Gidan Aunty book 2Hausa Novels

Gidan Aunty book 2 Page 17

Sponsored Links

BOOK 2

Page 17

Da Sauri ta dafe hannun da ya toshe mata baki ga baki d’aya ta tsure ,zuciyar ta sai bugawa yake da Sauri Sauri , Ammey na saka hannu akan handle d’in Wanda ya rufe wa tahee baki ya shige wata ‘kofa har yanxu hannunsa na kan bakinta da ya toshe , a haukace Ammeey ta shigo part d’inta har da sawa kofar pin Sabida kar Wanda ya shigo , haukane kawai ammey batayi ba alokacin, har wani zazzafan zazzabi taji yana kamata , da Sauri ta nufi ‘kofar d’akin tsafinta , tana ta’ba ‘kofar taji an d’aga ta an buga ta da bango , cikin azaba Ammey ta bud’e baki zatayi ihu taji saukar mari zafafa a kumatunta duka biyun , fitsarin da take ri’kewane ya kwacemata , bata gama shiga cikin tashin hankali ba sai data ga an ‘kara d’aga ta sama kamar wata kayan wanki an fara hajijiya da ita , wata murya taji kamar tana jari rai ta soma yi mata kuka a kunne , tana saka hannu zata toshe kunnen taji saukar mari, da Sauri ta sauke hannunta majina duk ya ‘bata mata fuska ga wata guda wa da take neman kwace mata, muryoyi ta soma ji mabanbanta suna kiran sunanta , ihu Ammey ta saki kamar mahaukaci ta fara zagaya d’akin , ita kanta batasan me take cewa ba “ ku bari ,bani nace akashe saba , itama bani ce Nace a kashe shiba , woolllhh , hahahahahha”, ita kad’ai sai faman surutai take wani irin wa wan harbi da akai matane yasata fashewa da kuka , hakorinta guda d’aya shima ya cire , ga zafin ciwon hakori ga zafin buguwar da tayi , azaba bata ‘kare mata ba sai ma wani irin ‘kai ‘kayi da jikinta ya fara yi kamar kamar wacce akayi wa feshi, gabaki d’aya nema take ta haukace lokaci guda .

