Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 94

Sponsored Links

Page 94

Tunda ta isa gidan uncle muhsin sai ta sake sosai abinta cikinsu nujood,bayan sun gama hira da hajjaa a kebance,ta tabbatar babu sauran abinda yake damunta,saidai lokaci lokaci gabanta yana yawaita faduwa,saita tsaya da abinda takeyi idan ya lafa kuma taci gaba da sabgarta.

Da yamma ya kira ta yaji kota wuce saloon din,tace eh gata ita da nujood sun fito zata rakata,abun mamakin saita taddashi acan,zaune cikin mota yana jiran isowarsu.

“Gaskiya gaskiya nima cewa abban zanyi ko ya samo min police na aura,ko ya samomin cikin abokansa,irin wannan kulawa widad ba kowacce mace ke samun irinta ba,just saloon ma sai an miki rakiya ko anzo an jiraki harki gama a maidaki gida don kada ki shiga motar haya?” Idanun widad din akan abbas din sanda nujood ke maganar,duk da basu qarasa ba suna kusa da qarasawar amma idanun kowa yana kan dan uwansa,saita saki murmushi kawai ba tare data amsawa nujood ba, saidai can qasan ranta ita kadai tasan ya takeji akan uncle din nata,har wani lokacin takan zauna tace wai shin wa tafi ji dashi,wa tafi so tsakanin shi ummu ko mommynta?(quruci dangin hauka,kowanne so akwai kalarshi,na iyaye daban na miji daban).

Fitowa yayi ya taka mata har zuwa bakin qofar wajen,sannan ya gaya mata abinda ya saba fadi

“Ki fada mata tayi miki mai kyau,irin wanda ba’a taba yiwa kowacce mace ba” dariya ta kamata itama kamar kullum,shidai yanason gayun nan,yana son kwalliya,duk sonta da kwalliya ta samu wanda ya fita,tana murmushi ta shige,yayin da nujood ta rigata yin gaba tana jin kunya,saboda tamkar mahaifi take kallonsa.

Sanda aka gama sai suka sauke nujood a gida,bayan ya bata kyautar dubu biyar,ta shiga ta yiwa hajjaa sallama,wadda ta hada mata kayan miya,kamansu kuka daddawa kubewa mai kyau da sauransu, saboda itama tasan abas din dason wannan cimar na gargajiya,tayi musu sallama ta fito.

Suna tafe a hanya suna hira,duk da uncle din nata shine jigon hirar,kadan kadan take saka baki,saboda yadda faduwar gabanta take qara yawa fiye da dazu,a wani shopping mall ya tsaya yana dubanta

“Zaki rakani?” Ya fada a tausashe,ta sake masa murmushi tana ajjiye jakarta ta fito tabi bayansa.

Tana biye dashi ne kawai,shi ya dinga daukan kalar kayan da yakeso,wanda duka qananun kaya,irinsu mini skert leggings shirt shirt na masu daukan hankali da kuma lalatattun sleeping wears,kusan wannan din al’adarsa ce,yanason wannan shigar a wajen matarsa,a lokacin da hafsa kadai yake da ita,duk sanda yayi siyayya irin wannan asarar kudinsa kawai yakeyi,don ba sakawa takeyi ba,a yanzun kuwa kusan tare suke zabar kayan da zata saka masa duk rana shi da widad din,musamman idan suna Kaduna,sai wanda ya zaba zata saka masa,bata wani damuwa saboda kayan sunfi mata dadin sakawa a yanzun,idan tana cikin gida zaiyi wuya ka ganta da atamfa bare lace ko shadda,kayanta kenan,wani mugun kyau kuma sukeyi mata,bama kamar idan ta raba gashinta biyu,kota musu manyan kalba,yakan lalace wajen kallonta ne,itakam da batajin nauyin jikinta tayita tsalle tsallenta abinta.

Chocolate ya hada dasu masu dan yawa saboda su mimi ya biya kudin suka fito,ya miqa mata ledojin yana cewa sanda yake shirin kunna motar

“Ta kayan taki ce,ta chocolate kuma ta sha zumamu mimi ce” qaramar dariya tadanyi, tanason zaqi kam yarinyar,sai ta buda ledar kayan nata tana diban wasu tana zubawa a ledar su mimi,yadan kalleta yana yin reverse

“Me kikeyi haka?”

“Mommyn mimi na sakawa wasu kayan,baka siya da ita ba,naga kudin da yawa” kai ya girgiza suna haurawa kwalta

“Kinason kiyimin asarar kudina na kawai…..” Sai kuma yayi shuru ba tare daya qarasa ba,sannan ya sake cewa

“Duka naki ne,jibi nakeson ki zaba me kyau a ciki…..wadda tafi kowacce kyau ki sakamin,ita kuma duk sanda muka fita ko tace tanaso saina siya mata nata daban” bata kawo komai cikin kanta ba ta gyara ledar ta mayar dasu yadda suke.

