Hausa NovelsSakayyah Complete Hausa Novel

Sakayyah 25

Sponsored Links

 

SAKAYAH

 

25

 

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

 

 

*Al’bishirunku Ma’aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma’aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken  GARKUWAR MA’AURATA*

 

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.

Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

 

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.

Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?

Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.

Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?

Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba’a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,

Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.

Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.

 

 

Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*

Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu’umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

 

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

 

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA

*(GARKUWAR MA’AURATA)*

 

Isrejy. Suna fita suka ga gari yayi shiru ga wani irin hadari daya haɗu baƙiƙƙirin, sanyayyar iska mai sanyi da ratsa jiki yana kaɗawa alamun wata ƙil hadarin ya watse ne ko kuma ya sako ruwa,  wani irin lumshe idanu Moddibo yayi tare da cije labɓansa na ƙasa cikin sauri ya shiga mota M Jameel yashiga maza mazaunin Driver yaja suka tafi suna isa gida aka fara yayyafi still yau ma ɗakin Moddibo M Jameel yashiga ya kwanta nan da nan bacci ya ɗauke sa.

Moddibo kuwa tunda ya kwanta yake juyi ahankali ya miƙe ya zauna idanunsa cike da ruwan fitina da zaran ya lumshe Idanunsa kyakkyawar suranta daya gani amafarkine ke masa yawa kana idan ya buɗe lokacin da suka kasance amota ne yake masa gezo zama yayi Atsakiyar gadon D ɗinsa ya shiga harbawa da masifar ƙarfi tamkar zai tsinke lokaci ɗaya jikinsa ya ɗauki rawa yayin da lips ɗin sa suka shiga rawa har haƙoransa na haɗuwa suna bada sautin Ƙat-ƙat-ƙat kana Idanunsa sun kaɗa sunyi jawur tare da ƙanƙancewa kallo ɗaya zaka masa kasan yana cikin tsananin buƙatar kasancewa da.

Mace da ƙyar ya miƙe yashiga toilet tare da sakarwa kansa ruwan sanyi duk da kuwa sanyin da ake agarin amma tamkar ƙarawa yake cikin mawuyacin hali da yanayin buƙatuwa ya fito tare da kwanciya rub da ciki cikin wahalallan hali bacci ya ɗaukesa.

 

Bayan kwanaki biyar sosai kafar Ramadan yayi sauƙi har ya fara takawa ahankali  sosai Mommy da Khausar da kuma Lamiɗo sukayi farin ciki ganin babu wata matsala.

 

Aɓangaren Uncle Naseer kuwa abubuwa suna tafiya kamar yanda ya tsara baki daya ya maida hankalinsa da nutsuwarsa kan Amina yana nuna mata zallar so tare da yimata duk wani abinda take so yayin da acan ƙasan ransa kuwa soyayyar Khausar na nan kamar yanda yake yana da burin ta kasance matar.

Aurensa kana yana jin

yana son ya haɗa shimfiɗa da ita yana so yaji shin ya ɗanɗanonta yake, domin itace mace ta farko daya fara so tare da ƙulafacin ɗanɗanar zumanta ita kaɗai duk da cewa yayi Sex da mata kala da ban da ban bai taɓa sanun cikakkiyar nutsuwa da kwanciyar hankali ba, yanaji  awajen Khausar ce kaɗai yake da ya ƙinin zai samu irin wannan nutsuwar da yake buƙata, duk wani tsarinsa yana yine dan ganin ya samu ya ɗanɗanin zumanta tare da kawar da ƙishinsa akanta.

 

Aɓangaren su M Jameel kuwa sun sake samun malam Arɗo da batun barinsu makaranta amma fir malam Arɗo yaƙi amincewa sam baya so ma suzo masa da batun yayin da M Jameel da Moddibo suka rage zuwa makarantar domin sukanyi kwanaki uku ko  huɗu ba suje ba wani zubin ma har satin ya ƙare baza sujeba kasancewar sun riga da sun faɗa masa cewa sun ajiye aikin.

