Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 21

Sponsored Links

Littafin Noor-Alhayat na siyarwa ne kindly patronize ur writer and read happily_

Aliyu ya d’an bude ido ya kalli Mum dinsa sannan small mum da ta hade rai, mumy tace “Toh ka ji, she didn’t notice” karasawa khadijah tayi ta dauke cup din ta nufi kitchen da aka nuna mata tana yi tana kallon TV har ta isa bakin kofar shiga, kin shiga tayi ta makale da bango tana kallon TV din, haka Mumy ta saki baki tana kallonta, ta kusa minti daya sai kuma ta juyo a hankali ta saci kallonsu, hada ido suka yi da Aliyu dake kallonta kamar yanda mahaifiyarsa ke kallonta ita ma, boye fuskarta tayi da hannunta da sauri tana yar dariya ta shige kitchen din, mikewa Aliyu yyi ya tabe baki yace “Lallai” sannan ya wuce sama, small mum dinsa ta mike tace “Kai fa kasan lallai, ni ban san me yasa Anty fatima take jajibe jajibe haka ba, ni abun ya isheni wllh” daga haka ta bi bayan Aliyu, Mumy dai bata ce komai ba, khadijah na ajiye cup din ta fito ta taho gun mumy ta durkusa gefenta a hankali tace “Anty naga remnant din fried potato and egg, and I am very hungry please can I take it?” Mumy ta gyada mata kai kawai tana kallonta, murmushi khadijah tayi tace “Thank you very much ma” daga haka ta mike ta wuce kitchen din cike da murna, ta dau dankalin da kwai ta xauna a nan kitchen din ta tankwashe kafarta ta fara ci tana lullumshe ido, a nutse take cin abincin kar ma ya kare ta fi minti goma a haka taji an shigo kitchen din, daga kai tayi tana kallon waye ta ga mutumin daxu ne, tun da ya kalleta sau daya bai sake kallonta ba ya nufi gun da mugs suke a ajiye, Khadijah ta bi sa da kallo tace “Are you a medical Dr?” Juyowa yyi da sauri ya kalleta, ta wara masa manyan fararen idonta tana cin dankalin bakinta, ya daure fuska yace “Am I ur mate that u are asking me dat?” Ta girgixa kai da sauri tace “Not at all…. I just…” Sai kuma tayi shiru ta debi kwai ta kai baki, coffee ya hada ya xuba madara da sugar cube daya, tana ta kallon mug din ganin xai fita tace “Please can you give me some of ur tea” Juyowa yyi fuska daure yana kallon ta, tayi saurin sunkuyar da kanta tace “Ohk ohk sorryyy” har ya isa kofa sai kuma ya dawo ya dau wani cup ya xuba mata kusan rabi ya bude coffee powder ya debi rabin tea spoon ya kara xubawa a nata ya jujjuya sannan ya dauka ya mika mata yace “Here” wara ido tayi ta karba tana murmushi tace “That’s kind of you, thank you” ko kallonta bai yi ba ya fice daga kitchen din, haka tayi ta hura shayin tana jira ya d’an huce ta sha, tana sipping din kadan ta mike a gigice tana neman kofar fita jin daci sosai, wani kofar da ta gani ta bude ta fita da gudu, bakin tap ta ga kyauta tana wanke kayan ciki, ga kifi ta gama wankesu a gefe, har da naman kaza a ajiye, khadijah ta tofar da ruwan shayin bakinta tana yatsine fuska ta nufi gun tap din tace “Dan Allah Anty xan sha ruwa kadan” matar ta kalleta fuska daure tace “Me kike yi a kitchen?” Khadijah na ci gaba da yatsine baki tace “Ina cin potatoe and egg ne” sake wukan hannunta kyauta tayi tace “Uban wa ya baki?” Khadijah ta bude hannu tace “Antyn dake parlor tace in dauka in ci, har na kusa cinyewa ma” Kyauta ta tsuke fuska tace “Mayya, wuce ki ban wuri, kuma kafin in shigo ki wanke kayan wanke wanken dake kitchen din nan, da gani a yunwace kika xo dama” Khadijah ta juya ta bar wajen ta koma kitchen, karasa cinye dankalin tayi ta ajiye plate din da cup a