Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 59

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

59
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

****************
Palonsa suka nufa Yana shiga da qafarsa daya ya tura kofar palon bayan sun shige,

Kan doguwar luxury console table Dake farkon shigowa palon ya zaunar da ita Bai tsaya komaiba ya hade bakinsa da nata
Itace tafara kissing dinsa tana susutar dashi gaba Daya missing din dayayi mata ya taso masa Yana qanqameta dakyau cikin jikinsa tana sake kashesa da yanda take kissing dinsa hayaqi kawai yakejin suna fita kunnuwansa.

Rigar jikinta ya yaga da hannuwansa ya zare ya jefar Yana bin milk Skims wireless embroidery bra dinta da kusan komai Yana Gani a ciki da matsiyacin kallo Yana ambatar sunanta cikin qasan maqoshinsa.

Abinda yake faruwa a gurin cikin sanyi me girma ne Dan kuwa numfashinsa ne kawai ke fita a gurin ahankali har sai daya tabbatarda bazai iya wahalarda ita a halinda take ciki na Jin yunwar da ko Bata fada masa ba yasan abinci tazo ci a dining din.

Sauko da ita yayi suka nufi bedroom dinsa ya zaunar da ita a bakin gado ya dauko mata wata shirt dinsa fara ya Saka mata sbd tata din bazata maidu ba Dan botiranta gaba Daya sun zube qasa Babu abinda zai riqe mata ita a jikinta hakama bra dinta Bata jikinta dole rigar tasa kawai ya Saka mata tareda mayar Mata da hularta ya rufe mata kanta suka fito Yana riqe da hannunta kaman basune suka gama abinda suka Gamo ciki din ba.

Suna fitowa zaunar da ita yayi ya zauna Shima kenan kafin yayi Wani motsin Husnah ta shigo gurin mum Aisha ma ta shigo Babu Wanda ya Kalli inda Amatu take shi suke kallo kowannensu a natse cikin girmamawa suka gaidasa suna masa sannu da zuwa Shima a natse ya amsa Yana kallan Husnah data sauya gaba Daya.

Cup din Daya dauka ya ajiye ahankali Yana kallanta cikeda kulawa Yana Dan kame fuskarsa sbd rashin Jin dadin ganinta ahakan yace

“Husnah,Wani abu Yana faruwa ne?
Kinyi rashin lafiya ne ko me???
Meyasa nake ganinki Hakan??

Shiru dukkaninsu sukai kowa gabansa na faduwa musamman Husnah din Se mum Aisha da kowannensu Baya fatan Koda tsautsayi ASH din yasan meyake faruwa a tsakaninsu.

Amatu ma shiru tayi tana kasa cewa komai bare dagowa Dan kuwa sosai ASH din ya zama serious da abinda yake fada amsar tambayarsa yake jira Kuma shirunsu ya Sakasa tabbatarda akwai abinda yake faruwa din.

Amatu ya juyo ya kalla yace taje ta kira masa maamah.

Tana Jin Hakan itama nata gaban ya sake faduwa Dan haka ta miqe a sanyaye sai alokacin idanuwan mum Aisha ya sauka kan rigar Dake jikin Amatun wadda ko zaa cire idonta ta shafa tasan ta ASH ce sbd kalan kayan dayake sakawa daban suke Dana Kowa duk mansion din da kewayansa kusa,hakama tayiwa Amatun yawa sosai rigar ga qamshinsa Dake tashi a jikinta….

Sarqewa tayi da qarfi tari me gigitarwa Yana taso mata tafara yinsa tana dafe kirjinta Dake Neman toshewa sbd Tarin tashin hankalin ta tabbata kenan ASH yafara ganin wannan yarinyar a boye ko me??

Ruwa ta dauka hannunta na rawa ta Bude takai bakinta tana sha da sauri sbd karta mutu a banza Asmau da yarta su samu ASH TALBA yanda suke so.

Amatu gaba Daya bata Tina da rigar dayake jikinta ba Kai tsaye maamah taje ta kirawo wadda itama Bata ma lura da meye a jikin Amatun ba suka dawo Saida suka shigo dining room din har lokacin kowa na zaune cikin zufa batareda sunce komaiba.