****Tun lokacin da aka kulle wa tahee baki ta nemi ta rikice tsoran tama kar Ammey ce ta kamata , yadda taji ana tafiya da Itace ya hana ta bud’e fuskarta sai ma ‘kara runtse idanuwanta da tayi, duk adduar da tazo bakinta shi takeyi, jin an tsaya kuma an saki bakinta ne yasa ta bud’e idanuwanta da Sauri taja baya har tana ‘ko’karin faduwa jikinta har karkarwa yake wajan juyowa , yadda tagansa a tsaye sanye da ba’ka’ken kayane ya ‘kara rud’ar da ita , hannunta da ya soma rawa ta d’aga ta fara nuna shi, batayi auneba taji ta rungume a jikinsa ,yadda ya rungumeta kamar za’a kwace masa ita , shi kad’ai sai faman sakin ajiyar zuciya yake , sosai jikin tahee ya soma rawa , gabaki d’aya ta rasa tunanin da zata yi, cikin sauri ta raba jikinsu tana dube duben ta inda zataga Mimi , ganin yadda take dube duben ne yasa cikin cool voice ya furta “ tana part d’in ummey “, hannunsa ya d’ora kan kumatunta da ya mara , da Sauri taja baya gudun kar asirinta ya tonu yasa tayi Sauri juya wa zata gudu. “ I missed you wifey ?”, ya furta mata a hankali, cikin wani irin expression tahee ta juyo tana binsa da kallo har yanxu jikinta be bar karkarwa ba , yadda taga yana matsota ne yasa ta soma ja da baya,still be dena bin nata ba yaci gaba da matsota, itama gabaki d’aya ta rud’e ga zafin da jikinta yake mata tun lokacin da shiga d’akin tsafin Ammey , jiri ne yayi ‘ko’karin kayar da ita ya ru’kota a jikinsa , wata nannauyar ajiyar zuciya ya Sauke kafin ya d’auketa gabaki d’ayanta yayi sama da ita zuwa bedroom d’insa . Yana shiga akan sofa ya zauna tare da d’orata saman cinyarsa , hannusa na dama ya mika a hankali har zuwa wuyanta, daidai Inda ban d’in abun fuskarta yake ya cire tare da yaye fuskar gabaki d’aya ya wurgar da ita , ai nahin fuskar tahee tafito fess da ita kamar zatayi kuka ganin tun ba’aje ko ina ba asirinta ya tonu shikenan yanxu zai fad’awa su ammey , tashi tayi daniyar barin wajan ya ‘kara dawo ta ita kan cinyarsa tare da saka both hannayensa biyu ya rungumota a jikinsa , cikin rad’a rad’a ya furta “ fushi kike dani? I can’t take it please”, da Sauri tahee tajiyo tayi hugging d’insa tana fashewa da kuka , cikin muryar kukan ta fara magana tana dukan ‘kirjinsa “why?, kamanta dani?,ka dena sona? Bakaso nazo wajanka? Nayi missing d’inka, me isa da ka gano ni ka ‘boyemun?” ,lumshash shun idanuwansa da ya zuba mata ya lumshe tare da hugging d’inta sosai a jikinsa , “ I’m sorry for the slap , I don’t meant to , but I have to sabida ke kanki baki san ana bibiyarki ba “, d’ago da kallanta tayi ta ‘kara zuba masa , gabaki d’aya yana so brain d’inta ya dena aiki “ taya ka shigo falourn? And taya kasan nice nazo ina bincike a part d’inta ?” Be amsa mata tanbayoyin taba , sai kallan cikin ta da yayi ya shafa a hankali “ the baby?”, itama tahee shafa cikin nata tayi kafun ta furta “ I lost it “, tana kai ‘karshe ya lumshe idanuwansa , jiyayi zuciyarsa na neman tsinkewa sabida babyn shi da ya rasa , hannunta d’aya tahee ta saka a kan fuskarsa da ya sashi bud’e , sosai eyes d’insa sukai ja d’an murmushi yasaki kafun ya shafa nashi cikin “ wifey , I’m hungry “, kanta kawai ta gyada masa , zata d’auki face d’inta ya hanata hakan, tare suka tafi 2 second floor cikin kicin d’inta da yake kamar sabo kullum , simple food ta girka masa , cikin Sauri sauri kar Ammey ta zargi wani abun amma taga ko ajikinsa be damu da hakan ba , ko da ta gama abincin still be bartaba har saida tayi feeding d’insa da kanta , sosai ta ga lokaci ya fara ja ,” I have to go, Ammeey zata zargi wani abun “, be kulataba ya ‘kara d’aukar a barsa kamar wata baby ya nufi bedroom d’insa da ita , yanxu kam hankalinta ya gama tashi , zata ‘kara magana ya katseta, “ nayi hakuri for long years , kina tunanin zan ‘kara kwana batare da Matata ba ?Simple No ! “ da Sauri ta girgiza masa kai “ No please! Ammey zata iya fuskantar wani abu , please am sorry kalb “ you’re sorry ? Ya tanbayeta yana ‘kara kallanta , ganin ta yi masa shiru tana ‘kara binsa da kallo ne Yasa shi d’auke kansa daga kanta , a hankali ya soma taku har yazo wajan gaban mudubin d’akin, daga jikin mudubin ya danna wani abu take gaban mudubin ya rabe gida biyu wata ‘kofa ta bayyana “ follow me “, abunda yace Matt kenan kafin ya shiga cikin d’akin da yake cike da cameras ta ko ina, wani white chair ya ja mata nan ma seat kawai yace mata , ba musu kuwa ta zauna sai faman bin d’akin take da kallo , tunda take bata ta’ba sanin cewa a kwai door awajan gaban mudubinba, yadda yake yarrafa computer din gabansama abun kallo ne , kafun ya ran’kafo Daidai saitin ta yana danna wani keyboard , take a Wajan palourn Ammey ya bayyana , abunda ya faru tun bayan barin ta palourn ya saka mata , sosai ta kurawa palour Ammey ido tana kallan abunda ya faru , ita kad’ai sai faman dariya take , ganin dariyar tata tana ‘ko’karin sha’keta ne yasa yayi saurin tsayar Dashi, da Sauri ta kalleshi a marairaice , alamar ya kunna mata , d’auke kansa yayi akanta yana nufar hanyar fita , Daidai zai saka ‘kafarsa a waje yaji saukar muryarta “ka dad’e kana bibiyarta? Me yasa da kasan true colour d’inta baka tonata ba , kake behaving a matsayin king dinta ? Har