Hausa NovelsNoor Al Hayat Hausa Novel

Noor Al Hayat 46

Sponsored Links

Sai da sudais ya gama kallon d’an uwan nasa sosai kafin ya kai masa mari yana huci yace “How dare you call me that” Aliyu na ganin shureim yayi kan sudais ya daga sa sama ya rungume sa a hankali yace “Yi hakuri ka kyalesa sweetheart” kuka shureim ya fara yi hana sa dukan sudais da Aliyu yyi, Sudais na huci yace “I don’t like you both” dai dai fitowar Nanny daga shago, da sauri ta karaso tana tambayar me ya faru ganin shureim na kuka hannun Aliyu, sudais ya fashe da kuka shi ma yace “Nanny shureim started 1st, he insulted me” Nanny ta hade rai tace “Ohh har cikin market din ma sai kayi fada sudais, kai dai baka ji kuma nasan kai ka fara tsokanarsa ba ruwan shureim, silly boy kawai from henceforth bana sake xuwa ko ina da kai, ko kace xaka bi ni sai na ma duka” juyawa sudais yyi ya fashe da matsanancin kuka da gudu ya bar wajen xai je gun uwarsa, bin bayansa Nanny tayi tana kwala masa kira don ta can tsallake khadijah take kuma titin is very busy, amma sudais yaki tsayawa kuka kawai yake yana gudu yana kiran Anty, Aliyu na ganin haka shi ma ya bi su da sauri shureim na hannun sa, khadijah dake cikin mota tana xaune maxaunin driver don ita ta kawo su kasuwar haka nan kawai taji gabanta ya yanke ya fadi dai dai lkcn da taji ihun da mutane ke yi, tana juyawa kawai ganin Sudais dinta tayi a tsakiyar titi shi ma duk ya rikice ihun da mutane ke yi, ga mota har biyu sun taho da gudu ko wanne na son kauce masa, tunda take bata taba irin ihun da tayi ba a lkcn, lkci daya ko ina na kasuwan yyi tsit don duk yanda motar ta so avoiding sudais hakan bai yiwu ba, sai kuma a ka dau salati Khadijah ta fito a rikice jikinta na rawa ganin sudais kwance cikin jini ta fasa wani ihu kanta na juya mata, suman da ya kamata tayi nanny ce tayi sa a lkcn, ita kanta bata san me ya hanata sumewan ba, Aliyu da yyi still shi ma ya kasa motsi na few seconds ganin abinda ya faru lkci daya yaji strength ya dawo masa, ya ajiye shureim dake ihu yana kiran dan uwansa ya nufi gun sudais dake a kwance kan titi cikin jini mutane sun taru kansa mata na kuka maxa na salati, har da kyauta cikin mutanen, babu rabon Anty khadijah xata ga abinda ya faru don tsabar kunya bata jira Aliyu ya fito ba ta hau adaidaita da baby suka koma gida, cikin tashin hankali Aliyu ya karbi yaron hannun wani mutumi dake jijjigasa yana salati, a nan Aliyu yaji kamar bai taba xama likita ba duk rayuwarsa gaba daya basira ta dauke masa ya rasa ya xai yi da sumammen yaron dake hannunsa fuskarsa duk jini, cikin matsanancin kuka khadijah ta isa gun ta wani fasa ihu a gigice ta durkusa jikinta na rawa take cewa “Na shiga uku, don Allah ku taimakeni kar ya mutu ku rufa min asiri, kar ku bari ya mutu” daga kai Aliyu yyi a karo na farko yana kallonta jin muryarta, lkci daya signal dinsa ya sake daukewa yana mata wani irin kallo ita kuwa sai jijjiga sudais take ba tare da ta kula a hannun wa yake ba tana kuka tana cewa ya tashi kar ya tafi ya bar ta, kyauta ta saki salati baki bude tana kallon khadijah tace “Kamar khadijah nake gani ni kyautar Allah” khadijah ta kalleta ita ma da sauri, da gudu ta nufe ta rikota tana kuka cikin rauni tace “Anty ku taimake ni kar ya mutu don Allah, kar ya tafi ya bar ni” Kyauta ta kwalalo ido tace “Yaron ki ne Khadijah?” Khadijah ta dinga gyada mata kai tana kuka sosai, kyauta ta fashe da kuka tace “In sha Allahu baxai mutu ba xa mu tafi asibiti yanxu khadijah, baxai mutu ba…” wata mata ta fixge yaron a hannun Aliyu a mugun fusace ganin khadijah kawai yake kallo tace “Dubi mutum kamar an dasa sa a gun ya sa yaron da ba mu san ko ya mutu ba ko yana raye a gaba yana kallo, wannan wani irin uba ne kai, ni na xata taimkon gaggawa xai bada….” Khadijah ta tsayar da kukan da take ta sake kyauta ta nufi matar ta rikota cikin rudewa tace “yaro na bai mutu ba kar ki kara cewa ya mutu don Allah kar ki kara, wllh bai mutu ba, Allah baxai sa ya mutu ba” sosai ta ba mutanen gun tausayi wani mutumi ya sa sudais tare da matar a motarsa domin xuwa asibiti, mutumin ya kamo hannun Aliyu dake tsaye yana kallon khadijah da har sannan bata lura da shi ba yace “kar ka damu he will be alright in sha Allah shiga mu je asibitin tare” bayan motar Aliyu ya shiga suka dau hanyar asibiti, sai a sannan basirar sa ta likita ya dawo masa ya karbi sudais a rude ganin numfashinsa na sama ya dinga basa numfashi, banda kuka babu abinda matar dake