Maamah na shigewa ta tsaya daga gefen tareda Dan kasa kallansa suka gaisa ta sake masa barka da dawowa
cikin mutuntawa a natse ya Bude Baki yace

“Meyake faruwa ne a gidan nan?
Husnah tayi jinya ne?
Akwai matsala ne a gidan daya kamata na sani?

Maamah ma shiru ta Dan yi sbd batasan me zata fada ba Kuma bayan abinda ta sani Wanda ita kanta batasan Menene matsalan Husnah dinba.

Numfashi ta Dan sauke ahankali ta Bude Baki tace

“Babu Wani matsalan bayan yanayin jikin Husnah Daya tashi sai Kuma kuka da tashin hankalin da nake ganin kaman dole akwai abinda yake damunta duk da Ina tinanin ko yanayin jikin Abeeda ne yake damunta”….shiru tayi daga Nan sbd Bata buqatan sanar dashi sauran tashe tashen hankalin da Husnah ta ringa sakasu da some somenta tinda ya wuce.

Shiru yayi Yana nazarin zancen maamah din sedai bayajin a yanzu da Abeeda ta tashi ciwonta zai Saka ciwon Husnah din tashi sedai Wani abun daban.

Kan Husnah Dake tsiyayo hawaye masu radadi ya Maida idanuwansa kafin ya Maida kallansa kan mum Aisha datake Dan sake shan ruwa tana Hana kanta sake sarqewa sbd fargaba Dan idan ASH yayi saurin ganota ya rabata da gidansa komai lalace mata zaiyi sbd Bata Riga ta Tara abinda ya kamata ace ta Tara ba a zamanta gidansa shekara da shekaru.

Kan Amatu ya Maida kallansa yaga itama duk tayi sanyi kanta akasa sai alokacin idanuwansa suka tinatar dashi da rigar dake jikinta Amma Bai damuba a yanzu damuwar datake Neman juyar masa da kan ‘ya yake Neman sani.

Sake maimaita tambayarsa yayi akan Husnah meyake damunta,

Dago kanta tayi ahankali zatai magana idanuwanta suka fara sauka kan AmatulMaleek da maamah ta tsayar a gefenta ta tareta daga zuwa cikin dakin da kyau,

Qurawa Amatu idanuwanta tayi tana kallan rigar jikinta da take ma ta hango Babu bra jikin Amatun,

Tsoshewa kirjinta yayi kafin idanuwanta suka fara Neman Dena Gani daidai tayi saurin rintse idanuaan sai kawai ta fashe da kuka Mai tsananin gaske tana kasa tantance abinda yake Shirin faruwa a cikin gidan ubanta da uwarta.

Kukanta ya Saka maamah Jin Babu dadi zuciyarta na sosuwa hakama tana mata nauyi lokaci Daya sbd tasan bakomai ne yake cin zuci da rayuwar Husnah ba sai irin abinda yake cin ranta na abinda zai iya biyowa bayan Abeeda tasan wannan auren na kaddara Dan haka itama cikowa idanuwanta sukai da hawayen ta Yanke shawarar yin magana dai a yau din komai ya zo karshe,
Dagowa tayi tareda dawo da kallanta kan ASH Dayake sauraron kukan Husnah har cikin ransa yake jinsa.

Bude Baki tayi zatai magana mum Aisha tayi saurin katseta sbd yanzu datake ganin alaman akwai abinda yake faruwa tsakanin ASH da Amatu batason a raba auren Se zancen ya Isa kunnen Abeeda Koda daga kwancen ne ta yanda zuciyarta zata buga ta mace,
Mutuwar Abeeda itace zata kawo mata komai datake so Dan mutuwarta zata buga mata zuciyar maamah,hakama mutuwarta zata qarasa juyar mata da kan Husnah haka shi kansa ASH din zai shiga Wani halin Dan haka so take kafin a raba auren kota Yaya ya Isa kunnen Abeeda koda shine abu na karshe da zata ji kafin komawa coman gaba Daya.

Hana maamah magana mum Aisha tayi ta hanyar cewa

“Husnah tana cikin damuwan rashin ganin mahaifiyarta ne bayan tashinta,
Kuka da damuwar datake ciki duk Hakan ne ya hanata walwala ganin takeyi akwai matsala babba da ake boye musu musamman dadewanka baka dawoba shine ya Bata tsoro sosai take shiga damuwa””

Husnah duk da tana cikin mummunan hali Saida ta dago ta Kalli mum Aisha tana kasa cewa komai sai qara kukanta datakeyi Wanda ya Saka ASH din kallanta da kyau ya tambaya idan Hakan dinne?