poising d’in da take sa maka kasan da haka ? “, fasa fita yayi ya jiyo ya d’an kalleta , yana sakin wani killer smile akan fuskarta “ if my brave barrister tana da basirar shigowa cikin gidan nan har ta ya’ki ma’kiyarta , me kike tunani akan mijin ta kuma ? A husband? Ko kuma a doctor? Da aka ‘batar masa da matarsa ? Shi kuma ya kasa ha’kura ya bar ‘kasar without doing anything?”, zai juya tayi saurin ri’koshi “ Tana kasan ni barrister ce !?”, hancin ta ya ja kad’an , kafun ya furta mata “ I don’t know “, yanxu ma ya juya zai fita ta ‘kara rikoshi sosai “ please “, yadda tace please d’innan gabaki d’aya saida tsi’kar jikinsa ta Tashi, lumshe mata ido yayi daidai saitin kunnanta ya furta “ from the start”, bai jira ta ce masa komai ba ya juya ya bar d’akin , da Sauri tabi bayansa itama har ya zauna kan sofa tayi saurin d’anewa kan cinyarsa tare da sakar masa wani peck a goshi, eyes d’insa ya zuba mata shi kad’ai yasan illar da kissed d’in nan zai ja masa , a shagwa’be ta furta “ please ka fad’a mun please “, what will I get in return ?” Shima ya furta har yanxu kuma yana binta da wannan kallan nasa da yake kashe Mata jiki, “ me kakeso?” Something “, ya fad’a yana d’age mata gira d’aya duk da tagane abunda ya ke nufi sai tayi kamar bata fahimce saba “ Menene kuma something ?” Murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa , wai Menene something, “ I will tell you after I give you the story “, gyara zama tayi sosai yadda zata ji dad’in labarin , shima both hannayensa ya zuwa cikin stomach din ta yana shafawa , wani murmushi na sauka akan fuskarta “ kina tanbayata Yaushe naganota?” Nodding kanta tayi masa a hankali , shima bai damu ba ya soma magana “ the day I missed you! Yes lokacin da kika bar gida bayan sun had’a plan d’in accident d’insu akai na , sunyi ‘ko’karin kasheni for a long time amma basu samu damar hakan ba , a time d’in naji rauni sosai Amma gabaki d’aya ina cikin hankali na , but babu Wanda ya fuskanci hakan sabida umarni da na bawa doctor arwan akan cewa nayi coma, and yes it works kowa ya yadda nayi comma d’in , aranar Ammey bata zo hospital d’in ta duba ni ba sai ummey, duk da itama naso na barta a comma din , to my very surprise ta ganoni lokacin da ta tabbatar kowa ya tafi , she was like “ nasan baka cikin coma , Sabida na ydda da d’ana nasan yana da dalilinsa nayin hakan , amma karka manta ni mahaifiyarkace, komai sirrin ka nawa ne “, a lokacin wani raunin mahaifiyata ya kamani bansan lokacin da na bud’e eyes d’ina ba , lokacin da take shafan kan , Aranar naga farin ciki da kuma ‘kunci a fuskar mahaifiyata, musamman raunin da yake cikin idanuwanta “, shiru king yayi yana sauke ajiyar zuciya Sabida dogon maganar da yayi yanzu , tahee ma sosai ta nutsu tana sauraran sa. Saida ya d’auki tsawan 2 minutes kafin ya cigaba da magana “ ban fad’a mata dalilin da yasa nayi haka ba , and itama bata nemi sanin dalilina nayin hakan ba , tsawan lokacin da akace Ina cikin coma gabaki d’aya nasan meke faruwa a cikin gidan batare da sanin kowa ba sai zaki dake kawo mun rahotan duk abunda yake faruwa , hatta mutanan da sukayi kidnapping d’inki suna hannu, har zuwanki Niger na sani, da tafiya Uk d’in ki”, da Sauri tahee tajiyo ta kallesa, cute kumatun ta ya d’anja kadan ganin mamakin da yake kwance akan fuskarta , bai jira jin me zatace ba ya cigaba da maganarsa, “ nasan komai da yake faruwa , all this while ba nabar Nigeria Sabida sa’banin da muka Samu da abeey ba , No!!, this is my plan for the whole time “, itama murmushi tahee ta saki tana shafa gefen kansa “ kuma ka dad’e kana bibiyar Ammey, and the cameras suma , ka dad’e da sanin me ke faru ko ? Sweetheart who are you “, murmushi ne ya kwace masa “ kina zargin mijin naki ?” , da sauri ta girgiza masa kai “ idan mijina zai iya ganoni, how comes bazan gano akwai abunda yake ‘boyemun acikin idanuwansa ba ?”, lips d’inta ya sumbata lokacin da take magana , “ kin ‘kara girma, and you’re too brave now “, hannu san ya d’ora kan cikinta “ zuciya ta bata mun dad’i , tunda nayi loosing baby na , amma haka Allah ya ‘kaddara , Allahn da ya bamu ya fi mu bu’katarsa , and question here is wanene guy d’in da yake cikin gidan ku ? And the small boy d’in da ake ganin su tare ?”, kallansa sosai tahee tayi kafun ta sauke ajiyar zuciya kad’an yadda bazai gane ba , bakinta har Sauri yake wajan furta “ babban yayan mimi ne , junior kuma niece d’insune mamansa ta rasu tun yana baby “, a hankali ya nanata sunan junior a bakinsa , itama kallansa tayi tasan ko giyar wake Tasha bazata fad’a masa Akhie d’insane ba da d’ansa tasan zai iya lalata gabaki d’aya shirin ya d’auko d’ansa “, yadda take binsa da kallo ne yasa ya hure mata eyes d’in nata , lumshe su tayi tana ‘kara kwanciya akan ‘kirjinsa “ akwai abunda kake ‘boyewa matar ka ? Who are you ?”, Tashi yayi tare da ita akan jikinsa har zuwa kan bed d’insu , sai da ya kwantar da ita kafun ya d’an sumbaci bakinta, yana kallan cikin idanuwanta , cikin rad’a rad’a ya furta “ JAMI’IN SIRRI “, yadda yaga ta zaro idanuwantane ya so bashi dariya , zatayi magana ya had’e bakinsu waje d’aya tare kashe light d’in d’akin ya bar dumm light kawai .

