Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 61

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

61
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

************
Ba maamah ba ko Amatun cikin faduwan gaba da firgici me girma a cikin zuciyarta ta juya ta Kalli Husnah din kafin ta dawo da kallanta kan maamah da sauri wadda zuciyarta ta buga da karfi sedai Kuma Sam zancen be shigetaba ba hakama batasan tayaya ma zata iya tsayawa tayi wannan maganar da Yara ba Dan haka shiru tayi tareda zubawa Amatu idanuwanta tsawon mintina Babu Wanda yace komai abinda maamah din zata fada suke Jira Amma ga mamakinsu sai kawai ta juya ta sauka batareda tace komaiba.

Amatu sanyi da firgici take Neman shiga Dan haka kasa bin bayan Maamah din tayi ta shige dakinta Husnah ma dakinta ta koma tana tsiyayar hawaye ta dauki wayarta a yau take son barin gidan ta tafiyarta sbd Jin tsanar Dad din takeyi tana shigarta tareda mamayeta.

Mum Aisha kuwa bayan Maamah tabi har dakinta ta zauna Babu magana mara dadin da Bata gaya mata tareda Bata tabbacin Amatu ta Dade da zaman cikakkiyar macen ASH TALBA Kuma wlh wannan cin amana ce Mafi girma Dan haka ta sani itace ta tarwatsa gidan Abeeda ta tarwatsa mata ‘yaya ta rabasu da ubansu sbd yanzu Husnah ta tsani Dad dinta hakama Haydar na ji zai tsanesa Shima Dan haka ta zama balai da masifa a rayuwar ahalin Abeeda.

Shiru maamah tayi har mum Aisha tagama ta fice daga dakin Bata iya cewa komaiba Bare motsawa,
Zuciyarta ce tayi mata Wani irin mummunan nauyi da ciwo tana buga mata ba daidai ba sedai bazata bari ta kwanta ba yanzu da duka gidan yake buqatanta Dan kawo karshen matsaloli.

Duk yanda taso riqe abinda takeji kasa riqewa tayi Dan haka ahankali ta fasa Wani irin kuka mara sauti tana rufe fuskarta da mayafin dayake jikinta jikinta na jijjiga sosai,
Bayan baqin ciki da qunci kusan a yanzu Babu abinda yake mamaye da zuciyarta da rayuwarta,
Bata cikin dadin zuciya,.ta Hana kanta walwala,ta Hana kanta Jin dadi da farin ciki duk akan kada auren Amatun da ASH ya zama cikakkiyar aure Amma Kuma yanzu ana fada mata zancen da Sam Bata yarda da zai iya yiyuwaba.

Amatu Kuwa tana shiga dakinta kasa cin abinda ta dauko tayi ta ajiye zuciyarta na shiga damuwa da fargaban abinda zai iya shiga zuciyar maamah da abinda Husnah ta fada gashi bama zata iya zuwa gurin maamah din ba Dan kuwa bama zata iya kallan fuskartaba bayan abinda aka furta din da Sam batamasan ta Ina zancen ya fito ba.

Babu Wanda ya fito breakfast Shima bayan shigarsa bedroom dinsa kirane birjik ya tadda a wayoyinsa Daya bari akunne ya tafi.
Shirin fita office kawai yayi ya fito ya Tararda ba kowa ya kira Husnah a waya ya sanar mata ta fito su fita tare sbd yanason Bata time dinsa sosai yanda ya kamata.

Qin daukan wayarsa tayi harya Dena Kiran,
Mr Jameel kawai yacewa bayan sun tafi driver ya kawo masa Husnah din office zasu fita.