kusa da shi take tana addu’ar Allah ya raya sa, jin mutumin dake ta sharara gudu a mota yyi parking Aliyu ya dago kai tare da bude motar ya ga asibitin da yake aiki ma mutumin ya kawo su, Aliyu ya fita rike da sudais yyi cikin asibitin da sauri nan aka shiga emergency da yaron, sai bayan kusan minti talatin Aliyu ya fito tare da wani likita daga emergency ward da aka shiga da sudais suka bar likita daya a kan sa da nurse, Dr Saif ya nufi gun su khadijah dake xaune reception da kyauta da wasu mutane har sun gaji da lallashinta don ko tayi kuka har ta gode Allah, tsabar tashin hankali ko gane asibitin bata yi ba, shureim dake jikinta ma kukan yake yana tambayarta me ya samu sudais, Nanny da ta suma an kwantar da ita asibitin ita ma, mikewa khadijah tayi da sauri ganin likitan, Aliyu ya tsaya daga inda yake har lkcn mask na bakinsa da hanci, Dr Saif yace “Ina mahaifiyar yaron?” Khadijah dake kallonsa gabanta na faduwa tace “Ni ce” Aliyu ya cire mask din dake fuskarsa yana kallon khadijah da wani irin mamaki, at the same time confusion, likitan ya tsaya kare mata kallo kamar bai yarda ba, can dai yace “Toh mahaifinsa fa?” Tana share hawayen dake xubo mata cikin rawar murya tace “Baya nan” likitan na kallon Shureim ya xaro ido yace “Subhanallah yan biyu ne?” Cikin kuka khadijah ta gyada masa kai, jikin likitan yyi sanyi sosai, ya shafa kan shureim dake kuka yana rike da mayafin Khadijah a hankali yace “Don’t worry my boy ur twin will be okay in sha Allah, madam xa ki iya shiga ki gansa amma plss kar ki wani damu ciwo ne kawai yaji a kai sai bruises, so don’t cry while inside, shi kuma wannan ki bar sa a nan ba sai kin shiga ba” daga haka ya juya yana kallon Aliyu dake nesa da su kafafuwarsa sun kasa daukarsa saboda shock yace “Dr plss see her inside, amma kar ta dade a ciki” daga haka ya kama hannun shureim yace “Big boy xo mu je office ka jira mumy” shureim xai masa taurin kai sai ya bi mamarsa ya daga sa sama kawai ya wuce office dinsa da shi don bai son ya ga dan uwansa a halin da yake ciki yanxu, Tuni Aliyu ya mayar da mask din fuskarsa yayi gaba kamar me counting step dinsa Khadijah na biye da shi a baya, tsabar tashin hankalin da ke tare da ita bata ko kalli wanda take bi ba balle ta san waye. Suna shiga ward din Aliyu ya tsaya bakin kofa ita ta shiga ciki gabanta na faduwa, ko gama ganin sudais bata yi ba ta fasa wani ihu, Nurse din ta karaso da sauri ta fitar da ita dakin tace “Haba madam, sai kace ba musulma ba wannan ihu haka” khadijah ta fashe da matsanancin kuka tana jijjiga nurse din tace “Don Allah Anty kar ku bari wani abu ya samu yarona, they all I have, plss ku taimake ni” rungumeta nurse din tayi tace “It’s ohk madam jikin ai da sauki, you just pray Allah ya tashi kafadarsa kuma kada Allah ya sa ya tashi da wata matsala” Khadijah ta xame kasa tana kuka tace “Na shiga uku wllh kilan mutuwa xai yi ya bar ni, don Allah ku taimaka min” juyawa nurse din tayi ta koma ciki ta rufe kofar, Aliyu ya kasa ci gaba da kallon khadijah lkci daya idonsa ya kada, yaranta? To waye ubansu? Abinda ya dinga masa yawo a rai kenan, kawai ya ga ta mike ta nufo sa, kana gani kasan ta gaji da kukan ta riko sa cikin rauni tace “Plss Dr kar ku bar min yarona ya mutu don Allah ina rokan ku, they are all I’ve got in this world bayan ummata, plss ka taimaka Dr ku cire masa abinda ku ka sa masa a hanci ina son yarona” Aliyu ya kasa ce mata komai lkci daya hawaye ya kawo idonsa, da ba don a rude Khadijah take ba bbu abinda xai hana ta gane Aliyu ne gabanta saboda kwayar idanuwansa amma saboda tashin hankali bata gane ba ganin, hawayen idonsa ta tsayar da kukan da take xuciyarta na bugawa tana kallonsa ko kiftawa babu, bayan few seconds cikin sanyin murya tace “Dr ya mutu koh?” Aliyu bai iya yace komai ba ya ji ya kasa controlling kansa hawaye suka shiga sakko masa, he don’t want to believe Khadijah conceived with him, he don’t want to believe she conceived that deadly moment, if so then he is not worth to be forgiven, bai cancanci ta yafe masa ba, don ya mata xaluncin da dole baxata iya yafe masa ba, sai a sannan maganganun da Anty khadijah take a waya daxu ya fara dawo masa, ya juya ya hade kansa da bango yana hawaye sosai duk ya ji ya tsani kansa, yanxu yaran nan nasa ne kenan?? He is there illegal father, the cute boys… Are his and Khadijah’s, they got them out of wedlock…. Lkci daya ya juya ta dalilin sound da ya ji bayansa, nan ya ga khadijah sume a kasa.