Ana kiran magariba suka isa gida,wasu masallatan ma har sun tayar,ya kashe motar ya rakota,gudun kada sallar ta qwace masa saiya tsaya daga qofar falonta ta bude ta shiga shi kuma ya koma da dan sauri don ya riski sallar.

Duhu falon saboda ta kashe dukka qwayaye kafin ta fita,tana tsoma qafarta gabanta yayi mummunar faduwar da har sai data dora hannunta a qirjinta,wani irin mahaukacin tsoro ya saukar mata,saita saka hannu tayi hanzarin kunna wutar sassan nata.

Duk da haske ya wadaci wajen amma abinda ya gushe na tsoron daya saukar mata din bashi da yawa,ta fara takawa a hankali kamar mai sanda ta nufi dakinta,duk inda ta tsoma qafarta ta dauke sai taji kamar ana biye da ita,wannan ya sakata qara hanzari,ta fada dakinta ta tura qofar tayi zaune bakin gado tana wuwwurga idonta cikin dakin,cikin sa’a bakinta ya kama kalmar

“Hasbunallahu wa ni’imal wakil,ni’imal maula wa ni’iman nasir” sannu a hankali saita fara jin tsoron yana raguwa,ta rufe idonta tayita maimaitawa kafin ta bude idon a hankali,sai taji tadan samu nutsuwa,ta ajjiye ledar da mugun takatsantsan saboda qarar ledar tana jinta har cikin kanta,ta cire mayafinta ta shige bandaki tana fatan mimi ta shigo mata ko ta rage zaman shurun.

Alwalar data yo ta qara mata nutsuwa,ta dawo ta tayar da sallah,sanda ta idar sai tayi zaune saman abun sallar,gidan shuru ba motsin kowa,sai qarar babban generator dake aiki a farfajiyar gidan,yana daya daga cikin abinda yasa ta tsani bauchin,wannan zaman,inda a kaduna suke da yanzun tana jikin uncle dinta,suna karatu k suna wani abun tare,komai ma tare sukeyi ita dashi,ba wani abu da suke rabawa,kama daga wanka bacci cin abinci,sallar ma wataran jam’i sukeyi ita dashi,ya tsefe mata kai ya yanke mata farce,wani zubin ma har ya gwada mata kalba,amma a bauchi fa,duka time dinsa yana rabasu ne a tsakaninsu.

Tana nan zaune har akayi kiran isha’i ta tashi ta gabatar,ta sake komawa ta zauna,tun yamma rabonta da abinci,amma kuma bata jin yunwa,batasan me yake damunta ba,wani lokacin ta tashi da mahaukaciyar yunwa,wani lokacin kuma ta tashi bata sha’awar cin komai,duk da haka dole ta tashi ta shiga kitchen bayan ta leqa window ko zataga wulgawar mimi amma ba ita ba alamarta,ta tsaya ta dafa indomie guda daya ta soya qwai biyu,tana yi tana takatsantsan,duk duk wani motsi da zatayi da kwanukan firgita takeyi,tana gamawa ta dawo daki ta zauna ta tasa abincin a gaba.

Tana fara ci taji bataso,saita ture plate din,zuciyarta na mata wani qunci,kawai sai ta fashe da kuka sosai tana curewa waje daya,gidan gaba daya ya fice mata akai.

Yana zaune da wayarsa a hannu yana amsa saqonni,su mimi na gefe suna wasansu,yayin da hafsat din ke hada masa abincin dare

“Yau ba zuwa wajen anty mimi?” Ya tambayi yarinyar yana aje wayarsa bayan hafsat din tace ta gama zubawar

“A wajen mahaifiyarta zata kwana” hafsat dake shirin zama tayi caraf da maganar,duba daya yayi mata ya kauda kansa gun yaran yana gayyatarsu suzo suci abinci,kusan al’adarsa ce wannan,tunda mamarsu bata iya cin abinci dashi ba,tare dasu yake cin abinsa,tun bai saba ba har ya zame masa jiki.

Tana daga zaune a gefensu,bata ce komai ba,suna cin abincin suna hirar su da yaransa yana dariya abinsa,abinda yake sake qule hafsat kenan,sai abu mai ciwo ya faru,tana ganin abun yakai munzalin bacin rai,amma sai yasa yaransa a gaba suyita sabgarsu,taja qwafa can qasa tana jijjiga kai,idan komai bai faru ba ashe bata cika hafsatu ba.