Baki ɗaya sun mai da hankali da nutsuwar su akan abinda suka sa gaba na batun aikin da zasu fara a Company Abban M Jameel.

Abba kuwa kasancewar yanzu damuna ne yasa ya maida baki ɗaya hankalinsa da ragowar kuɗin hannunsa akan noma musamman nomar Auduga da ake masa saboda yana amfani dashi a Companyn’,sa na Marrocco yana buga manyan zannuwan gadaje sallayoyi da jallabiyoyu na mata da maza riguna na alfama  da dai sauransu.

 

Wata ranar Litinin tun safe garin Gembu suka tashi da ruwan sama tamkar da bakin ƙwarya sai daf Azahar ruwan ya tsaya gari yayi sanyi Sanyayyar iska na kaɗawa yayin da bishiyoyi ke rangaji tamkar zasu karye ko wanni magidanci yana farin ciki da kasancewar wannan Weather mai cike da Ni’imah da kuma sanya shauƙi.

Acan ɓangaren Moddibo kuwa da yammaci misalin ƙarfe biyar M Jameel ne zaune aka 2sitter yayin da Moddibo ke kwance akan 3sitter yayi rub da ciki idanunsa alumshe.

Anutse M Jameel ya ɗago kansa daga kan system tare da kallon Moddibo cikin yanayin shaƙuwa da ƙaunar junansu yace.

“A.J muje gidan Ummi mana”.

Cikin Yanayin buƙata da tsananin sha’awar dake addabarsa ya damƙe ƙasan mararsa waye wan garin yau yasha ruwan lipton da lemun tsami har ya godewa Allah amma ko kaɗan abinda yake ji bai raguba hakan yasa ya kasa furta komai.

Jin kamar bai jiba yasa M Jameel sake maimaitawa.

Ahankali Moddibo ya ɗago Idanunsa cikin raunin murya da yanayin harbawan da ɗin sa keyi kana muryarsa Asanyaye ya kalli M Jameel tare da cewa.

“J bazan iya ba Wallahi bazan iya ba”.

Ya faɗa yana lumshe Idanunsa ajikinsa yana jin tamkar idan ya miƙe  ɗin sa zai tsinke baki ɗaya ya rasa inda zai sanya ransa yaji daɗi ji yake tamkar ya ɗaura hannunsa akai yaita zunɗuma ihu koda zaiji sanyin Aransa baki ɗaya lips ɗin sa rawa suke idanunsa sun sauya launi zuwa ja jijiyoyin goshinsa sun tashi yayin da goshinsa ke tsata-tsafo da zufa.

 

M Jameel kuwa lura da yanayin da yake ciki da yayi yasa ya miƙe tare da nufar kichen kamar ko yaushe ruwan Tea da lemun tsami da kuma zuma ya haɗa masa kana ya fito ya miƙa masa tare da cewa.

“Gashi kasha”.

Ba musu Moddibo ya sanya hannu ya karɓa domin baya cikin yanayin da zai iya musa masa ahankali yakai kofin bakinsa tare da kafa kai ya shanye saboda yanda yake ji ajikinsa.

Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe kana cikin sanyin murya yace.

“Tun da kasha ka kwanta Insha Allah zaka ji sauƙi bari zanje gidan Ummi anjima zan dawo bazan daɗe ba”.

Kai Moddibo ya gyaɗa masa still Idanunsa alumshe M Jameel kuwa key mota ya ɗauka tare da ficewa kai tsaye gidan Ummi ya nufa.

 

Yana isa yayi Parking Cike da nutsuwa ya buɗe Murfin motar ya fita tare da duba agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa dake nuni da ƙarfe 5:15 lumshe idanunsa yayi kana ya buɗe tare da nufar cikin Falon bakinsa ɗauke da Sallama shiru falon ba kowa sai dai komai akimtse kana ga ƙamshin tularen wuta dana Room freshner dake tashi, Murmushi yayi Aransa yace.