Tsit gidan yayi kowa cikin damuwa da nauyin zuciya yake musamman Husnah da Maamah Dan Amatu yunwarta kasa riquwa tayi jiki ba qwari ta fito ta sauko qasa ta samu abinci a kitchen taci ta qoshi ta koma sama kenan zata shige bedroom dinta Husnah ta fito dakinta suka Hadu a tsakiyar palon
Kasa riqe zuciyarta Husnah tayi ta tsaya gaban Amatu tareda tarewa cikin daci da tsananin baqin ciki tace

“Menene sunan da zaa kiraki dashi?
Kafin ki jefawa mijin Aminiyar mahaifiyarki kanki ya kamata kiyi tinanin alaqan maamah da mum,
Menene su…..cikin Bacin Rai da baqin cikin maganar idanuwanta suka rufe bata tsaya komaiba ta kama hannun Husnah din da karfi ta fizgeta zuwa hanyar palon Dad din nata Dan Bata amsar maganarta a gabansa sedai ko taku biyu bataiba taji an riqo nata hannun tana juyowa Taga maamah tana mata Wani irin kallo idanuwanta jajir.

Magana zatai sbd idanuwanta da suka cika da bacin Rai da baqin cikin abinda Husnah din ta fada mata maamah ta katseta Kai tsaye da cewa

“Ina Zaki?
Ina Zaki jata kuje??

Sakin hannun Husnah din tayi tareda kallan maamah din bacin ranta Baya boyuwa tace

“Maamah kinji kalaman data jefeni dasu?
Kin….

Daga mata hannu maamah tayi cikin Bacin Rai da baqin ciki tana cewa

“Komai aka fada Amatu kece kikaja,
Meyene alaqarki da abinda suke fada din?
Shin kin menene ma ya hadaki guri Daya da ASH din harma wanna abin duka yake neman lalacewa?

Katseta Husnah tayi hawayen baqin cikinta na qaruwa tace

“Maamah wlh a dakin dad ta kwana….

Shiru maamah tayi jikinta na rawa tana kallan Amatun da dukkanin bacin Rai hakama Amatun sai alokacin hawayen baqin ciki me tsananin gaske ke ciko idanuwanta
maamah tace

“Me Husnah ke fada?

Saukowa hawayenta sukai tana kasa cewa komai saima nauyi da zuciyarta tayi kafin tayi magana baqin ciki ya Saka idanuwanta Neman juyewa ta dafa Bango da sauri sbd jirin Daya debeta zai zubar Dan Bata dauka maamah zata jefeta da wannan tambayar ba.

Kuka Husnah ta sake fashewa dashi tana ihun mum dinta mutuwa zatai idan taji wannan mummunan labarin,
Hakama Amatu taci Amanar mum dinsu da Haydar.

Gaba Daya hargitsa gurin tayi da kukanta da maganganunta da suka Saka Amatu barin gurin zuciyarta na nauyi da tsananin damuwa da bacin Rai da fushin da batama San tanada shi ba.

Maamah kasa cewa komai tayi sai kawai ta bar palon ta kira ASH da kanta akan tanason magana dashi idan Yana gida.

Baya gida ya sanar mata Amma zai dawo da wuri a ranar.

Mr Jameel kuwa drivern da aka Saka ya kawo Husnah office din Dad dinta ya sake kira Amma driver ya sanar masa Husnah Bata fito ba.

Amatu bayan shigewarta daki kuka ta saki me ciwo da dacin Rai sbd lamarin yafara yimata yawa,
Ta rasa tayaya ta rasa so da kauna tareda yardar mahaifiyarta..

Kuka takeyi sosai Wanda ma batasan Yaya takejin Yana zuwaba Yana sake tayar da zuciyarta zuwa wuya.

Wayarta anty Farha keta kira Amma takasa dauka Dan haka ta kira khaltume wadda sukai tsit sbd ihun kukan da Husnah keyi tana fasa kayan palon saman ko zuciyarta Dake balbala da wuta zata sauka Amma Sam Babu abinda takeji a zuciyarta da jikinta bayan zafin baqin ciki.

Maamah Dake dakinta tana Jin ihun Husnah din da tashin hankalin datakeyi tana ambatar sunayen Amatu Dana mum dinta Amma Bata motsaba daga dakinta sbd yau lamarin ya isheta Babu abinda take buqata bayan barin gidan itada Amatun Dan ita yanzu bama zata iya bari Abeeda ta dawo ta tadda Amatun a gidan ba bare tasan meya faru.