sink, coffeen kuma ta rufe sannan ta fito parlor, Mumy dake xaune har lkcn ta nuna mata jakar kayan ta tace “Ki dau jakar nan ga daki can ki kai ki ajiye” Mumy ta fada tana nuna mata dakin dake parlorn, khadijah ta xaro ido tace “Anty kayan fa sun yi datti sosai they are not washed, they are even smelling” Mumy tace “Me yasa baki wanke su ba toh?” Ta langwabar da kai tace “Ni ban iya ba Anty, I only use to wash plate” mumy dake ta kallon ta tace “Toh dauka ki kai su can waje ki ajiye” tace “Ohk ma” daga haka ta dau jakar ta fita da shi can waje, ta dawo, xaunawa jikin kujera kusa da Mumy tayi tana kallon wani program da Mumy ta sa, a hankali tace “Anty bakya kallon cartoon?” Kallon ta mumy tayi, tayi murmushi kafin ta canxa channel din xuwa cartoon, happily khadijah tace “Thank youuu” Mikewa mumy tayi ta wuce sama, Khadijah ta gyara xaman kallon cartoon, a haka Kyauta ta fito daga kitchen ta ganta, daure fuska tayi tace “Ke dan kaza kazan ki ba wanke wanke kwanukan dake kitchen nace kiyi ba kika taho nan kina kallo?” Khadijah ta bata fuska tace “Plss xan yi, ina son in gama wannan cartoon din ne, I have never watch it before” Kyauta ta bude baki da mamki, tana son kara tabbatar da anya ta ji xancen su yakumbo da Hajiya sosai daxu kuwa, ita dai kamar ji tayi ance aiki yarinyar nan xata yi, ko dai bata ji dai dai bane? Khadijah ta turo baki ganin Kyauta taki tafiya, ta nufi kitchen din tace “Toh naji xan wanke” daga haka ta bi gefenta ta shiga kitchen din, kyauta tayi kwafa ta fita don ba ma driver sakon da xai siyo mata na farfesun da xata yi, Khadijah na wanke cups din a kitchen cikin sink trying hard bata xubda ruwa kasan kitchen din ba a hankali take wanke wanken, Aliyu ne ya shigo rike da mug din daxu, tana ganinsa ta tsuke fuska, shi kam bai kara kallonta ba ya ajiye mug din xai fita tace “Wait” da kamar baxai tsaya ba sai kuma ya tsaya ya juyo, cup din da ya bata coffee daxu ta dauko ta cire murfin ta taho gabansata daga kai tana kallonsa tace “You didn’t tell me that it was medicine u made…. I wouldn’t have ask for some” kallonta ya tsaya yi, xata kama hannunsa ta sa cup din da sauri yace “Ke xan mare ki fa” turo baki tace “Toh ni nace baxan sha ba is it by force” mika masa ta kara yi, ya dauke kai yyi murmushi yana shafa beard dinsa, kallon sink yyi yace “Toh xubar” ta xaro ido tace “How? Why? For what reason? Why shud I throw it away? Ummata told me that they are consequence of throwing food away” shafa kansa yyi ya karbi cup din ya karasa sink xai xubar ta rikosa da sauri ya buge mata hannunta, ta bata fuska xata yi kuka, kusan rabi ya xubar ya nufi inda kayan shayi suke, ya kara madara ya xuba Milo da sugar cube uku ya kara ruwan xafi a ciki ya juya sannan ya mika mata, ta wara ido da sauri tace “For me?” Ya hade rai tayi saurin karbewa cike da murna tace “Thank you very much” dai dai nan kyauta ta shigo kitchen din, tayi kasa da kai tace “Sannu da xuwa yallabai, ina kwana” yace “Lafiya lau” daga haka ya fice kitchen din, khadijah ta nemi waje ta xauna ta tankwashe kafa ta fara shan shayin idonta lumshe, muryar kyauta taji tana cewa “Kee shine ya baki shayin nan?” Ta bude ido da sauri tace “Ehh” kyauta ta hade rai ta karasa ta ja kunnenta tace “Idan kina shisshige ma yan gidan nan sai na ci kaza Kazan ki shegiya kawai” khadijah ta ci gaba da shan shayin ta bata ce komai ba. Kyauta ce ta karasa wanke wanken tana gunguni khadijah sai lekota take ta cikin