Suna gama cin abincin ta kada kan yaran zuwa dakinsu,basa jin bacci a sannan amma haka ta tilasta musu kwanciya,ya fahimci me take nufi,bayason suje wajen widad din,sai shima ya watsar da ita,ya wuce toilet yayi wanka hade da brush,ya shirya cikin wasu silk pyjama sky blue,ya dauki wayarsa ya wuce sassan widad din don ya mata sallama,ta bishi da harara ba tare da yasan me takeyi ba,cikin ranta fana fadin

“Na kusa maganin matsalata naga qarshen wannan rawar kan”.

Tun kafin ya qarasa yaji ya qagu ya isa din,ya buda qofar da sallama a bakinsa,yadda yaga falon komai a kashe yasan tayi shirin kwanciya ne,don haka ya zarce bedroom dinta kai tsaye.

Buda qofar da taji anyi har tsakiyar kanta,ta zabura ta daga kanta da sauri hantar cikinta na kadawa,wani mugun tsoro yana mamayarta,suna hada ido ta miqe da sassarfa ta isa gareshi hadi da fadawa jikinsa ta rushe da kuka

“Ya salam……ya Allah” ya furta a tausashe hannunsa a bayanta yana dan bubbugawa

“Menene baby?,mene?” Ya tambayeta yana sunkuya dai dai fuskarta,hucin bakinsa dake bada qamshin blueberry mouth spray yana sauka saman fuskartata,saita cusa kanta wuyansa tana sake sakin wasu hawayen.

“Tom,abun ya motsa kenan” ya fadi can qasan zuciyarsa yana dan sakin murmushi,ya riqeta sosai suka koma gaban gadon suka zube a qasa,ya sanyata a jikinsa yana sake lallashinta.

Sun jima a haka sannan ya samu ta tsagaita kukan,ya zaunar da ita sosai saman qafafunsa yana kallon fuskarta da tayi jajur saboda kuka

“Me ya faru?” Sai tayi masa narai narai da ido xata sake sake masa kuka,yayi saurin cewa

“Noo….ya isa, kinci abinci?” Sai sannan ta maida dubanta ga abincin data zuba din,shima ya tayata kalla,yasa hannu ya jawo plate din ya motsa abincin yana kallon qwayar idanunta

“Zakici wannan din ko na canza miki wani?” Kai ta girgiza alamun zata cin,ya sake daukan cokalin ya fara diba a hankali tana zaune saman qafafunsa yana bata hadi da sako mata irin hirar da yasan zata sanyata ta sake.

Babu laifi tadan sake din,don kafin ya gama bata tana murmushi,duk da qasan ranta wani irin tsoro ne keta mata tasiri,bayan ta gama ya tabbatar ta kammala komai na kwanciya,yayi tsaye hannayensa cikin aljihun wandonsa yana kallonta

“Shikenan?,saida safe?” Kanta ta kawar gefe,tana jin ranta ya motsu,yanzun tafiya zaiyi wajen mummyn mimi,saita gyada masa kai a sanyaye,sannan tace

“Mimi ba zatazo tayani kwanan ba?” Dan jim yayi kafin ya amsa

“Sun wuce dakinsu kafin na fito,don’t worry ki kwamta ki rufe idonki,yanzun nan zakiga safiya tayi, okay?” Saita gyada masa aki a hankali,tausayinta sosai yaji,yasan ko yaya batason rabuwa dashi,bare yanzun data saba da zama jikinsa kamar wata ‘yar mage,ya sunkuya a tausashe yayi kissing dinta,ya juya zai kashe mata hasken dakin tace

“Ka bari zan kashe” don batason duhun da zata zauna a ciki kafin bacci ya dauketa

“Okay” ya furta can qasan maqoshi,ya juya a hankali ya fice a dakin yana waigenta.

Idonta ta mayar ta lumshe tana jin ficewarsa,wani abu na tsaya mata a wuya,ta gwammace taci gaba da barin idon a rufe maimakon ta bude ta kalli hanyar da yabi ya fice din.

Cikin mintunan da basufi qwaya biyu ba taji yanayin dakin ya fara sauyawa,kamar komai na dakin motsi yakeyi,ciki harda kujerar data kwanta a kan,zuciyarta tayi mugun bugawa, madaukakin tsoro ya mamayeta,kafin takai ga bude idanunta taji dukka wata gaba ta jikinta tayi nauyi,kamar wadda DANNAU ya danneta,ta kasa motsa koda dan yatsanta bare tayi yunqurin tashi daga inda take kwance……….[3/21, 3:18 PM] +234 813 343 4840: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Back to top button