Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 16

Sponsored Links

Washegari talata Khadijah na ta share tsakar gidan da aka sa ta tayi tun asuba har lkcn bata gama ba Kawu ya fito cikin shiga ta alfarma da daya daga kayan mahaifin Khadijah, matansa sun rakosa xuwa balcony ana yi masa Allah ya tsare hanya, ganin Khadijah da yayi ya juya yana kallon matan nasa yace “Gobe er can ta shirya da safe xa a kai ta makarantar boko” Hajiya Maimuna tace “Wanda su Sumayya ke xuwa?” Wani kallo yyi mata yace “Ke xa ki biya, ko ina naga kudin biyan wannan makarantar, makarantar da yaran Bala ke xuwa xa a kai ta, ina jin ko a Jss2 aka ce take ko one” Khadijah ta mike tace “Aa jss2 nake Abba” Wani shegen kallo yyi mata yace “Kun ga irin rashin tarbiyar ko, kun gani ko, to yanxu wa ya sako bakinta, dama na samu labarin an baki tuwo ki ci jiya da daddare kin ki ci tunda kin taho da abinci daga gidan marigayi Muhd, to wllh xa ku yi aiki hand in hand da yunwa in har baxa ki ci abinda ya sauwwaka ba, baxa ki taho gidana kina min sangarta ba” daga haka ya nufi daya daga motocin dake tsakar gidan, Khadijah ta ci gaba da sharanta na yan koyo da take yi. Throughout haka ta dinga aikin da ba ta iya ba bata taba yi ba a gidan, duk ta gaji amma ko kadan bata ce haka ba sai turo baki da take ta yi, Hajiya Salaha ta kai mata dundu yyi sau biyar daga karshe ta gaji da bin ta tana mata dundun ta kyaleta, Hajiya Maimuna kuwa ta surfa mata xagi ya fi a kirga, duk wnn abun sai dai ta turo baki ko ta bata fuska daga nan kuma shkkn, kunu da kosai a gantale aka bata a cup, ita ma ta ci a gantale ta bar masu abinsu don ba saba ci tayi ba, sai da suka yi baccin rana sannan ta samu tayi sallahn zuhr ta lallaba ta kunna TV ta rage volume ta xauna tana kallo happily, dauke wutan da aka yasa ta turo baki, a hankali ta kwanta nan kasan parlon nan da nan kuma bacci ya dauketa don tun tashin asuba. Ko abincin rana ba a bata ba wai sai yaran gidan sun dawo, basa kuma dawowa sai karfe biyar, suna dawowa kuwa da yamma aka xuba ma kowa shinkafa da wake da mai da yaji da Hajiya Maimuna ta girka, Hajiya Salaha ta sa Sumayya ta xuba ma Khadijah don ita Hajiya Maimuna rantsuwa tayi baxata bata ba, khadijah ta tsura ma shinkafa da waken ido da aka barbada ma yaji, a hankali ta kai hannu ta dinga tsince waken tana ajiyewa a kasa gefenta, Hajiya Maimuna dake ta kallonta ta mike ta karbe kwanon abincin ta kai kitchen ta rufe, abincin da ba ta ci ba kenan har aka yi magrib sannan isha, tana ganin aka ba kowa shinkafa da miyar da Hajiya maimunar tayi amma ban da ita, bayan ta idar da sllh ta samu Sajida dake waya ta duka gefenta a hankali tace “Anty ni ba a ban shinkafar ba” ta mata wani kallo tace “Toh ni na dafa ki samu su Hajiya mana” mikewa tayi ta wuce dakin Hajiya salaha, ta samesu xaune da yaranta ana assignment, kallonta tayi tace “Lafiya??” ta girgixa kai tace “Ni ba a bani abincin ba ina jin yunwa” tsawa tayi mata tace “Fita ki ban waje, ba dai shayi da soyayyen kwai kike jira ba yunwa xai kashe ki gidan nan” a hankali Khadijah ta juya ta fita, ta tafi gun kwanciyarta ta rakube hade da rufe ido tana tuno Ummarta. Washegari kamar jiya da asuba aka tasheta, har gari ya waye tana shara, sai da duk yaran suka wuce makaranta sannan Hajiya maimuna tace idan ta ga dama ta wuce tayi wanka ta shirya, tsaye khadijah tayi a bathroom