********
************
Tun lokacin da Ammey tabar part d’in dada ake nemanta, ummey ce ta basu uzurin ko akwai abunda ya ri’keta shiyasa kowa ya fita daga harkar nemanta ya cigaba da harkar gabansa.

*** Ammey kam kamar wata zautacciya haka ta koma jikin abun ya lafa ta d’ora hannu akai tana faman saki ihu, duk wannan ihun da take babu me jinta da Sauri ta raru wayarta har fad’uwa take , ko kallan gabanta batayi ta nufi d’akin tsafinta , ydda taga abubuwanta masu mahimmanci sun faffashe ne yafi komai d’aga mata hankali, wani number ta d’aga ta kira , amma har kusan 2 missed calls ba’a d’agaba , hankalinta ba ‘karamin tashi yayi ba , duk da hakan bata hakura ba sai da ta ciga da kiran number sai faman zafa d’akin take , cikin sa’a kuwa wannan karan aka d’aga kiran nata , banji me aka ce mata ba sai wata kururuwa da ta saki tana ‘kara yin ball da kayan wajan , ita ka d’ai faman surutu take , tun tana shirmenta harta fara to nawa kanta asirin abunda suke aikatawa da ita da na wayar da ga ‘karshe ma ball tayi da wayar tata , ta fashe tass a ‘kasa , tsugunnawa Ammey tayi gabaki d’aya ta fita a hayyacinta musamman idan ta bud’e bakinta sai mutum ya d’auka ‘yar biri ce ga gashin kanta da ya mimmike tsaye sai kace fika fikin tattaba , yanxu kan kamar me aljanu haka ta Tashi a guje ta nufi d’akinta ta saka masa key.

?????????????????????????

King kuwa tun lokacin da ya kashe fitilar d’akin be saurarawa tahee ba , sai da ya fanshe tsawan shekarun da yayi batare da shi ba , tun tana dukansa tana ihu har ta dawo ya kushi, still king ko gezau beyi ba aikinsa kawai yake yi baji gani, azabar da tajine tasaka duka ‘karfinta ta gantsara masa ciwo amma duk da haka kamar ba mutum ta cijaba, tun tana neman hanyar guduwa har ta kasa motsawa sai hawayen da yake bi mata fuska.