Khaltume ce ta sanar da anty Farha abinda yake faruwa cikin damuwa gashi mum Aisha ta tattara ta fita batama gidan bare dakatar da Husnah wadda gaba Daya t zare Babu abinda take gani bayan Dad dinta da Amatu suna cin Amanar mum dinta.

Ita kanta Amatu datake dakin tana Jin duk abinda Husnah din keyi hakama kuka takeyi sosai Dan kuwa tasa bacin Rai da tsananin kukan da Maamah Tasha Koda Bata fada ba,
Ita komai ya isheta itama batason zaman kaman yanda Husnah take fadan bazata iya zama inda Amatu take ba itama Hakan takeji sbd abubuwan sun mata yawa.

Anty Farha Kam tashi hankalinta yayi Dan haka ta kira wayar mr Jameel ta sanar masa anata tashin hankali a Mansion din.

Satar kallan ASH yayi Wanda yake amsa waya ahankali yaga yanda yake wayar hankali kwance da nutsuwa.

Yanda Mr Jameel yake satar kallansa ya tabbatar masa da magana me mahimmanci Dan haka ya Dan takaita wayar ya kashe Yana kallansa yace

“Uhumm Ina ji”

Cikin damuwa da Dan sauke Kai mr Jameel din yace

“Ana rigima ne a mansion tsakanin Husnah da L.A”

Shiru yayi tareda dagowa ya zubawa Mr Jameel din idanuwansa Yana nazarin zancen sbd baijin akwai abinda zaisa ma ko hayaniya Husnah tayi da Amatu Bare rigima,
Wayar da maamah tai masa ce ya dawo masa.

Wayarsa ya dauka Kai tsaye maamah din ya kira.

Tana daf da katsewa ta dauka a natse sedai muryarta Sam Babu dadi da alamu kuka tai ko makamancinsa.

Baima yi mata magana ba sai kawai ya kashe wayar Yana nazarin abinda zai zama rigimar,
Idan har Husnah zatai hayaniya da little Abeeda akan maganar aurensa dayake kanta ne dakuma mum dinta hakama Asmau yasan Daman tanada damuwa da auren.

Idan maamah tana cikin wannan halin to little Abeeda na cikin Wanda ya fisa,
Dagowa yayi ya Kalli mr Jameel Kai tsaye yace

“Ayiwa Maamahn little Abeeda komai su wuce tareda Husnah Greece”

Kaman Mr Jameel na Jira ya gyada Kai da sauri Dan kuwa yau ba sai gobe ba zai tura su Lagos suna can zai qarasa musu komai su wuce.

Fitowa sukai Kai tsaye mota ya nufa da sauri aka Bude masa ya shige suka nufi gida Yana kashe wayoyinsa tin a hanya.

Koda suka iso Husnah tafara gabalaita da kukan datakeyi da tashin hankalin hakama maamah dole tazo ta riqeta tana kokarin dawo da ita hankalinta cikin kulawa da damuwa me tsananin gaske.

Anty Farha ta riga su ASH isowa Dan haka ta ringa buga dakin Amatu wadda ta rufe kanta data cikin tayi kuka harta galabaita sbd maganganun da maamah ta shigo ta fada mata masu kama da tafiyarsu zasuyi subar gidan hakama batajin zata sake barinta ko fitowa daga dakin nata har su samu barin gidan.

Tashi hankalin anty Farha yayi musamman ganin palon kaman anyi damben balai a cikinsa sai tsoron ko Wani abin ya faru kafin su zo ya shigeta ta ringa buga kofar tana Kiran sunan Amatun,
Gasu maamah da Husnah a palon hakama su karima suna palon qasa a tsaye jiki duk yayi sanyi sbd Basu taba ganin wannan tashin hankalin a gidan ba bayan na gobarar da Akai.

Babu tsammani sukaga ASH a cikin palon kallo daya yayiwa gurin gaba Daya ya Kalli Husnah Dake jikin maamah tana kuka har lokacin ya nufi kofar dakin Amatun Kai tsaye daidai ta budewa anty Farha kofan dakin Dan haka anty Farha janyewa tayi ta basa kofa ya shiga Kai tsaye Yana kallan idanuwanta dasukai jajir ko tsayuwar arziki Bata iyayi.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Back to top button