A hankali khadijah ta bude idanuwanta da suka mata nauyi ta dinga bin inda take kwance da kallo, Umma ce xaune dakin da Nanny da ta ci kuka har ta gode Allah, sai kyauta da tayi tagumi, Umma ta mike da sauri ganin khadijah ta bude ido ta karasa kusa da ita da damuwa tace “Sannu daughter, how are you feeling now?” Mikewa xaune Khadijah ke son yi amma kanta yyi mata nauyi ga kirjinta dake mata xugi, Umma ta riketa tace “Koma ki kwanta” Kyauta ta iso kusa da ita ita ma da damuwa tace “Sannu khadijah” Shiru khadijah tayi kamar me son tuno abu, Umma ta hade rai tace “Don’t stress ur self thinking of anything, just relax….” Hawaye ya kawo idonta ta kamo hannun kyauta cikin rawar murya tace “Anty mai girki ina sudais dina, ya mutu koh? Don Allah ku gaya min, kar ku” Umma ta dakatar da ita a mugun fusace tace “Ke kika kashe sa halan? Ji wani xance da kike ma mutane khadijah” Girgixa kai khadijah tayi da sauri hawaye na sakko mata, Kyauta tace “Toh yana nan lafiya khadijah, har ya tashi shi ma, suna can tare da d’an uwansa da wani likita” Khadijah na goge idonta tace “Toh xan iya ganinsa don Allah?” Harara Umma ta watsa mata tace “Da drip din xa ki je ki gansa, kuma ki rufe min maki haka, ance maki yana lafiya” Khadijah bata sake cewa komai ba sai dai ban da faduwa babu abinda gabanta yake, Umma ta mike ta shiga hada mata shayi, Nanny ta xauna kusa da ita cikin sanyin murya tace “Kiyi hakuri Khadijah, Sudais yana nan lafiya har ya tashi, suna tare da Shureim yanxu haka” Sai a sannan khadijah ta ji hankalinta ya kwanta sosai, Nanny ta mika mata wayarta tace “An kira ki har sau biyu, but I picked…” Khadijah ta karbi wayar tana kallon wanda ya kirata ta ga Khaleel ne, ta kalli nanny a hankali tace “Me ya ce?” Nanny tace “Na gaya masa abinda ya faru, yace xai xo clinic din” Khadijah bata ce komai ba ta ajiye wayar, ta ji tana ma son ganinsa, jin xai xo hankalinta ya kara kwanciya. All this while Aliyu na ward din da sudais yake tare da Shureim, kwata kwata bai son ya bar su ko na minti daya, da ya fita ba a jimawa xai dawo kuma har lkcn ya ki cire mask din bakinsa da hanci, damuwa ce sosai tare da shi, da ya kalli yaran ya tuna nasa ne sai yaji hawaye a idonsa, shi kuma irin tasa kaddarar kenan?? Har yan biyu ba ta hanyar aure ba, har ransa yake jin tausayin kyawawan yaran, he wished ba ta haka suka xo ba, Shureim bai ganesa ba sai dai ya lura da irin yanda sudais dake kwance ke kallonsa, A hankali ya isa kusa da yaron ya duka a sanyaye yace “You want something??” Sudais ya girgixa masa kai, Shureim ya kallesa da sauri na few seconds kafin yace “The voice…. sounds familiar” murmushin karfin hali Aliyu yyi ya sauke mask din fuskarsa a hankali yana kallon yaron, Shureim yyi shiru yana kallonsa can ya juya ya rungume hannunsa ya hade rai yace “You caused my brother’s accident” Jikin Aliyu yyi sanyi sosai, ya mayar da dubansa kan sudais ya ga ya ki kallonsa shi ma ya hade rai, bude kofa aka yi xai mayar da mask dinsa da sauri yaji muryar colleague dinsa, Dr Muktar ya karaso yana kallon yan biyun yace “Maa sha Allah, he is recovering fast” ya kamo hannun Sudais yace “How are you feeling now handsome?” A hankali Sudais yace “Alhmdllh” Dr mukhtar yyi murmushi yace “Good” kallon Aliyu yyi yace “Kasan kuna yanayi da boys din nan sosai, da ba don na san baka taba aure ba bbu abinda xai hanani cewa yaranka ne Dr” Aliyu ya kirkiri murmushin karfin hali yace “Gaskiya ne” Dr mukhtar yace “Naga kamar sun ma shiga ranka kai ma tunda gashi ka ki barin ward din tun daxu” Aliyu yace “Sure they are cute” Dr mukhtar yace “Just came to check on them dama” daga haka ya juya ya fita, Aliyu ya kamo hannun yaran murya can kasa yace “Am sorry for all that happened sweethearts forgive me plss” a hankali Shureim yace “Ohk…” Kallon sudais da yyi shiru yyi yace “And you sweetheart?” Sudais ya sauke kansa yace “Me too” jawo yaran jikinsa ya yi cikin sanyin murya yace “I love you boys” lkci daya idanuwansa suka kada, how he wish Khadijah xata yafe masa ba tare da ta sa masa heart attack ba, ta ajiye komai su xauna tare da yaransu, bai taba saba maganar mahaifiyarsa ba amma da kamar wuya wannan karan, it will be different…. he will marry Khadijah and have his boys in sha Allah, and he will neva be ashame showing them as his children, wani mugun son yaran ne ke fixgarsa yana rungume da su, bude kofar dakin aka yi Umma ta shigo tare da wani likita, khaleel na biye da su a baya, A hankli Aliyu ya daga mask dinsa sannan ya juya suka yi ido hudu da khaleel, Dr Abdul yace “Dr their grandma and a Dr also, my frnd Dr Ayman” Aliyu sai kallon khaleel yake kamar yanda shi ma khaleel ke kallonsa duk da fuskarsa a rufe yake, Umma ta kalli Dr Abdul sanin ance baxa a bar su su shiga gun yaran ba tace “Mun gode Dr” Dr Abdul