11pm lokacin da komai ya lafa tahee na kwance a jikinsa tana sakin masa kuka kad’an kad’an , shima kansa yasan ya mata lefi dan be raga mata ba amma ba lefunsa bane hakan , ha’kurinsa ya ‘kare bazai iya kasancewa babu ita ba , “ sorry sweetheart! I can’t hold it! Bazan iya jure rashin kasan cewa dake ba ! Am sorry please wannan kukan ya isa haka “, banza tahee tayi dashi sai ma ‘kara ‘karfin kukan ta da tayi , kamar da gaske yayi ‘ko’karin mi’kewa “ shikenan tunda bazaki ha’kura ba , bari nakira ummey ko abeey su zo su baki hakuri “, ‘karamun duka ta kai masa da ya sashi ‘kara rungumeta , cikin tsokana ya soma “ummey , oumma kuzo ku temakeni zai kasheni, abeey, taheer ya dena Sona “, ganin yana neman tona mata asiri yasa ta rungumeshi tana dariya , “ I love you “, cewar king, “ I love you too”, tahee ta mayar masa da amsa tana ‘kara rungumesa , sai kuma tayi saurin d’agowa “ JAMI’IN SIRRI ? Yaushe kazama? “ mayar da kanta yayi kan chest d’insa kafun shima ya bata amsa “ Long time ago!” Bata kuma cewa komai ba ta lafe a ‘kirjinsa Kawai tana sha’kar daddad’an kamshin turaransa , bayan sunyi wanka wani kayan ya saka mata duk yadda taso ta hanashi gudun kar Ammeey ta ganeta be kulataba , hatta guduwa da tasoyi ‘kin bari yayi , dole ta ha’kura tun tana magiya har bacci ya d’auketa a jikinsa .

Kiran sallah asuba ne ya tashe su gabaki d’ayansu, da Sauri tahee ta sakko daga kan gadon har saida king ya ri’kota, lumshash shun eyes d’inta da suke cike da bacci ya zuba mata , a hankali ya furta “ ina zaki?”, wai ina zaki, tasan halinsa da Sauri ta furta “ zan koma kaga bansa nayi bacci anan va , please “, gado ya nuna mata alamar ta koma ta kwanta ,zai ‘kara nuna mata bed ta fashe masa da kuka , gashin kansa ya shafa , kafun ya zuro ‘kafarsa ya nufi inda take “ oya goge hawayen ! Shiknn zaki koma amma da condition “, da Sauri ta furta “ na yadda “. Kanshi ya jinjina mata kafun ya d’aga ta gabaki d’ayan ta duk mutsu mutsun da take be sauketa ba har saida yashi toilet da ita . Acikin toilet d’in ma da kanshi yayi mata wanka ya hana tayi da kanta , sai da yaga jam’i na ‘ko’karin wuce shine yasa ya ha’kura ya ‘kyaleta, saida sukai alwala suka canza kaya tukunna kafin ya jata zuwa wata ‘kofa ta part d’insa bayan ya mayar mata da face d’inta ,har suka ‘karasa part d’in Ammey , anan d’in ma saida suka sha daru da yace zai d’auke ta , da ‘kyar ta Samu ta gudu, shi kuma ya dawo part d’insa kafun su tafi masallaci shida zaki.

Tana shiga part d’in Ammey kamar wata mara gaskiya ta yi Sauri shigewa d’akinta ,ganin babu Wanda ya ganta ne yasata sakin ajiyar zuciya , kafin ta cire face d’inta ta tayar da sallah, tana idarwa wani dad’i ne ya kamata , finally mijinta ya dawo gareta , tuno oummanta da taheer ne yasa ta sakin kuka kuma , sosai tayi kewarsu, ga kewar su junior ma da ya cika ta , amma duk da hakan bazata karaya ba , da Sauri ta mayar da face d’inta ta gyara ko ina na d’akin lokacin gari ya soma haske sannan tafito. Tana fitowa suka had’u da asabe tare suka soma ayyukan gidan .