cup ta take shan shayin ta, Mumy ce ta shigo kitchen din tana kallon kyauta tace “Kin bada sakon da nace kyauta” cike da ladabi kyauta ta bar wanke wanken tace “Ehh Hajiya” Mumy tace “Ohk, ina yarinyar nan take” kyauta ta nuna mata khadijah, Mumy tace “Ohk, idan ta gama ki turo ta ta xo ta amshi sabulu a sama tunda akwai omo a nan ki nuna mata yanda xata wanke kayan ta ga su can a waje wai masu daud’a ne” Kyauta tace “Toh Hajiya” daga haka Mumy ta wuce, Kyauta ta balla mata khadijah harara tace “Maxa ki gama kije ki amso, ni dai bbu wanki da xan maki” khadijah ta karashe shanyewa ta nufi gun sink ta ajiye cup din xata fito kyauta ta fixgota tace “Maxa wanke ni xan wanke maki?” Turo baki khadijah tayi ta fara wankewa a hankali kyauta ta kwace cup din tace “Tafi sama ki karbo min sabulun bbu abinda kika iya wllh” Khadijah ta juya ta fita ta wuce sama, tsaye tayi corridor tana kallon doors dakunan, ko wani daki na da taxara sosai daga na kusa da shi, aka bude wani kofa sai ga Anty khadijah, tana ganin khadijah ta hade rai tace “Ke me kike yi a nan, maxa sauka ance maki masu aiki suna hayowa nan ne” a hankali khadijah tace “Am sorry, Anty ce tace in xo….” Tsawa Anty khadijah ta mata tace “Maxa sauka shegiya” Mumy ce ta bude kofa ta leko tace “Ohk ni nace ta taho ta karbi sabulu khadijah” Anty khadijah ta hade rae tace “Kai Anty ki daina haka wllh ba shi da amfani ina kika taba ganin ana haka ma dai tukun, baki ganin yanda kawayenki suke da masu aiki ne, shegun ka ja su jiki su cuce ka kawai” mumy bata ce komai ba ta shiga ciki ta fiddo wasu sabulu masu tsada ta mika ma khadijah tace “Ki kai ma kyauta” khadijah ta karba ta juya, Anty khadijah tace “Ko da wasa kika sake hayowa nan wllh sai na mareki ko da kuwa Hajiya ce ta aike ki….” Khadijah dai bata ce komai ba har ta sauka, Kyauta ta kwace sabulun suka fita, bakin tap ta xuba duk kayan a roba tana yatsine fuska ta xuba ruwa da omo tace “Maxa taho ki wanke tsummokaran ki shegiya” Khadijah ta xaro ido tace “Kai Anty ban iya wanki ba fa” dagowa kyauta tayi da sauri tace “Toh uban wa xai maki” khadijah ta bude hannu alamar bata sani ba, kyauta ta dinga masifa tana jaraba ta shiga wanke kayan khadijah na tsaye tana kallonta, tas ta wanke su gaba daya tayi ta dauraya, khadijah dake ta tsaye tace “Anty in je in dinga yin shanya?” Kyauta tace “Ja can, warce bata iya wanki bace xata iya shanya” khadijah dai bata ce komai ba, kyauta tace “Ni dai da ki tafi ki ban waje in daina ganin ki” Khadijah tace “Toh Anty” daga haka ta wuce ciki da sauri taje ta ci gaba da kallonta, xaune ta samu Anty khadijah a parlor Aliyu na xaune kusa da ita sanye da 3qtr da farin riga yana nuna mata abu a laptop, tana ganin khadijah ta yi mata alamar da ta koma inda ta fita fuskarta daure, ganin Anty khadijah tayi shiru Aliyu ya daga kai yana kallon inda take kallo, dai dai lkcn da khadijah ta juya da sauri ta koma kitchen din, Anty khadijah tayi tsaki tace “Gayyar tsiya” shi dai Aliyu bai ce komai ba yana ci gaba da danna laptop dinsa, Komawa gun kyauta Khadijah tayi, kyauta ta hade rai tace “Dawowa kika yi?” A hankali khadijah tace “Wannan Aunt din ce ta koreni” Kyauta ta tabe baki tace “Wannan aikin ai sai khadijah baxawarar gidan, warce ta fi matar gidan xakewa, ta ki xaman aure ta xo nan duk ta gallabe mu da su Usman, ai sai ki je ga dakali can ki xauna ya kika iya” tafiya khadijah tayi ta xauna tana kallon kyauta dake ta daurayan kayan ta.