yace “Ba komai Mama” Dr Abdul yace “Ayman bari in koma bakin aiki na” khaleel yace “Tnxx Abdul” daga haka Abdul ya fita, Shureim ya sauko saman gadon ya rungume khaleel, khaleel ya daga sa sama yace “How are you” kamar xai yi kuka yace “I am fine but my brother isn’t” Khaleel ya ajiye sa ya karasa yana kallon Sudais cike da tausayinsa, Shureim kuma ya nufi gun Umma dake kallon Sudais ita ma a sanyaye, plaster ne gaba daya kansa, khaleel ya kamo hannunsa yace “You will get well soon in sha Allah my boy” Sudais xai fara kuka ya rungume sa yace “Noo don’t cry be a strong boy” Sudais yace “Uncle ina Antyna” khaleel yace “Xata xo yanxu” sudais yace “Ka kai ni wajenta I want to see her” Khaleel yace “Noo she will be coming soon” Aliyu dai na tsaye yana ya na kallonsu, Can ya kalli Umma yace “Plss Maa it shouldn’t take long xa ku iya tafiya yanxu the boy need rest” Umma tace “To xa mu fita yanxu Dr” khaleel ya juya yana kallon Aliyu, mikewa yyi ya isa gabansa yana kallon cikin idonsa yace “Then discharge him now, xa mu je gida in ci gaba da treating dinsa or I take him to another hospital” Aliyu yyi murmushi daga cikin mask din fuskarsa yace “And who are you to say that? His father? Or?” Umma tace “Aa bai kai haka ba Dr xa mu fita yanxu ai” wani kallo khaleel ya dinga ma Aliyu, Umma tace “mu je khaleel tunda a bakin aikinsu suke” kallonta khaleel yyi, duk da bai yi niyyar fita ba amma ya ji kunyanta yace “Toh umma” daga haka ya nufi kofa Shureim ya bata fuska kamar xai yi kuka yace “Uncle are you leaving us?” Sudais ma ya dinga kallonsa Kamar xai yi kukan, Khaleel ya juyo yace “Noo sweetheart I am around” Daga haka ya fita, Umma ta bi bayansa tana kara ba Aliyu hakuri tana fita ta rufe kofar, wata cleaner ce ta shigo dakin da abinci da ruwa da Aliyu ya sa ta siyo, ya mika ma Shureim nasa ya karba, Ya shiga ba sudais nasa da kansa. Khadijah duk ta damu tana son ta ga yaranta ganin har da Shureim ma tun da ta bude ido bata gansa ba, amma tsoron Umma yasa ta kasa cewa komai don tana iya balbaleta yanxu tunda ta ce mata they are all fyn, Khaleel dake tsaye dakin yana kallonta ya lura da yanayinta, ita ma ta tsaya kallonsa amma ta kasa ce masa komai ya san she Wants to say something, ya kalli Umma dake magana da wasu neighbours dinsu biyu da suka xo duba sudais, Nanny kuma ta koma gida tayi girki, Kyauta ma ta koma tace xata dawo ko da daddare da mai gidan ta, Khaleel ya karaso kusa da ita a hankali ya d’an duka yace “What?” Murya can kasa kamar xata yi kuka tace “I want to see my kids plss” wani kallo ya mata, sai kuma ya d’an yi murmushi yace “To sannu mai kids” ta bata fuska tana kallonsa alamar please, yace “Ohk wait bari Umma ta raka bakin nan sai in kai ki” lkci daya hankalinta ya kwanta tace “Toh ngdd” Umma na fita don yin rakiya ya cire mata drip din hannunta da ya kusa karewa, duk da jirin da take ji ta mika masa hannunta ya rike ta sauko daga kan gadon ta sa takalminta sannan suka fita ward din da sauri tana jin kamar xata fadi ba don ya rike hannunta ba, direct ward din da yan biyun suke ya nufa da ita, a hankali ya murda kofar ya bude, khadijah tayi ido hudu da Aliyu dake ba sudais abinci, still tayi a gun taji komai nata ya tsaya, xuciyarta ya dinga bugawa da sauri da sauri, Shureim ya sakko ya taho da gudu ya rungume ta, sudais yyi murmushi cike da jin dadi ganin uwar tasa yace “Anty….” Mikewa Aliyu yyi ya rufe abincin yana kallonta da khaleel yace “You can come over… But just few minutes” Khadijah ta warce hannunta a na Khaleel ta janye Shureim a jikinta ta juya ta bar wajen kamar xata tashi sama, direct reception ta nufa, tana kallon nurses din cike da masifa tace “Who is the Dr in charge of this hospital…” Kallonta nurses din suka tsaya yi, can wata ta mike tace “Me ya faru madam” tana huci tace “ohk, I want my kid discharge immediately, ku bani bill din in biya in bar nan yanxun nan plss” cikin tsawa ta kare maganar nurse din ta koma ta xauna tace “Easy madam, this a hospital, they are patients all over, ki je gun likitan da ya karbe su, shi xai yi discharging dinsu ba mu ba madam” khadijah na mata wani kallo tace “Wani likita kenan ina office dinsa kuma?” Nurse din tace “Dr Aliyu, kina haurawa sama office dinsa is by ur right, xa ma ki ga sunansa a jiki” kallonsu Khadijah ke yi xuciyarta na bugawa jin sunan da suka kira, can ta juya kamar xata tashi sama ta wuce upstairs din, Har lkcn khaleel dai na tsaye bakin kofa yana kallon Aliyu, Aliyu ya isa dab da shi yana masa wani kallo yace “Da matsala ne malam, naga kallon yyi yawa?” Wani murmushi khaleel yyi yace “You watch and see” Dawowa khadijah tayi dakin cikin tashin hankali ta nufi gun yaranta ta cire dip din hannun Sudais ta sauko da shi kan gado ta kama hannun Shureim ta nufi kofa, tsayawa gabanta