Alokacin da tahee ta dawo part d’in Ammey sai alokacin ita kuma Ammey ta samu ta runtsa, sabida yadda ta kasa bacci , data kulle idanuwanta zataji wani irin kuka da gurnani yana biyota. A firgice zata bud’e idanuwanta ko addua bata tunanin tayi , tana bud’ew kuwa zataga wasu ‘kananun halitta na biyo ta gadan gadan, a rike zata mi’ke tayi ta ‘kwalla kiran neman agaji amma babu Wanda yake zuwa dan gabaki d’aya wannan ihun da take babu Wanda zai jita , a gabaki d’aya cikin Daren nan Ammeey bata runtsaba da tayi gigin yin bacci zataji saukar mari ko duka a jikinta, haka ta zauna zuru zuru kamar me ta’bin hankali , sai wajan sallah asuba abun ya lafa , take a Wajan wani wahalallan bacci ya d’auketa ko tunanin gaida uban gijinta batayi aranta.

*********
***************
Har Wajan 10 babu Ammey babu alamar fitowarta, ko ajikin tahee sai ma d’aki data koma taji a bincinta hankali kwance, kafun ta kwanta kwana daddad’an bacci ya d’auketa .

Cikin bacci taji an ta’bata da Sauri ta bud’e idanuwanta zata saka ihu ya sakar mata kiss abaki , cikin rad’a rad’a ya furta “ matsoraciya “ da Sauri ta tashi zaune tana sakin ajiyar zuciya , “ Ina Kwana “ , ta furta a hankali , amsa mata gaisuwar tata ba sai ma tanbayar da ya jefa mata “ me yasa kike kwana a ‘kasa ?”, ganin be amsa mata gaisuwar taba ne yasa ta d’an turo masa bakinta kamar yadda ta saba “ kawai banasan kwanciya akai , ni ban yadda da komai na part d’innan ba “, bakinta da ta d’an turo masa ya d’an ‘bille mata shi “ kika ‘kara turo mun bakin nan zamu ‘karayin second round , “ ta Sauri ta saka hannunta toshe bakinta , bece mata komai ba sai hannu daya sa ya jawo katifar daga inda take zuwa side d’in tahee. Ita kuma idanuwanta basu sauka ako ina ba sai a kan d’an tudun dake ‘kasan katifar , da Sauri ta tashi ta ‘karasa wajan, zata d’aga yayi saurin dakatar da ita shima ya ‘karaso wajan , d’an mat d’in da yake wajan ya yaye , wani Jan ‘kyalle suka soma cikin karo dashi, nuni yayi wa tahee da ta ja baya , Hakan kuwa ta faru tana ja baya yayi Bismillah tare da yaye jan gyallan, wani ramine ya bayyana cikinsa kuma tulune a ciki, bakin sa d’auke da adduar ya d’auko tulun, be ‘bata lokaci ba ya fasa tulun da aka nanna d’eshi da jan ‘kyalle , yana fasawa wata Jan laya guda biyu suka fad’o sai wani ‘karamun maciji da aka sossoka masa allura , zafi hannunsa ya soma kamar Wanda ake ‘konawa fata amma duk da hakan be hakura basai da ya kwance layar, gabaki d’aya sunan dada da ummey da abeey layar farko, alaya ta biyu kuma duka sunan abeey ne a cike da wasu irin rubutu, hatta macijin da aka sossoka wa allura sunan abeey ne a jiki, kallan tahee yayi kafin ya furta “ d’auko mun ashana “, da Sauri ta d’auko masa ashanar data d’auko kwana kin baya , bai damu da a inda yake ba , ya had’asu waje d’aya ya kunna musu wuta . Sosai wutar da soma ci ,sai ga wani sautin tass yafito da ‘karfi cikin macijin ya fashe wani ‘bakin ruwana na fitowa daga cike me wari. Sun dad’e suka ci a huta kafin gabaki d’aya su ‘bace batt babu su daga layoyin har randar da ya fasa da ‘kyallan, kanshi yaji ya fara sara masa , a hankali ya d’auko phone d’insa da ake kira , number uncle musaddiq daya ganine yayi picking call d’in bansan me aka ce masa ba sai mi’kewar da naga yayi , a hankali ya furta “ on my way “ sai kuma ya kashe kiran ya nufi hanyar ‘kofa da Sauri tahee ta kallesa , “ Ina zaka ?” Kallan inda ya ‘Kona abun nan yayi kafun ya maida kallansa kanta “ ina tunanin abunda na ‘konane yayi affecting Abeey, Ance yana cikin magana dasu uncle musaddiq ya fad’i , so I have to go “. Zan raka ka” girgixa mata kai yayi “ no ki zauna anan kinji “sai yayi pecking d’inta a baki ya bar d’akin. Yana fita tamayar da kallanta wajan da ya ‘Kona layoyin, kamar babu abunda akai , ajiyar zuciya ta sauke , Allah ya temaketa bata kwana akai ba , da Sauri ta gyara Wajan ta mayar da katifar wajan kamar babu abunda ya faru.
Ba’kin macijinnan kuwa da ya fashe me kwari be tsaya a ko ina ba sai a bakin Ammey a haka ya dunga shegewa bakinta tana bacci.

