina bazai iya ko ganin bacin Rai na na bare yanka qafana….

Katseta mum Aisha din tayi da cewa

“Idan shine ya haifeki ba,
Idan shine ya haifeki daga tsatsonsa shine bazai iya Miki Hakan ba Amma tinda mijin uwarki ne kawai Kuma qanin mahaifinki mezai Hanasa ko aurar dake ga Daya daga cikin securities dinsa idan har bazai iya yanka qafarki ba bayan kin tura namiji yayiwa matarsa fyade,matarma wadda yakeso fiyeda Taki uwar Daya rufe babinta a rayuwarsa…….

Zuru Husnah tayi tana kallan mum Aisha da idanuwanta batareda ta fahimci Kalma ko Daya datake fada ba daga kalmominta na farko dasuka shiga kunnuwanta.

Naufal ne ya miqa hannu ya jijjigata daga zaunen dayake Yana cewa

“Abinda ake nufi ana shine ba ASH ne Wanda ya haifeki ba auran mamanki yayi dake a hannunta Dan rufa muku asiri ya Baki sunansa….””

Bata gane abinda suke fada ahankali taji jinta na daukewa bakinsu kawai take ganin suna motsawa suna fadan maganganun da Sam batajin komai.

Maimaita mata kalmomin suka ringa yi Daya bayan Daya har sai da jinta ya dawo zantukan suka ringa shiga kunnuwanta suna ratsasu zuwa cikin kanta,
Maimakon su Isa ga zuciyarta cikin kanta suke wucewa suna juya kan ahankali.

Zubewa tayi qasa take Neman yi mum Aisha ta tareda tareda kama hannunta kaman makauniyar da akewa jagora.

Harabar asibitin ta fito da ita Babu mutane sosai kowa abinda yake gabansa yakeyi.

Motarta ta Bude tareda kamata ta shigar da ita ta zaunar a mazaunin driver tareda saka key ta tada motar ta kama hannunta ta Dora mata kan steering ta kalleta tace

“Kije gida”

Rufe mata kofar motar tayi tareda juyawa ta koma ciki Dan tasan Babu yanda Husnah din zata iya Kai kanta gida a wannan halin itama yau zata dandani abinda ake nufi da azaban hadarin data saka Naufal a ciki ya rasa qafa ita Kuma kila ran zata rasa gaba Daya.

Tana juyawa Husnah taja motar a cikin mummunan gudun Daya Saka securities din asibitin tareta suka hanata fita sbd tsaro suka hau bincike motarta tana zaune kaman wadda Babu komai a tareda da ita bayan numfashin datake shaqanta kaman tana shaqan gas take ji sbd ficewa hayyaci.

Suna gamawa suka hanata fita Saida ta Dan dawo hayyacinta suka Bude mata gate ta ja motar cikin Wani irin tsananin gudun gaske me qarfi ta hau titi ko ganin gabanta Batayi sosai.

Ko data Isa mansion din TALBAs ganinta yafara qaranci sosai Dan haka parking dinma Bata qarasaba ta fito motar tana hada hanya ta nufi cikin gidan.

Step din farko na stairs data Dora kafarta zata hau Sam sakon Naufal ya shigo wayarta Wanda yasata dubawa da idanuwanta Bata Gani sosai.

“Idan har kin samu Isa lafiya karki manta wadda ta fada Miki waye babanki itace takeda abin fadawa ASH TALBA abinda ya samu matarsa waye sanadi”

Qurawa sakon idanuwanta tayi hannuwanta na rawa sosai sbd idan ta fahimci abinda suke nufi shine idan ta fada Wanda ya fada mata ita ba yar ASH bace zasu fada masa abinda tayi.

Da dafa Bango ta Isa palon saman seda zuciyarta Dake kokarin bugawa ta kasa riqe abinda takeson riqewa ta Isa dakinta ba shiri Bata saniba ta zube tsakiyan palon tareda fasa Wani irin ihun Dayake dauke da tsananin girman baqin cikin da zuciyarta ke Neman fashewa akansa…

Gaba Daya mansion din sautin ihun nata ya dauka Wanda ya Saka kowa fitowa hankali tashe musamman Amatu da anty Farha da bedroom din Amatun yake palon sosai ihun yafi shiga kunnuwansu.

Maamah ma dasu khaltume duk a rikice sukayo saman sedai Koda kowa ya iso Husnah din ta sume a gurin hawayen Dake cikin idanuwanta suna gangarowa Babu abinda yake motsi nata.

Amatu ce tayi kanta cikin kulawa ta fara tabata tana ambatar sunanta cikin fargaban abinda ya sameta.

Maamah dasu khaltume kuwa harma da anty Farha Babu abinda yazo ransu Se Madame abeeda lokaci yayi ta cika kawai Dan haka kowa jikinsa ya dauki bari musamman maamah dataji zuciyarta na Neman tsayawa daga aiki tayi Baya Amatu ta miqe da sauri ta tareta tana kiranta a tsorace cikin damuwa da tsananin kulawa.

Zaunar da maamh din tayi su Kuma su khaltume suka kama Husnah din itama suka Kai kan kujera tareda debo ruwa suna zuba make Amma Sam ko motsawa Batayi.

Rawa jikin maamah ya sake dauka ta miqe da kanta ta karbi ruwan tana zubawa Husnah din Amma Sam Babu alaman zaa sameta.

Farha ce cikin tashin hankali ta dauko wayarta ta kira likita Amma Sam Bata shiga dan haka kawai suka kwasheta zuwa asibiti.

Maamah da Husnah dinne a Baya anty Farha na gaba Amatu ke driving sbd Basu tsaya cewa driver yakaisu ba.

Asibitin da suke zuwa aka nufa da ita suna Isa aka amsheta da gaggawa sbd kusan lamarin ya sake tsananta Dan numfashinta ma ya tsaya cak.

Maamah ma kusan dole suka buqaci likita ya dubata Dan kuwa itama zubewan take Neman yi Dan itama Amatun zuwa lokacin ta saddaqar da cewan Wani abu ya samu Madame abeeda ne.

Bayan an duba maamah itama an Bata gado ta huta na awanni hakama Husnah gadon aka Bata
Shiru Amatu tayi sai alokacin jikinta yayi sanyi da damuwan halinda ASH yake ciki idan Wani abin ne ya samu Madame abeeda.

Numfashi ta sauke ahankali tana kallan wayar anty Farha dake hannunta tanajin tanason Jin muryarsa Dan sanyaya damuwansa sedai zataso da tata wayar zata kirasa Dan haka ta danne abinda take ji a zuciyarta idan ta koma gida ta kirasa.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Back to top button