Kyauta ta gama shanyan kayan ta dau sabulun da ya rage ta mika ma khadijah dake ta xaune a gun da ta nuna mata tace “Kina shiga parlor xa ki ga wani kofa, maxa ki shiga ki ajiye sabulun nan saura kuma ki min tabe tabe nasan yanda na ajiye komai na” tashi khadijah tayi ta karbi sabulun ta wuce ciki, ta kusa minti daya tsaye bakin kofar kitchen tana lekan parlorn don har lkcn Anty khadijah na nan, tun xuwanta wajen Aliyu ya ganta, da sun hada ido sai ya dauke kansa, can dai small mum din tasa ta mike tace “Xan tafi in kwanta Son” yace “Alright” daga haka ta wuce sama, sai a sannan khadijah ta shigo parlorn tana taku a hankali ta shiga kofar da kyauta ta ce mata, kare ma dakin kallo ta dinga yi, komai fes fes kamar ba dakin mai aiki ba har da gado a dakin, khadijah ta ajiye sabulun tsakiyar dakin sannan ta juya ta fito, gun Aliyu ta nufa ta tsaya kusa da shi tana kallon laptop din kafarsa tace “Kasan me?” Ko kallonta bai yi ba idonsa a kan laptop din, tace “Nima ina da laptop da Abbana ya siyo min ah….” Shiru tayi tana kallon sama tana son tuna sunan kasar, ta langwabar da kai tace “May be it’s china! kuma na iya operating laptop din amma kawu ya amshe min” kamar xata yi kuka ta kare maganar, ya dago kai ya kalleta yace “Na tambaye ki?” Dariya ta yi har da rufe fuskarta tace “A’a kawai gaya maka nake yi” yace “Toh juya ki bar nan” Dai dai shigowar kyauta parlon, ganin Aliyun tayi kasa da kai tace “Sannu yallabai” yace “Yauwa sannu da aiki” Kyauta ta shiga dakinta, ya kalli khadijah yace “Wuce ki ban waje” ta buda ido tace “Ohk” daga haka ta bi kyauta dakinta, kyauta dake kokarin ajiye sabulun da khadijah ta yasar mata a tsakiyar dakin ta juya ganinta ta rufe kofar dakin, sannan ta ja kunnenta tace “Ba nace ki daina ma mutan gidan nan shisshigi ba, ke wani irin kunnen k’ashi gare ki, me ya hada ki da likitan har xaki je ki tsaya gabansa?” Khadijah ta turo baki tace “I was just telling him about my laptop” sake baki kyauta tayi tana kallonta, can ta dungureta tace “Sannu baturiya, you dey tell am about ur laptop koh? Wai ma ina iyayenki?” A hankali khadijah tace “They are late?” Kyauta tace “Wa ya kawo ki gun aiki?” Khadijah ta langwabar da kai tace “Wata mata ce, she is very wicked” kyauta ta rike ha6a tana kallon khadijah, muryar Hajiya taji tana kiranta a parlor ta juya da sauri ta bude kofar ta fita khadijah ta bi bayan ta, Hajiya dake tsaye tace “Kyauta white rice kawai xa ki yi da miya for lunch, pepper soup din da xa ki yi kuma na dinner ne idan kinga xaki iya yi yanxu kiyi, idan baxa ki iya ba ki bari da yamma” kyauta ta risina tace “Toh Hajiya” Mumy ta juya ta koma sama, Aliyu dake parlorn har lkcn yace “Mumy baxa ki aiki ba yau” Tace “A’a sai gobe” Kyauta ta shiga kitchen Khadijah na biye da ita, Ruwan shinkafar ta daura kan gas, duk inda ta bi a kitchen din sai khadijah ta bi ta, gajiya da karon da suke ci Kyauta tayi ta fixgota ta nuna mata kofar fita kitchen din tace “Tafi ki ban waje baki min ko wani amfani a nan” da sauri khadijah ta fita kitchen din, bbu kowa parlorn haka yasa ta dau remote da sauri ta canxa xuwa cartoon, ta rakube kasan kujera tana kallo, kafin karfe daya Kyauta ta gama shinkafa da miyar ta fito parlor, dai dai sakkowar Anty khadijah downstairs, tun a stairs ta bude baki tana kallon khadijah da