Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 26

Sponsored Links

Shirin tafiya islamiyya suka yi bayan sun ci abinci, tun da Khadijah ta fito sanye da uniform din islamiyya Siyama ke ta harararta, kyauta da ta lura da hakan ta ja Khadijah kitchen tace “Kafin su gama iskancinsu da harare harare tafi gun Sanusi ki jira a gun motar” Khadijah ta fita ta tafi gun da motar yake ta tsaya, Aliyu ne ya fito baby na biye da shi a baya ita ma ta shirya, Baby tace “Yayanmu kenan baxan je mu taho da Daddy ba?” Yana bude motarsa yace “Ai islamiyya xa ki baby” ta bata fuska tace “Yaya yau kadai xan yi fashi fa” yace “Bulalan da xa a maki fa?” Tace “Ae cewa xanyi bani da lafiya sai ka rubuta min medical report in kai” yace “C’mon wuce ki shiga mota ku tafi makaranta my frnd… Bakin ki kamar medical report” Juyawa tayi kamar xata yi kuka ta tafi gun Khadijah dake kallonsu, ya shiga motarsa ya bar gidan. Karfe shidda da ‘yan mintuna suka shigo gidan daga islamiyya, wani saurayi ne xaune parlorn shi kadai yana danna laptop, ba can suke kama da Aliyu ba amma kana ganinsu kasan yan uwan juna ne, su siyama suka yi kansa cike da murnar ganinsa, siyama ta rungumesa tace “Wllh nayi kewarka ya salim, wai don Allah yaushe Yaya Aliyu xai tafi duk ya takura mu gidan nan, the house is just boring with him, idan Abba xai koma ya tafi da shi ya bar mana kai plss, Allah ya Aliyu is a problem in this house ko irin d’an birthday din frnds da party ya hana mu xuwa daga boko sai islamiyya” kamar xata yi kuka ta kare maganar, shi dai saleem sai uhn, uhm yake ta cewa yana sunkuyar da kai, sum sum Aneesah ta wuce sama, hakan yasa siyama ta bi parlon da kallo ta ga ya Aliyun xaune dinning yana kallonta, dauke kai tayi da sauri ta toshe baki tana xaro ido tace “Na shiga uku” Saleem ya dinga dariya kasa kasa har da kyakyatawa ba tare da ya kalli direction din Aliyu ba, Khadijah dake tsaye ita ma ta rufe fuskarta da Hijab ta wuce dakin kyauta tana murmushi, bin ta da wani kallo saleem yyi da wani expression yace “Who’s this?” Siyama ta yamutse fuska tace “The new housemaid after kyauta….” ya buda ido yace “What” tabe baki tayi ta mike tana satan kallon Aliyu tace “Sannu da gida yayanmu” kallon fork din gabansa yyi ya dauka tana ganin haka da gudu ta wuce sama tana turo baki, Saleem yyi murmushi ya mike ya isa dinning din yace “Big bro duk ka takura masu koh” Aliyu bai tanka sa ba ya dau Apple din gabansa ya fara ci. Bayan isha duk yan gidan suka hallara a dinning kasancewar in dai Daddy na garin duk a tare suke yin dinner a dinning area, Last cooler din kenan na soyayyen kaji kyauta ta dauka xata kai masu dinning din kasancewar ta mance Daddy ya hango Khadijah da ita ma ta fito daga kitchen xata shiga dakin kyauta rike da plate din abincinta, yana kallon Mumy yace “Kun yi baki ne?” Mumy ta kalli direction din Khadijah kafin ta shiga dakin ta kira ta, Juyowa Khadijah ta yi ta dawo, Sau daya Aliyu ya kalleta ya ci gaba da cin abincinsa kansa a sunkuye, Mumy tace “Yarinya ce aka kawo min riko daddy, kayi hakuri ban sanar maka ba yau satinta kusan uku, dama ina jiran sai ka dawo ne” yace “Riko kuma, daga ina” mumy ta yi yar dariya tace “Marainiyar Allah ce nan da ka gani” Saleem ya juya yana kallo Khadijah dake tahowa, Siyama ta tabe baki tare da tura abincin gabanta, Khadijah na isa wajen tana kallon Daddy a hankali tace “Good evening sir” da fara’arsa yace “Evening how are you” Khadijah tace “Alhmdllh, hw was the trip?” Ya kalli Mumy yana murmushi yace “It’s great” Shiru Khadijah tayi daddy ya nuna mata kujeran dake kusa da Saleem yace “Have ur sit ke ma” Ta gefen ido Saleem ke kallonta, Khadijah ta buda ido tace “Noo uncle I will love eating alone” daddy yyi murmushi yace “Alright then, do what pleases you” a hankali tace “Thank you” daga haka ta juya ta wuce, Daddy ya dau cokalinsa yace “She is sharp, haka nake son baby ta xama but baby is too meek” baby ta turo baki, Mumy tayi dariya tana kallon Baby da ta bata rai, kyauta ta bar wajen tana washe hakora a ranta tace “Har da mai gidan ma turanci take tsabar iya turancinta” sai da Daddy ya bar dinning area din sannan Saleem yyi facing Mumy yace “Wai mumy wacece yarinyar?” Aliyu ya ajiye cup din hannunsa yace “Did you have any business with her” Siyama ta hararesa ta gefen ido tace “Ya saleem na gaya maka house maid ce ko baka yarda bane, xan ma karya ne?” Mumy ta kalleta tace “She is a house maid or other wise thats nt ur problem, kuma kada ki sake kiranta da haka, yar rainin wayo kawai” jefar da cokalin hannunta tayi ta bar dinning din da sauri Aliyu ya bi ta da wani irin kallo, mikewa saleem yyi yace “Akan wata banxa can xaki bata mata rai mumy, for what….” Daga haka ya bar dining din shi ma, Aneesah ma ta tabe baki ta mike ta bi bayansu, Mumy ta bi su da kallo kafin tace “Allah ya kyauta” shi dai Aliyu bai ce komai ba, can mumy ma ta mike ta bar dining din, Baby ta bi abincin da suka bari ta kwashe naman kai ta sa a nata, Aliyu dake ta bin ta da kallo yyi murmushi yace “Glutton of the house” washe baki tayi tace “I don’t want it to waste yayanmu” yace “Then go and share it with Iman” mikewa tayi rike da plate din ta wuce dakin kyauta, ba a dau lkci ba ta fito ta ajiye plate din kan dinning tace “Na bata yayanmu, xan je wajen mumyna” daga haka ta wuce sama, yana ta xaune dinning din Khadijah ta fito rike da plate xata kai kitchen, tsayawa tayi ganinsa sai kuma ta nufesa tana murmushi ta buda dara daran idonta tace “Yayanmu thanks for the school bag I love it” kallonta yake yace “Wa yace maki sunana yayanmu” tayi dariya tace “Na ji baby tana kiranka haka, Anty kuma tana ce maka Aliyu, su Anty siyama kuma yaya Aliyu” bai ce komai ba ta juya xata wuce sai kuma ta dawo tace “But did you buy the bag with d name iman or you where d one dat place it there?” Yace “I don’t knw” wara ido tayi tace “Okay” sannan ta wuce kitchen, ganin kyauta ta fito gyaran dinning din ya mike ya wuce sama. Kafin Khadijah tayi bacci baby ta shigo mata da tsaraban da Daddy ya kawo tun daga kan chocolates, teddy bears, novels, takalma, rigan sanyi da ribbons na gashi sai kaya kala daya, kai kana ganin tsabar kasan na baby ne Mumy ta raba ta bata ta kai ma Khadijah, kyauta ma baby ta kawo mata nata tsaraban tana ta godiya baki har kunne. Kyauta na kitchen bayan su Khadijah duk sun wuce makaranta taji muryar saleem yana cewa “The great Aunt, ko minti goma ban yi da cewa xan kira ki inji yaushe xaki dawo, don duk gidan ba dadi ashe dai kina hanya” Anty Khadijah dake shigo da jakunkuna tace “Wllh kuwa, don ma d’an iska tsinannen mai mota muka samu, shi yasa na so Anty fati ta bani motar ta da xan tafi ta ki, banda haka wani banxan ne ya isa ya bata min rai a titi” Saleem dake taimaka mata shigo da kayan yace “Ae sai a hankali bin motar haya Anty da baki fara ba” Kyauta ta kwalalo ido ta jingina da kofa tace “Asshaa… Baxawara an dawo” Muryar Anty Khadijah taji tana cewa “Toh baxa ki shigo bane iklima ko kin kasa cire takalmin ne” kyauta ta leka a hankali suka yi ido hudu da Anty Khadijah, fitowa kitchen din tayi baki har kunne tace “Lale marhaba, Hajiya ashe ku ne, sannun ku da isowa” babu yabo babu fallasa Anty Khadijah tace “Ki hado ma iklima breakfast bata karya ba muka taho” sai a sannan yarinyar ta shigo parlorn, baxa ta wuce su baby ba a shekaru amma kana ganinta kasan cikin wahala take, ga tabo duk jikinta, kyauta ta karasa kusa da ita da gudu ta rungumeta tace “Yau ga iklima na gani ashe kece, yar kyakkyawa maa sha Allah, sannu da xuwa iklimatu” Anty Khadijah tace “Dalla ki cikata ki tafi ki nema mata abun k’ari, dangi uwa ko na uba” da sauri kyauta ta juya ta nufi kitchen, iklima ta bi ta da harara tace “Ashe ma house maid ce, kawai xata shafa min datti a jiki” Saleem yace “Iyye kaji Iklima manya, wato datti xata shafa maki koh, to ina su Yusuf?” Ta turo baki tace “Ai basu san mun taho ba” Anty Khadijah da ta yi hanyar stairs da jaka tace “Kafin ta gama maki breakfast din taho in sa maki ruwan xafi kiyi wanka, Saleem ku kuma saukan yaushe” Saleem yace “Jiya muka dawo Anty” tace “Daddy na part dinsu kenan” Saleem yace “Ina ji” bin bayanta yyi da sauran kayan, sai da suka isa dakinta tace “Aliyu fa?” Ya ajiye jakar hannunsa yace “Ya fita aiki.” Mumy ce ta fito jin muryar yar uwarta ta shiga dakin ita ma.

Back to top button