Gyada Kai kawai tayi sbd a matse take da son barin gurin kafin ganinta ya dauke gaba daya.

Sallaman maamah yayi Yana cewa ya gode taje,
Juyawa tayi takira Amatu ta bi bayanta suka bar gurin.

Kallan Husnah yayi itama cikin kulawa yace taci abincin idan ta gama ta samesa suyi magana.

Tashi yayi batareda Shima yaci abincin ba yabar gurin sbd ya tabbatarda akwai matsala a gidansa da baisan da itaba,.tsaf ta karanci kowa da abinda yake kokarin boyewa Dan haka zai gano koma Menene yasan abinda yake Neman daga zaman lafiya da Kwanciyar hankalin kowa a gidan.

Yana barin gurin abinda mum Aisha ta fara juyowa ta Kalli Husnah tana fada shine

“Lokaci yayi da Abeeda zata dawo Nigeria ta qarasa jinyarta a cikin Yan uwa da yayanta da mijinta tinda ta Farka idan ba haka ba lokacin da Zaki tattara ki bita can ASH ya dawo hannun Amatu da uwar Amatu”

Tana gama fada ta miqe tabar gurin tabar Husnah zuciyarta na tafasa kukanta na qaruwa,
Babu abinda take tsakanin buqata a yanzu bayan dawowan mum dinta Koda a kwancen ne dole zataje ko bada sanin Dad dinba ta dawo da ita sedai kawai su gansu tinda Neman mantawa yakeyi da mum dinta akan Amatun da ta kasa yarda ma da abinda yake Shirin faruwa Sam Sam bazai yiyuba.

Amatu suna fitowa da maamah komai maamah din Bata ce mata ba ta Sauka ta wuce bedroom dinta,

Shiru ta Dan yi a tsaye itama a palon saman kafin ta shige bedroom dinta ta zauna tana shiga damuwan shikenan maamah zata dawo da fushinta akanta.

Shiru gidan ya dauka yayi tsit bayan awa kusan biyu da lamarin.

Husnah palon Dad dinta ta tafi jiki a mace Dan sanar dashi tanason zuwa gurin duba mum dinta.

Cikin nutsuwa da kulawa ya kwantar mata da hankali tareda Bata tabbacin Daman tafiya Mr Jameel zai mata komai a cikin satin ta wuce.

Bayan sun jima suna magana miqewa tayi zata fice idanuwanta cikin kaddara da tsautsayi suka sauka kan bra din Amatu Dake jefe qasan gurin qaton console din dayake palon hanyar kofan ficewa da rigarta da suka watsar dazu.

Dafa Bango tayi tana Dan danne abinda yake taso mata tasamu ta Isa kofa ta fice batareda ma yasani ko fahimtar abinda ta Gani ba duk da shi baisanma kayan suna gurin ba.

Da dafa Bango ta Isa dakinta ta Bude ta shige ta rufo kofar ta Saka mata key ta Isa tsakiyar dakin ta zube qasa tareda fasa kuka me Qarfi tana rufe bakinta da hannunta tanajin ma har Dad din nata ta tsana Kuma tsana me tsanani.

Amatu tini ta kwanta sedai ta kasa bacci sbd batajin zata iya bacci batareda taci abinci ba Dan haka taketa juyawa kan gado a sanyaye cikin damuwa.

Kasawa tayi ta sauko gadonta ta zira slippers ta nufi kofar dakin ta fice.

Dining room ta nufa ta tarar da akwai abinci a Jere
Cikin Jin dadin Hakan ta dibi abincin a plate da drink da ruwa da abubuwan da zata iya ci duk a trey ta dauka ta juya zuwa dakinta.

Tana shiga dakin ta ajiye trey din kenan aka Turo kofar dakin tareda shigowa
Da sauri ta juya Se ganinsa tayi a natse hankali kwance ga mamakinta da drink a hannunsa alaman ya kawo mata sbd sanin Ba lallai taci abincinba.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Back to top button