Aliyu yyi yana kallonta da kyau yace “Ba inda xa ki je da su Iman” xaro ido tayi jin abinda ya fada ta tura sa da karfi amma go gezau, xuciyarta na heaving da mugun mamaki tace “Ba inda xan je da su kamar yaya??? ka taba sanin su ne, ko kuma ni ka san ni ne? Where did you knw us from” yyi wani murmushi yace “Khadijah, am giving you my words, you are not moving a step forward with my kids, ki fadi duk amount da kika ga yyi suite din ki, tun daga daukar cikinsu, rainon cikin, haihuwarsu har xuwa girman su yanxu and I will pay you, kilan hakan kadai xai sa ki yafe min idan na amshi wahalata da na hada ki da at a very tender age, ni kuma baxan ji kunyan daukansu in kai su gida gun iyayena a matsayin yaran da na haifa out of wedlock ba, shikenan kema na raba ki da wahala na raba ki da rikon ‘ya yan da kika samu ta hanyar fyade da aka maki, sai ki tafi kiyi auren ki hankali kwance ba tare da kin kara tunanin kina da yaran da kika haifa ba ta hanyar aure ba, I am collecting my boys today for ur own good”
Kallonsa Khadijah take ko kiftawa babu, bakin ciki da takaici ne fal idanuwanta, xuciyarta ya dinga mugun bugawa, ta hadiye abu da kyar, lkci daya idanuwanta suka yi jajir cikin muryar da ba ta ta ba tace “Come again Aliyu… I didn’t get you” Cire mask din bakinsa yyi gaba daya yana kallonta da kyau cikin husky voice dinsa yace “You are not daft Iman, you heard me right, or you ask ur bodyguard xai maki bayani da kyau” bai rufe baki ba ta sauke masa mari tana huci, wani murmushi khaleel yyi yana shafa sajensa yace “Seems you both need privacy” daga haka ya juya ya bar wajen har sannan yana murmushi, Aliyu ya kauda kansa na few seconds kafin ya juyo a hankali yana kallonta da wani irin mamaki, hawaye na sauka idonta tana girgixa kai tace “Allah ya isa tsakanina da kai Aliyu, shari’ar mu da kai dama na fada maka sai a lahira, kuma yarana ba naka bane, ba kai ka haifar min su ba, you don’t have any right over them, idan duk duniyar nan xa su hade nan wlh wllh baxan baka su ba, ni na sha wahalan kayana ni na haife su, baka isa ka raba ni da su” ta fashe da matsanancin kuka xuciyarta na mata xafi, hakan yasa su shureim ma suka fara kuka suna rike da ita, kallonta kawai Aliyu yake da idanuwansa da suka yi jajir, ganin khaleel ya bar wajen khadijah ta kama hannun yan biyun ta da sauri ta juya xata bi bayansa Aliyu ya fixgota yayi jamming kofar yana mata wani mugun kallo, lkci daya ta cakumosa tana kuka mai taba xuciya tace “Ka bude mana mu fita Aliyu, ka bude kofar in fita da yarana kar in tara maka jama’a” yanda ta rikice haka yaranta ma suka rikice suna kuka, daukar ta Aliyu yyi ya nufi bathroom dake ward din ya tura ta ciki yace “I will teach you sense Khadijah….” daga haka ya rufe kofar da makulli ta dinga bubbuga kofar a rude tana kuka tana kiran sunansa, Sudais ya kara fashewa da matsanancin kuka yace “Why are you doing this to our Anty, plss let her out” Shureim ya dinga bubbuga kofar shi ma yana kuka yana kiran ta, Aliyu ya hade kansa da bango ya runtse ido xuciyarsa na bugawa, lkci daya ya juyo ya kama hannun yaran gaba daya suna turturjewa ya watsa masu wani mugun kallo da idanuwansa da suka yi ja, ba shiru suka yi tsit ko wanne a tsorace, ya bude kofar ward din ya fita da su, ward na intensive care ya shigar da yaran tunawa da yayi bai taho da motar clinic din ba, banda kuka babu abinda suke yi suna kallonsa a tsorace, fuskarsa daure yace “I don’t want to hear any of you cry again” shiru suka yi sudais ya riko hannunsa yace “plss bring out our Anty from the toilet” sauke idonsa kasa yyi a hankali yace “Ohk i will do that now” daga haka ya fita ya rufe kofar yanda baxa su bude ba, sama ya wuce da sauri ya shiga office din Muktar ya dau makullin motarsa sannan ya sauko, yana bude kofa su sudais suka yi tsit daga kukan da suke, Shureim yace “Uncle where is she plss” hannunsu ya kama ya fita da su, ya bi ta bayan asibitin xuwa parking space, back seat ya saka yaran gaba daya sannan ya shiga driver seat ya tada motar ya bar asibitin. K’asa kuka twins din suka yi a motar saboda Aliyu da ya hade rai, kana ganinsu kasan a tsorace suke barin Shureim, driving kawai yake har ya iso gida bayan yyi parking ya fito ya bude masa motar yace “Come down” da farko kin sakko suka yi, ganin kallon da yake masu duk suka fito, Shureim na goge idonsa cikin rawar murya yace “I thought you where a good friend, plss don’t kidnap us away from our Anty, she will be sad” Duk da hawayen da ya taru idon Aliyu hakan bai hanasa durkusawa gabansu ba ya rungume su gaba daya yace “I didn’t kidnap my kids, I brought you two to ur Granny” Sudais ya xaro ido yace “We left her at d hospital and this is not our home” Aliyu na kallonsu cikin sanyin murya yace “This is your father’s home” A tare suka hada baki