??????

Har bayan sallah azahar Tahee tana faman tsammanin zaman jiran king amma babu shi babu alamar sa , gashi babu waya a hannunta balantana tayi tunanin kiransa , tunanin taje part d’insa ne ya fad’o mata a rai, tana fitowa ta tarar da Ammey zaune kan kujera kamar mara lapiya harta d’an fad’a , saita nutsuwarta tahee tayi kafun ta ‘karasa cikin falon tana saka fake smile akan fuskarta , “Hajiya ina wuni”, shiru Ammey bata amsa gaisuwar da tahee tayi mata ba , akaro na biyu Tahee tana gaishe da Ammey , still bata amsa ba , sai akaro na uku da ta d’an kirata ne Ammey ta firgita sabida tunanin da ta fad’o, gabaki d’aya tayi zuru zuru, bata amsa mata da baki ba sai da kai kawai ta amsa mata ,itama tahee ko ajikinta sai ma ‘kara tanbayarta da tayi “ hajiya ko akwai abunda kike so ?”, nuni Ammey tai da tafi,har yanxu tana kan tunanin da ta fad’a tun safe ko abinci bata samu sa saka a bakinta ba . Itama tahee kamar wacce aka sa dole zata ‘karayi Mata magana ta daka mata tsawa “ nace banasan koma ki ‘bace mun dagani yanxu “ yadda tayi tsawar saida ta nemi tsoratar da tahee , juyawa tahee tayi zata bar wajan sukai karo dashi, ba Kayan d’azu ne a jikinsa ba ya canza , kamshin turaren sai shawagi yake cikin falour , sau d’aya ta kallesa ta d’auke kai ta nufi d’akin ta , sai dayaga wucewarta kafun ya lumshe eyes d’insa , kan d’aya daga cikin kujerun falour ya zauna yana bin Ammey da narkakkun idanuwansa masu wuyar fassara,kamar kullum saida ya daidaita kansa kafun ya furta “ Ammey?” Shima shuru bata amsa ba , sai a karo na biya da ya kira ta ta firgita dan yanxu magana kasan akai mata furgita take “ meke damunyi “, zaro masa ido ta fara , batasan ma amsar da zata Bashi ba gabaki d’aya , a rarrabe ta furta “ gajiya ce da kuma d’an ciwan kai da nake faman dashi “, gyada mata kai Kawai yayi dan ya gaji da saurarar muryarta , be jima ba ya bar falon batare da ya nemi inda tahee take ba.

Tahee kuwa a tunaninta zai biyo ta d’akin amma sai taji shiru , gashi bata da dalilin da zai da taje part d’insa tunda Ammey na falon, har akai sallahr la’asar sai faman fita take tana dubawa ko Ammey ta koma d’akinta , amma har yanxu tana falourn ba kamar koda yausheba da sai tayi wanka sau biyu ko uku, yau tun rigar data saka har yanxu bata cire ta ba. Ai akai sallah magariba , shiru bai sake dawowa ba , akayi isha’i shima still shiru , ko abinci tahee bata Ciba ta kwanta , ita kad’ai har bacci ya d’auketa , duk Wanda yaganta yasan ba jin dad’in baccin take ba .