dake tsakankanin dakunan su Hajiya, soson wankan ta da Abbanta ya siyo mata daga Kasar waje ya xama na kowa da kowa hadda sabulunta mai tsada, ta turo baki ta dau sabulun kadai ta yi wanka da shi ta fito cike da kyankyanin bayin, tun da ta fito parlor Hajiya Salaha ke kallon kayan jikinta, khadijah ta durkusa gefenta a hankali tace “Na gama” tabe baki Hajiya salaha tayi ta nuna mata cup din kunu tace “Gashi can ki dauka, kosan ya kare” Khadijah ta leka cup din da sauri a xaton ta shayi ne, a hankali ta mike ganin ba shi bane ta isa gun cup din kunun ta dauka, Hajiya salaha tace “Ko yau ma baxa ki sha ba” bata ce komai ba ta dinga shan kunun da yyi mata tsami a baki tana d’an yamutsa fuska, sai hararanta Hajiya salaha take tana kwafa, daga karshe kadan ta sha ta ajiye ta mike tace “Na koshi” duk da uban yunwan da take ji cikinta na kugi, Hajiya Salaha tace “Toh ki hutar da kanki tafi ki juye a flask ki hada duk kwanukan ki wanke, kuma ki min irin na ranan in fasa maki jiki da wayar wuta” ita dai khadijah bata ce komai ba ta mike taje yin yanda tace nata. Wani almajirin Kawu ne ya taho kai ta makarantar, shegen nisa ce da makarantar kuma almajirin me suna musa yace da kafa xata dinga xuwa kullum don haka gwara ta dinga kallon hanyar da kyau, tunda suka shiga makarantar Khadijah ke kalle kallen ko ina, don ita dai bai yi mata kama da schl ba, gashi ko plaster ba ayi ba, yaran ma basu da yawa, Musa ya shiga gun wani wanda da alama shugaban wajen ne, ita tana tsaye waje, tana jin mutumin na ce ma musa ai lesson ne wa yaran da basa gane karatu, kuma na shekara daya ne kafin yaro ya shiga boko, musa ya tambayesa nawa ne yace dubu uku da dari biyar, nan take musa ya basa kudin, ita kuma aka kira wata daliba ta kai ta ajin karshe musa ya wuce, su kusan goma ne a ajin, ita dai tunda ta shiga ajin take kallon malamin dake ta koya sentence making, “The boy was tall…” Shine abinda malamin ke ta nanatawa yaran na fadi su ma, khadijah dake ta kallon sa tace “Excuse me, but you said present tense sir?” Malamin yace “Yes” tagumi tayi tace “Sorry but that’s past tense class master” kallon board din yyi da sauri sannan ya kalleta, bai kulata ba ya ci gaba, nan ma kuma sai da ta sake masa gyara, hade rai yyi yana kallonta, can ya basu classwork ya koma ya xauna, sai bayan kusan minti sha biyar ya karba sannan ya fara koyar da Multiplication a board, sai da ya gama tas, sannan ta kai masa gyaransa a littafi tana nuna masa, fita malamin yyi xuwa gun shugabansu, ba a dau lkci ba ya kirata, tana tsaye yace “Ke tunda baki da kunya kar ki sake xuwa makarantar nan daga yau, tunda kin iya abinda ake koyarwa ki xauna a gidan ku ko kuma a kai ki school ga kudin ku” karba tayi tace “Ohk, in tafi yanxu” yace “Tafi” juyawa tayi ta fice daga uncomplete building din, gano gida bai mata wahala ba saboda sharpness dinta, su Hajiya salaha dake xaune parlor suna hira suka saki baki suka ce me kika dawo yi, tace “Ba abinda suka iya fa a wajen, they are just teaching rubbish, ni bana son wajen school nake so, am in jss2” Hajiya maimuna tace “Shine kika dawo” gyada mata kai tayi ta mika mata kudin hannunta, ta tafi jikin kujera ta rakube ta xauna, duk suka bi ta da kallo baki sake. Yunwa sosai take ji amma bata ce komai ba, Kawu ne ya fito a shirye xae fita wajen karfe goma da rabi, ganinta yace “Wannan yarinyar musa bai