gun ce masa “Where is he?” Shiru Aliyu yyi yana kallon handsome boys din, sudais yace yace “Anty told us our father… Is a Barrister, she said he travelled immediately we where born and that… he will come to us one day” Jikin Aliyu yyi mugun sanyi yana kallonsu, Shureim yace “We will love to see our dad” mikewa Aliyu yyi ya kama hannunsu ya wuce cikin gida da su. Sudais ya bata fuska kamar xai yi kuka yace “I thought you are taking us back to our Anty” gaba daya yan gidan na parlor xaune ana jajanta abinda Kyauta ta ma Anty khadijah, saleem sai cewa yake da ma da shi aka je ya lallasata ya cire mata hakora ya ga wanda ya tsaya mata, mumy dai bata ce komai ba sai kallon Anty khadijah dake kwance kasa take duk jiki yyi tsami don ma ta gasa jikin da ruwan xafi, baki a kumbure har da ido, iklima ma an sallamota tana sama a kwance, gaba daya occupant din parlorn suka dinga kallon Aliyu da twins din hannunsa, Anty khadijah ta mike xaune da sauri ita ma tana kallonsu, Baby ta mike da mugun mamaki tana kallon yaran tace “Laah yaran da muka gani a kasuwa daxu, yaya where did u knw dem from, mai ya samu kan wannan” Aliyu ya isa har gaban Mumy dake kallon yaran ya sake hannunsa, a sanyaye yake kallonta, yyi gathering courage da kyar yace “Yaran da Iman ta haifa kenan, she got pregnant after the incident” Ba Anty khadijah kadai ba har Mumy sai da ta girgixa ta mike tana kallon yaran dake ta kallonta sannan ta mayar da dubanta kan Aliyu cikin wani yanayi tace “How did you knw Abuturrab, where did you get dem from???” hawaye suka shiga sakko masa yana kallon mahaifiyar tasa a sanyaye yace “I met them today mum, I don’t knw if Khadijah will ever forgive me… I ruin her at a very tender age, this boys are my blood, Mumy na kawo su gida ne don nima in yi facing ko da kadan ne daga cikin abinda tayi facing a rayuwarta duk da ni na fita ga ta….” Kasa ci gaba yyi ya bar parlorn ya wuce sama hawaye na sakko masa, Anty khadijah dake ta xufa ga cikinta da ya tsure tace “Mun shiga uku, Anty fati kin ga wani sharri koh, kin ga wani hauka irin na Aliyu ko? yaushe Aliyu ya isa haifan wa ennan yaran? ta je an mata ciki a wani waje ta makala masa kuma ya yarda saboda wawa ne shi… a ina ma ya ganta???” Kai kana gani kasan kame kame kawai take duk ta rude, Su Shureim sai bin kowa na parlorn suke da kallo a tsorace, baby ta fashe da kuka cike da tausayin yayanta, Salim ma sai kallon yaran yake a duk jikinsa yyi sanyi ganin kamannin Aliyu sak tare da su, Mumy ta fashe da kuka sosai ita ma tana kallon yaran, hakan yasa su ma suka fashe da kuka, babu abinda take gani tare da yan biyun sai Aliyunta lkcn da yake kamar su, Anty khadijah ta haura sama kusan a guje tana cewa “Yau na ga abinda ya isheni bai ishi Allah ba, ina yake ya xo ya fitar mana da shegun nan da ake shirin kakaba masa, ya xo ya mayar da su inda aka basa su, amma Allah ya isa tsakaninmu da yarinyar nan, ta rasa wanda xata ma sharri sai Aliyu saboda tsautsayi ya gifta tsakaninsu? Ni dai nasan da hankalin Aliyu baxai mata fyade ba, sharrin shaidan kawai da kuma sharrin ta don ita ke shisshige masa, wlh baxa mu amshi shegu gidan nan ba, kaf xuri’ar mu ba a taba haka ba baxa a fara a kan d’an yayata ba” tana wucewa sama mumy na share hawayenta ta kama hannun yan biyun ta wuce sama xuwa dakinta da su. Wata nurse ce ta shigo dakin ba ma sudais allura ta ga babu kowa dakin sai kofar bayi da ake ta bubbugawa ta isa da sauri ta bude kofar da mamaki ganin key aka sa ta waje, khadijah ta fito tana bin dakin da kallo ganin ba kowa ta riko nurse din a rikice tace “Na shiga uku nurse ina yarana? Where are they plss” nurse na kallonta da confusion tace “Yanxun nan na shigo madam” da gudu khadijah ta fita xuwa ward din da aka kwantar da ita, ta ga Umma ce xaune sai Nanny da khaleel dake tsaye ya jingina da bango idonsa a kan wayar hannunsa, ta fashe da matsanancin kuka ta xube wajen tace “Wayyo Umma na shiga uku ya tafi min da yarana” khaleel ya iso gabanta da sauri da mamaki yace “Ya tafi da su ina? Kina kallonsa ya tafi da su” ficewa yyi ward din da sauri, Umma da ta gigice tace “Wa ye ya tafi da su Khadijah, waye shi” Khadijah ta riko Umma tana kuka sosai tace “Umma Aliyu, ya tafi da yaran, ya wuce min da yarana” a sanyaye Umma ke kallonta, Nanny ta bi bayan khaleel da sauri tana cewa “Me ya kawo sa asibitin, mun shiga uku” umma ta dago Khadbijah ta rungumeta, cikin rawar murya take cewa “Umma kar ku bari ya raba ni da su, baxan iya rabuwa da su ba, don Allah a taimake ni a karbo min yarana ni na yafe masa duniya da lahira ya bar min yaran, wllh na yafe masa har cikin xuciyata amma yayi hakuri ya ba ni yarana” tana kai wa nan ta kara fashewa da matsanancin kuka tana kiran Umma, hawaye ya shiga sakko ma umma ta rasa abinda xata ce ma ‘yar tata.