8:30pm yashigo cikin d’akin ynxu ma ya canza kayan , ganin yadda take baccin a takure ga fuskarta kamar a had’e yasashi sakin murmushin da ya ‘kara masa kyau , gabaki d’ayanta ya d’auketa kamar wata baby , ko da zai fito saida ya kulle mata d’akin sannan ya nufi ‘kofar da yashigo , babu kowa a falourn shiysa yayi wuce warsa kai tsaye da ita a hannunsa , har shiga cikin palourn sa bata farka ba , yana ajjeta akan kujera ta bud’e idanuwanta , da Sauri ta Tashi zaune sai faman kunbure kunbure take kamar zata fashe , “ am sorry ai gashi yanxu nazo ko?” , ‘kin kulashi tayi ta nufi stairs , tana shiga d’akinta shaf shaf wanka tayi ta saka wata yar finginan rigar hutawa , dogon gashin kanta ma ta saka wa reborn, sannan ta saka wata hula me shegen kyau , tana Fito wa ta tarar dashi tsaye , yanxu ba mata kulashi ba , zata wuce ya janyo ya jikinsa , a kunne ya rad’a mata “ wifey ynxu da kin koyi fad’a ko d’azu na saka miki saban baby ne ?” Da Sauri tahee ta rungumeshi , ga wata kunya data kamata lokaci d’aya , “ ni ka bari banaso “, okay ki tsaya na kalleki ni banga wannan ba ai ko zaki mun nima ?” Duka ta kai masa kirji tana sakin dariya , a kan sofa ya zauna , kafun ya zaunar da ita akan cinyarsa, “ yajikin abeey ?”, saida ya lumshe idanuwansa kafun ya furta “ da Sauri , zuwa gobe zai dawo normal “, hannunta ta tusa cikin gashin kansa “ am sorry! Nasan ka yadda da ita sosai , ka dena ‘boye abunda ke cikin zuciyar ka ! You can always cry on my shoulder! Da wahala mutumin da ka yadda Dashi yaci amanarka! Kayi kuka please “, da Sauri ya kawar da zancen ta hanyar furta “ yunwa nake ji “, duk da taga yadda idanuwansa suka sauya be kuma cewa komai ba, shima bai kuma ce mata komai ba sai tray d’in da ya shigo dashi,” baki ci abinci ba , kina so ki mun azara ko ? Oya open your mouth “ a hankali ta bud’e bakinta ya saka mata gas meat d’in da ya d’akko , itama wani ta d’auka zata saka masa ya nuna mata fingers d’inta , fork ta ajje ta saka hannun, tana sa masa a baki ya rike hannun, saida ya sid’e abunsa tas sannan ya saki hannun , haka suka cigaba da jiyar da juna , sannan ya bata fresh milk, saida suka ‘koshi kafun ya d’auki babbynsa zuwa kan gado, yanxu ma duk gardamar da ta so yi be saurare ta ba . Ba ita ta koma part d’inta ba sai da akai kiran sallah asuba .

???????
Haka rayuwarsu ta cigaba da tafiya cikin farinciki kullum idan yazo ya d’auki babbynsa baya bari ta dawo sai bayan sallah asuba . Ammey ko damu da inda tahee take ynxu batayi sabida ita kanta a firgice take , duk dare idan tace zata kwanta bata iya bacci Sabida furgicin da yake haka ta bacci, kullum cikin dare haka zatayi ta ihu , tana neman temako amma babu alamar za’azo , ba ita take runtsa wa ba sai bayn kiran sallah asuba , shiysa king da tahee suke sharholiyarsu, yanxu bata damu ba dakanta ma zuwa part d’insa take duk lokacin da taso dan yawan cin lokaci a part d’insa take yini.

A gabaki d’aya basu zauna ba Sabida aikace aikacen da suke a part d’in ummey, har yanxu ummey bata ce mata komai ba , amma mimi ta sanar da ita komai , maganar yah moh ne da na junior kawai itama bata sani ba , haka suka ci gaba da aikace aikace Sabida gobe ba’kin da zasu zo , gobe mahma da sha’aban zasuzo, a gefe d’aya small mom da su zoya zasuzo, samreen ma a gobe zatazo Nigeria , ga dangin ango da zasu zo , dan abbey ya fad’a wa dady bikin ‘ya’yansane yana bukatar ganin kowa da ko kafun bikin. Tun lokacin da abbey ya suma , zuwa safiya ya farka ,tunda ya farka yake nuna wa ummey soyayya kamar lokacin da suke amare ko sau d’aya be tanbayi inda Ammey take ba , hatta dada tsawan lokacin nan kamar bata ta’ba wanzuwa ba , babu Wanda yake nemanta.itama Ammeey bata zuwa sbida wannan abunda yake faruwa da ita a cewarta sai ta nutsu ta saita kanta zataje wa abeey.

????GIDAN AUNTY ????

07041879581
MSS LEE

Back to top button