kai ta makarantar bane” Hajiya salaha tace “Uhn gata nan ya kai ta ta dawo wai bbu abinda suka iya kilan mai tsada take so” ya juya da sauri yana kallonta yace “Me ya dawo da ke?” Tace “Abba they are teaching rubbish there, kuma ina ta correcting dinsa, ban san whether he reported me bane, sai aka kira ni wai in tafi kar in sake dawowa, har da kudin ma an bani na dawo da shi” Kawu ya gyara tsayuwa yana gyada kai yace “Ohhhw haka aka yi kenan, toh kin ma kanki, Alhmdllh Muhd baxae gan ni da ko wani laifi ba don na kai ki makarantar kika gudo, don haka sai kiyi ta xama gidan” daga haka yyi ficewarsa, ita dai bata ce komai ba, Hajiya Maimuna tace “Wato ke isassa kin raina makarantar shine kika je kina ma malaman fitsara ko, uban wa ke da kudin asaran da xai kai ki irin makarantar da ubanki ya sa ki tun farko?” Khadijah dai sai kallonta take, Hajiya Salaha tace “Ni da nace xan fara awaran siyarwa xan dauko mai aiki wllh da Alhaji xai yarda da sai ta dinga kai min can bakin kasuwa, kinga ai ba talla bane wnn, xama waje daya xata yi” Hajiya Maimuna tace “Ae ko da xai yarda nima sai in hada mata da Omon siyarwa na” Hajiya salaha tace “Toh bari ya dawo dai mu ji” suka gama dai hirarsu duk suka shiga dakunansu domin kwanciya suka bar ta ita kadai a parlorn ga yunwa dake dawainiya da ita, da rana yau kam taliya da wake suka girka, gashi ita bata cin wake tun tana karama, Hajiya salaha ta dan yarfa mata a kwano ta bata, kamar xata yi kuka tace “Ni ban iya cin wake ba” Hajiya salaha tayi er dariya ta mayar da abincinta cikin tukunya ta fito kitchen din, sai a sannan khadijah ta fara hawaye don tunda take bata taba jin yunwa irin wannan ba, ita shinkafa da miya take so, tsakar gida ta tafi ta xauna tana share idonta, har wani rawa jikinta yake don yunwa, tashi tayi ta fice gidan gaba daya, ta shiga gidan dake kusa da na kawunta, gidan shigen na kawunta ne, taga wani yaro xaune tsakar gida yana cin tuwo da koren miya, fita tayi da sauri har tana tuntube, gidan dake kusa da wannan ta tura ta ji a kulle, haka na kusa da shi ma, a gida na hudu ta tsaya tana kallon babban gidan don ya fi duk gidan anguwar, tura gate din tayi taji a bude ta shiga tana kallon mai gadin ta gaishesa yace “Wa kike nema?” Ta nuna masa cikin gidan sannan tayi wucewarta, har ta isa balcony kallon karen dake cikin cage a gidan take, ta murda kofa a hankali ta shiga parlorn, tsaye tayi bakin kofar ganin wani matashi da baxai wuce shekara ashirin da shidda ba yana xaune parlorn da plate din abinci a hannunsa idonsa a kan tv, yana kallonta da dan mamaki yace “Wa kike nema” ta kalli abincin hannunsa kamar xata yi kuka a hankali tace “Nobody, I am just hungry” ya buda ido kamar ya ji mugun abu, a hankali tace “Please” ajiye plate din hannunsa yyi yace “Take” ta karaso ciki da sauri ta xauna kan kafarta tana kallon shinkafa da miyar da naman kaza sai coslow dake gefe murya can kasa tace “Thank you” daukan spoon din tayi ta kai abincin baki ta fara ci, ya kafeta da ido irin kallon mamaki, muryar wata dattijuwa taji tace “Who’s this?” Ya juya ya kalleta kafin yace komai Khadijah tace “Good afternoon ma.. I am khadijah” matar ta kasa cewa komai, ta kalli yaronta dake xaune kamar yanda shi ma yake kallonta, Khadijah ta dau kazar abincin tana ci tana kallon matar.

*Haske writers association*💡

✨ *Noor-Al-Hayat*✨

Back to top button