Direct office din Dr Abdul khaleel ya wuce, ya samesa xaune yana aiki, ganin khaleel ya bar abinda yake yi yace “He is improving ko Dr” khaleel bai tanka sa ba isa gabansa ya dafa table yana kallonsa bbu yabo bbu fallasa yace “Dr Aliyu…. Where is his home?” Dr Abdul yace “Aliyu? Ba yana office ba?” Khaleel yace “Baya nan” da mamaki Abdul yace “Hope babu matsala dai?” A takaice Khaleel yace “Babu, ina gidansu yake” Abdul yace “Toh, he is not the type that mingle gaskiya I dont knw his home” juyawa Khaleel yyi ya fice office din, direct parking space ya nufa ya hau motarsa ya wuce gidan Farouq. Umma ta dinga kwantar ma khadijah hankali duk da taki saurarenta, daga karshe Umma ta fita ta biya bill dinsu don bata ga amfanin xaman asibitin ba, na khadijah kadai suka karba ban da na sudais kamar yanda Aliyu yyi instructing din su, da kafa suka fita asibitin don Umma bata xo da mota ba, suna isa bakin titi ta tsayar masu da abun hawa suka wuce gida. Girgixa kai Farouq yyi yana kallon Khaleel yace “Ni fa ba ruwana, kamar yanda na ki ba sa address din ka, to kai ma baxan baka address din sa ba gaskiya, ku kuka san abinda ya hada ku can..” Wani kallo khaleel ke masa kafin ya mike ya fice daga gidan ya shiga motarsa ya wuce, yana driving ya dau wayarsa ya fara kiran Khadijah, har ya katse bata dauka ba, nan ko tana zaune ita kadai daki tayi kukan har ta ji ba dadi, Umma kuma na parlor da Nanny sun yi jigum, Umma ta rasa ta ina xata fara yanxu ta ina xa su fara xuwa neman yara, Jin wayar ya sake ring Khadijah ta daga da kyar ta kai kunne, jin muryar ta jikin khaleel yyi sanyi, a hankali yace “Plss ki kwantar da hankalin ki Khadijah, xa a amsar maki kids din ki, he have no right over them, in sha Allah we will get back ur kids” kasa cewa komai tayi tana share hawayen da ke xubo mata, yace “Kin san address din can gidansu?” Shiru tayi kafin ta girgixa kai cikin sanyin murya tace “Na manta” yace “Amma xa ki gane gidan?” Nan ma ta d’an yi shiru, anya xata gane gidan yanxu kuwa, murya can kasa yace “Khadijah?” Tace “Kilan in gane” yace “Good, kuna clinic din har yanxu?” Ta girgixa kai tace “Mun dawo gida” yace “Toh xan taho yanxu, but promise me baxa ki sake kuka ba plss” a hankali tace “Toh baxan yi ba” yace “Good, ina tahowa yanxu” daga haka ya katse wayar, Sosai Khadijah ta ji hankalinta ya kwanta, ta ji ta samu natsuwa. Tun da Aliyu ya shiga dakinsa bai sake fitowa ba, Mumy da maganganun Anty khadijah suka fara sa mata ciwon kai ta daga kai tana kallonta a karo na farko tun shigowarta dakin, ban da kumfar baki kamar wata xararriya babu abinda take tana nuna yan biyun dake xaune kan gadon Mumy, suma yaran kallonta kawai suke a tsorace, Baby ma na tsaye sai hararan Anty khadijah take tana tabe baki, Mumy ta dakatar da ita a tsawace tace “Khadijah ki fita ki ban waje don Allah ki bar ni in ji da guda daya, ciwon kai kike kara min ki fita don Allah, ko makaho ya shafa yaran nan yasan na waye, Baxa ayi DNA din ba….” Anty khadijah da idanuwanta suka kankance da mugun mamaki tace “Anty fati ni kike cewa in fita in baki waje don ina nuna damuwa ta kan shegun da aka makala ma Aliyu aka ce nasa ne, Ni Anty fati??” Mumy tace “Ehh ki fita nace” tayi wani murmushi tace “Xan fita yanxu kuwa” daga haka ta fice daga dakin kamar xata tashi sama, Mumy ta kalli yan biyun dake bata tausayi har ranta, a hankali tace “Me xa ku ci?” Sudais dai bai ce komai ba, Shureim ya girgixa mata kai shi ma bai ce komai ba, karasowa tayi ta xauna gun yaran tana kallonsu, wani sonsu take ji a xuciyarta, ta d’an yi murmushi tace “Ayi maku noodles and egg?” komawa Sudais yyi ya kwanta ta kai hannu jikinsa taji xafi sosai, kallon baby tayi tace “Xaxxabi ne jikinsa fa sosai…” Baby ta karaso ita ma ta taba yaron taji xafin jikin ta kalli Mumy tace “Mumy ko in kira yaya?” Mumy tace “Kira sa” juyawa tayi ta fita, ita ta fara dawowa dakin sannan Aliyu ma ya shigo, kallon yaron yake har ya isa kan gadon ya taba jikinsa, dago sa yyi ya xaunar da shi, yana kallonsa yace “Are you feeling pain anywhere?” Sudais ya nuna masa kan sa, kamar xai yi kuka yace “I want to go to my Anty plss” Aliyu ya lumshe ido ya bude a hankali yace “Ohk I will take you there” Mumy dake kallon Aliyu tace “Ina ita khadijahr take?” Kamar Aliyu baxae ce komai ba, sai kuma ya shafa kansa murya can kasa yace “Bayan ta bani su tayi tafiyarta” wani kallo Mumy ke masa ganin yanda yyi maganar, can ta girgixa kai tace “Karya kake…” Da sauri ya kalleta, sai kuma ya marairaice yace “Mumy bata sani ba na taho da su, idan ta sani baxa ta bani su ba” Bude baki Mumy tayi tana kallonsa, da damuwa tace “Me yasa xaka yi haka Aliyu, me yasa xaka raba su da uwar su….” Kasa cewa komai yayi, Mumy da duk jikinta ya kara yin sanyi tace “Aliyu tell me how everything happened, garin yaya kayi ma yar mutane haka, where was I that day? kar ka boye min komai plss, tell me the truth….” kallon Mumy Kawai yake ko kiftawa babu, can ya xauna gefen gado ya rike kansa yana jin kamar ya fara mata hawaye, bai son tuna mummunar ranan nan a rayuwarsa, Mumy na kallon Baby tace “Baby xo ki tafi da su ki dafa masu indomie ki basu, shi wannan ki kai sa dakin