“Allah sarki Ummina ba dai tsafta ba”.

Numfashi ya fesar tare da nufar kichen inda yake jiyo motsinta.

Tsaye yasame ta a kichen ta tuƙa tuwo tana kwashewa aleda cike da so da ƙauna yace.

“Ummina”.

Juyawa Ummi tayi fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi ta kallesa kana tace.

“A’a yaushe kashigo?”.

Yana ƙara sa shiga kichen ɗin yace.

“Yanzu Ummina”.

Juyawa Ummi tayi tare da leƙa bayansa”.

Dariya yayi kana yace.

“Nasan wa kike nema ai”.

Murmushi tayi kana tace.

“Eh to ai ban gan shi bane naga Hussain banga Hassan ba”.

Cikin sanyin murya yace.

“Yana gida Ummi yau yana ɗan jin zazzaɓi ne shiyasa bamu zo tare ba”.

Girgiza kai Ummi tayi cike da tausayawa tace.

“Subhanallah Ubangiji ya bashi lafiya Allah ya sawwaƙa mishi”.

Ahankali M Jameel yace.

“Ameen”.

Kana ya matsa jikin kular yana ƙoƙarin budewa yace.

“Ummina yau me kika girka mana ne?”.

Murmushi tayi kana tace.

“Tuwo ne”.

Wara ido yayi tare da cewa.

“Miyar me za kiyi mana Ummi?”.

 

Tana ƙoƙarin wanke nama ta kallesa kana tace.

“Miyar taushe zanyi”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“A to asamana nama da yawa”.

“Toh Babana za’a saka”.

Ta ida maganar tare da ɗaura naman akan gas kana ta yanka albasa tare da sanya Maggi, citta kamafari ta rufe.

M Jameel kuwa Attaruhu, Albasa,Tattasai ya haɗa ya wanke tare da gyarawa kana ya ɗauko blander ya zuba.

Kallonsa Ummi tayi kana tace.

“Ka bari fa da yaji kada yashiga Idon ka”.

Kai ya girgiza tare da cewa.

“A’a Ummi kibari in tayaki nima yau na samu ladan da Asma’u ke samu dana iyama ni zan miki girkin nan”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Ai dai kam hakan ma Nagode yayi Allah yayi albarka Ubangiji ya tsareka daga sharrin duk kan abinƙi kuma ai kafin Asma’u samun lada in sha Allah”.

Kallonta yayi kana yace.

“Ameen Ummina”.

Ummi kuwa buɗe tukunyar tayi tare da zuba mai kana ta zuba jejjegen da M Jameel Yayi a blander.

M Jameel dake gyara kifi banda ya juya ya kalli Ummi tare da cewa.

“Ummi ya yau naji gidan Shiru ina Asma’u da Bashir”.

Tana ɓare Maggi tace.

“Sunje gidan Goggon su takwarar Asma’u”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Ayyah shiyasa yau naji gidan shiru sun barki ke kaɗai to Malam fa?”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Ai dai kam Malam kuma yaje wata rugar Fulani nan kusa amma sai gobe zai dawo acan zai kwana”.

 

Kai ya jinjina tare da cewa.

“Ashe dai yauma kam zan ta yaki ɗebe kewa gidan nan”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Ai dai kam ko zamu kwana ne?”.

Ahankali ya juya ya kalleta tare da cewa.

“Da nafi kowa farin ciki Ummina ace zan kwana gida ɗaya dake”.

Murmushi Ummi tayi batare da tace komai ba.

Ana kiran sallar maghariba suka gama dai-dai lokacin kuma Asma’u da Bashir suka dawo atare, alwala M Jameel Yayi kana Bashir ma yayi hannun Bashir ya riƙe suka tafi masallaci su kuma sukayi alwala tare da gabatar da Sallah.

M Jameel kuwa koda suka idar da Sallah basu dawo ba saida sukayi Isha’i sannan suka fito.