gaba daya hankalin ta na kan TV, kyauta na ganinta tayi kasa da kai xata koma kitchen ta kwalo mata kira, sai a sannan khadijah ta mike da sauri, cike da isa Anty khadijah tace “Ba ki gaya ma yarinyar nan rules din gidan nan bane kyauta?” Kyauta tace “Ban kai ga gaya mata ba Hajiya, tun daxu ina kitchen ne da na san nan ta xauna kallo da baxan barta ba kiyi hakuri Hajiya” Anty khadijah ta kalli khadijah fuskarta daure tace “An ce maki nan din gidan ubanki ne da kika taho kika hakikance a parlor kina kallo a matsayin ki na mai aiki da aka dauka yau” khadijah tayi shiru bata ce komai ba, a tsawace Anty khadijah tace “Ba magana nake maki kike kallona da shegun idanuwanki ba” Kyauta tace “Kiyi hakuri Hajiya hakan baxai kara faruwa ba idan Allah ya yarda” Anty khadijah tace “Halan baki san ita ma aiki aka dauketa ba da xaki bar ta tana kallo ke kuma kina ta aiki a kitchen, ina ce tare ya kamata ku yi aikin ba?” Kyauta ta risina tace “Kiyi hakuri naga yarinya ce Hajiya” Wani kallo ta jefeta da shi tace “Yarinya? Ai iyayen nata sun san yarinya ce suka kawo ta gidan aiki, maxa idan akwai wani aikin ki bata ta tafi taje tayi yanxu, daga yanxu kuma bana son sake ganin kina aiki ita tana xaune” kyauta ta juya da sauri tace “Toh Hajiya” bin bayan ta khadijah tayi, Anty khadijah ta dakatar da ita tace “Daga yau na sake ganin ki xaune cikin parlorn nan wllh sai na lahira ya fi ki jin dadi gayyar tsiya kawai” A hankali khadijah tace “Am sorry maa” daga haka ta bi bayan Kyauta da sauri. Kyauta ta fixgota bayan sun shiga kitchen din ta ja kunnenta tace “Kin ga xaki fara ja min matsala koh? Da nace ki wuce daga kitchen ce maki nayi kije kiyi kallo??” Khadijah ta girgixa mata kai kamar xata yi kuka, kyauta ta nuna mata can wani gefe tace “Tafi ki je ki xauna wawiya kawai, dole ne sai kin yi kallo har wancan baxawarar xata dinga maki gori bata san at times condition ke sa crayfish yyi bend ba, banda haka uban me xai kawo mu gidan nan” khadijah tayi dariya har da kyakyatawa tace “Anty is crayfish bent?” Hararata kyauta tayi ta juya ta ci gaba da abinda take, a dinning kyauta ta jera lunch din duk me son ci a can xai je ya diba, ta dau wani katon roba ta kusa cika sa da shinkafa nama yayi takwas ta fita parlor tana leke leke, dawowa tayi da sauri ta mika ma khadijah tace “Maxa maxa tashi ki kai dakina da sauri ki ajiye a bayan kofa ki rufo dakin” khadijah ta mike ta karba abincin ta fita da sauri, har xata shiga daki ganin Aliyu ta tsaya, sai kuma ta nufesa har gun stairs tana nuna masa abincin ta tabe baki tace “Kaga Anty mai girki tace in kai mata abincin nan daki da sauri, may be she fetched all the food kila har da kai ma baxa ka samu ba, cos there is nothing left in the pot, I even saw when she was pouring water inside” Aliyu ya rungume hannunsa ya hade rai yace “Where did u knw me from?” Tana rike roban abincin da kyau saboda tiririn da yake innocently tace “In this house mana, I….” Turata yyi baya da sauri har sai da ta kusa faduwa shi ma ya koma baya ganin ta sake roban hannunta gaba da uban shinkafa da miyar da nama suka tarwatse kasan tiles har kan stairs, ta xaro ido ta toshe baki kamar xata yi kuka tace “Shikenan ka xubar… wllh bani bace ba kai ne ka xubar, ka xubar ma Anty mai girki abinci….” Kyauta ta fito da gudu daga kitchen jikinta