ki ya kwanta” Baby ta karaso ta sakko da boys din daga kan gado ta wuce da su dakinta, Mumy na kallonsa tace “Ina ji Aliyu” Da kamar baxai ce komai ba, sai kuma a hankali ya fara magana, “Mumy ni dai nasan I woke up fine that very day….” Ya d’an yi shiru, nan ya fara ba ma Mumy labarin abinda ya faru ranan bai boye mata komai ba har yanda bayan kwana biyu ya ba ma khadijah kudi me yawa yace ta wuce gun ummarta, hawaye kawai Mumy ke yi tana kallonsa a sanyaye, bai iya ya dago kai ba shi ma hawayen na sakko masa cike da karfin hali yace “Mumy nayi abinda nayi ne out of confusion, I was confused, ban taba xaton xan aikata ma khadijah haka ba, bayan tafiyar ta ku shaida ne, nayi bankwana da kwanciyar hankali da farin ciki na, I never had rest of mind again kuma na kasa gaya maki abinda ya faru ban san ya xa ki dau xancen ba, shi yasa a ko da yaushe nake ce maki ki taya ni da addu’a, wani lkcn idan na kwanta bacci ita kawai nake gani, kuma it’s not as if nasan da cikin bane, kawai ni dai nasan ban kyauta mata ba saboda marainiya ce bata da kowa, ban san ta Inda xan fara nemanta ba don ban san kowa nata ba, da babu abinda xai hanani nemanta Mumy, idan baki manta ba akwai wani lkci da na taba tambayar ki ko kina da number warce ta kawo ta kika ce baki da shi, ni ban sa ko Khadijah xata yafe min ba and it looks as if I don’t deserve that…. Amma abinda ke bani mamaki har yanxu shine yanda aka yi Anty khadijah ta san abinda ya faru bayan bata gidan kuma ita ta fita tare da su baby a ranan, gidan ya rage daga ni sai Khadijah, sai kuma jiya tana waya a bathroom din dakinta, I overheard all what she was saying on the phone…. Nan ya gaya ma Mumy duk abinda ya ji Anty khadijah ke fada a waya jiya, yana girgixa kai yace “We shud keep on pretending mum, she was so shock da ta gan ni a dakin, but i pretend ban ji komai ba, hakan kuma ya sa hankalinta ya kwanta, a sannu abinda take yi xai bayyana a fili tun da ba mu da hakkinta, kuma ina mai tabbatar maki soon komai xai bayyana, ke dai kawai ki ci gaba da sa mata ido, xan dai sa su Sanusi su tone bayan gidan to check what she was talking about on phone” Mumy ta dinga kallonsa ko kiftawa babu cike da shock, ya goge idonsa har lkcn bai kalleta ba yace “And… Mumy kilan idan ke kika yi ma khadijah magana xata iya yafe min, ni ta ki saurarata har yanxu, kuma mumy plss kar ki ce min baxan iya aurenta ba, hakan kadai ne xan iya mata in wanke kaina, I knw I can’t pay her all what she passed through, kar ki hana ni aurenta mumy…” Mumy ta sauke ajiyar xuciya har lkcn tana mamakin abinda Aliyu ya fadi mata kan Anty khadijah, she is still finding it hard to believe that, infact bata ma yarda bane tasan Anty khadijah baxata yi abinda Aliyu ke fadi ba, Aliyu yace “Mumy kinyi shiru” Mumy ta kallesa ta kara sauke ajiyar xuciya sannan tace “Idan kuma ita bata son ka fa?” Ya d’an hade rai yace “Toh sai ta bar min yarana taje tayi aurenta shikenan na raba ta da wahala, idan kuma ta yarda ta aureni sai mu xauna mu rike yaranmu, domin kuwa su din abun kyama ne idan ta kai su wani gidan, ko ba yanxu ba wataran xa a kyamace su, to idan muna tare fa? We can never do that to them” Mumy bata kuma cewa komai ba tayi nisa tunanin da take na Anty khadijah, Bude kofar dakin Anty khadijah tayi ta shigo tana kallon Mumy da kumburarrun idonta da ta sha kukan takaici, kallo daya Mumy ta mata ta dauke kai xuciyarta na kara karyata Aliyu, Aliyu kam bai ma kalli inda take ba, tana kallon Mumy tace “Ina son sanin matsayin auren iklima a gidan nan Anty fati, na hada kayana idan Ita ma in hada nata ne toh…” Sai a sannan Aliyu ya kalleta yace “Anty aure ya taba mutuwa ba ayi saki ba?” Hararansa tayi ta juya ta fita, dakin baby ta bude ta dinga kallon yaran dake kan gadon cike da tsana, a tsorace suke kallonta su ma, can ta juya ta fita dakin ta sauka downstairs xuciyar ta na tafarfasa, Baby ce kitchen tana bare eggs da ta dafa masu indomien na kan wuta, Anty khadijah ce ta shigo kitchen din ta dau cup ta xuba ruwan xafi daga flask, Baby ta kalleta ganin yanda ta tsaya tana tunani, da sauri Anty khadijah ta bude gun da madara suke ta fiddo kayan tea ganin kallon da baby ke mata, tana hada shayi tace “Baby ina wani sarka da na baki ki ajiye min ranan da aka yi bikin iklima a gidan nan?” Baby tace “Anty yana cikin jakata a daki” Anty khadijah tace “Je dauko min kayana” Baby tace “Yanxu Anty?” Anty khadijah ta balla mata harara tace “Aa anjima” a sanyaye baby ta juya ta fita kitchen din bayan ta rage gas kar indomien ya kone, Anty khadijah ta fara kalle kallen kitchen din da sauri, lkci daya ta fita waje ta kofar kitchen din ta tafi gun da ake ajiye snipper, Baby har ta fara haura stairs ta d’an tsaya, da sauri ta koma ta rabe jikin bango tana lekan kitchen din ta ga Anty Khadijah bata ciki, har xata juya ta bar wajen sai ga Anty Khadijah da gudu ta dawo kitchen din ta bude abun hannunta ta xuba cikin indomie da ke kan wuta, Xaro ido baby tayi taji kafafuwarta sun kasa daukar ta, lkci daya hawaye ya cika idonta ta juya da sauri ta haura sama, dakin Mumy ta shiga ta fashe da kuka, Aliyu ya mike yana kallonta yace “Me ya faru?”

Back to top button