na rawa jin karar faduwar roba kamewa tayi gun ganin khadijah can bakin stairs ga tulin shinkafa a xube kasa, xata koma kitchen suka yi ido hudu da Aliyu ta sake dawowa da gudu bakinta na rawa tace “Subhanallahi ta xubar, ban san baxata iya ba dama nawa ne da nata da nasu Usman…” Khadijah ta daga hannu da sauri tace “Noo Anty mai girki bani bace ba fa, shine ya turani baya kawai abincin ya fadi a hannuna” Aliyu ya tsallake abincin ya bar wajen, Kyauta ta koma kitchen da gudu ta dauko wani karamar roba ta dawo ta dinga kwashe shinkafar tana xubawa a babban roban, khadijah tace “Hope u are nt eating this any longer?” ko kallonta kyauta bata yi ba ta gama kwashe abincin ta kai dakinta da gudu ta fito ta shiga kitchen ta fito da sweeper, cikin yan mintuna ta gama gyaran gun ta goge, sai a sannan ta mike tana hararan khadijah tace “Ae yau sai dai yunwa ya kashe ki gidan nan, ba dai ni kika yi niyyar toxartawa ba? Yanxu da baxawara ce ta sakko ba bawan Allahn nan ba ya xan yi da raina?” A hankali khadijah tace “Kiyi hakuri” kunnenta ta ja tace “Baxan yi ba, sai kin gaya ma yan garin ku da yunwar cikin ki yau, little brat kawai” daga haka kyauta ta koma kitchen da sauri, khadijah ta langwabar da kai ta bi ta da kallo. Da kyar khadijah ke cin shinkafar tana yi tana kallon shi da kyau ko xata ga dirt a ciki, kyauta sai hararata take tana ci hankali kwance, Khadijah tace “But Anty mai girki me yasa baki xuba mana wani ba?” Kyauta tace “Kika sake ce min Anty mai girki sai na kalla maki mari, Anty mai girkin gidan ku, nace idan baxa ki ci ba ki dau naman ki tashi ki ban waje ni xan iya cinyewa, kila ma gidan da kika baki samun irin wannan xaki xo nan kina min iyayi” Khadijah ta xaro ido tace “The woman is always cooking concoction there, bata taba irin wannan abincin ba” Kyauta tace “Toh ki rufe min baki ki ci abinci yanxu yaran gidan xa su dawo daga makaranta” khadijah tace “Ohk” Jin shigowar mota kyauta ta bar ma khadijah sauran abincin ta mike da sauri tace “Toh gasu can… Idan kin cinye ki fito da roban kika kai kitchen” daga haka kyauta ta fita, yara uku ne suka shigo parlorn sanye da kayan makaranta daya kamar khadijah take tana jss3, daya kuma na ss1, babban cikinsu na ss2, khadijah ta fito rike da sauran abincin ta tsaya bakin kofa tana kallon yaran, Gaba daya dinning suka nufa ko wacce na cewa “Yaya ina yini?” Aliyu dake xaune gun ya amsa masu gaba daya, bbu warce ta gaida kyauta dake ta masu sannu da xuwa duk suka wuce sama, banda yar karamar cikinsu sa’ar khadijah, Kyauta ta washe baki tace “Yauwa sannu Anty khadijah ya makarantar?” Yarinyar da ita ma sunanta khadijah tace “Alhmdllh, kyauta who is that girl staring at us?” Kafin kyauta tace komai khadijah ta turo baki tace “I am not staring at you…” daga haka khadijah ta shige kitchen da roban hannunta, duk wannan abun Aliyu na kallonsu daga dinning, yarinyar ta juya da sauri ta tafi gunsa tace “Ya Aliyu who is she?” Ya kamo hannun Kanwar tasa yace “Ask mumy” yarinyar tace “Ohk” daga haka ta wuce sama kyauta na cewa ta na cire uniform tayi sallah ta xo ta karbi abincinta, kyauta ta bi khadijah kitchen ta jawota fuskarta daure tace “Ke fa ba ruwanki da yaran gidan nan naga har kin fara masu fetsara, ki tsaya a matsayin ki idan ba haka ba baxawara ta ishe ki”

Back to top button