Asma’u kuwa Anutse ta fito daga Bedroom bayan ta idar da sallah kusa da Ummi ta zauna kana tace.

“Ummina Ayyah yau aiki ke kaɗai”.

Kallonta Ummi tayi kana tayi murmushi tare da cewa.

“Ina kuwa nayi aiki Ni kaɗai Yayanku yazo ya tayani yau shiya mana miya ma”.

Wara ido Asma’u tayi tare da sakin murmushi kana tace.

“A lallai kai ashe yau zamu sha miyar Yaya kenan”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.

“A sosai kam zaku sha miyar Yaya Jameel”.

Atare M Jameel da Bashir suka shigo tare da zama.

 

Gnin shigowarsu yasa ta miƙe tashiga kichen kular tuwon ta ɗauko kana ta koma ta ɗauko Plate-plate ta dawo Ummi ce ta karba ta sakawa M Jameel kana ta zuba masa miya agefe sannan ta zubawa Asma’u da Bashir.

Ahankali M Jameel ya kalli Ummi kana ya kalli Asma’u da Bashir sai kuma ya kalli tuwon Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa.

“Toh Ummi muci tare mana musamu ladan cin abinci tare”.

Ɗagowa Ummi tare da kallon sa kana tace.

“Kuma dai”.

Cikin wani irin yanayi ya gyaɗa mata kai kana yace.

“Allah kuwa Ummi”.

Kallonsa ya mayar kan Asma’u tare da cewa.

“Asmeey jeki ɗauko Tray babba ki kawo mana”.

Kai Asma’u ta gyaɗa kana tace.

“Toh Yaya Jameel”,.

Sannan ta miƙe ta shiga kichen ɗin ta ɗauko Babban faranti ta fito dashi tana ƙoƙarin juyewa yace.

“Kawo in zuba mana”.

Murmushi Asma’u tayi tare da faɗin.

“Yah Jameel da kan ka kabari zan zuba mana”,

Girgiza kai yayi kana yace.

“A’a Asma’u kawo in zuba mana bana so ki wahalar da kanki”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Laaa Yah Jameel ka jika Allah zanyi mana”.

Lumshe Idanunsa yayi tare da saurin dafe ƙirjinsa kana ya buɗe Idanunsa tare da Kallonsu ɗaya bayan ɗaya tare da cewa.

“No Asmeey ki bari in zuba mana kaɗai”.

Saurin Kallonsa tayi tare da miƙa masa Plate ɗin.

 

Murmushi yayi tare ɗaukar Plate ɗin tuwon ya zuba musu akan babban farantin kana ya ɗauka ya ajiye musu Atsakiyar su tare da kallon Bashir yace.

“Ɗauko Mana drinks”.

Kai Bashir ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh”,Kana ya miƙe ya ɗauki Plate ya ɗebo drinks da swan water ya ajiye musu.

Ya zauna sai ya zamana M Jameel da Ummi na facing juna Asma’u da Bashir ma na facing juna sai ya zama sunyi Cycle plate din na tsakiyar su.

 

Ummi kuwa shiru tayi tare da zubawa M Jameel Ido Batare da tace komai ba kana tana jin wani irin yanayi mara misaltuwa azuciyarta wanda takasa sanin na menene hakanan ta tsinci kanta da Kallonsa acikin kwanakin nan.

Ahankali M Jameel ya janyo kular miyar tare da ƙara musu namar da bandan kifi kana fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Hayya kuci yau zakuci miyar da baku taɓa ciba irinta ba dan ni nayita ko Ummi?”.

Ya faɗa tare da ɗago kai sai yaga baki ɗaya Idanun Ummi na kansa faɗaɗa Murmushin fuskarsa yayi tare da cewa.

“Kai Ummina ya dai?,Ai gaskiya na faɗa”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.

“A gaskiya ka faɗa kam”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Toh Ummi kici mana”.

Dariya Ummi tayi tare da girgiza kai kana tace.

“A’a kai da kayi dai ka fara ci muga result ɗin da fuskarka zai bayar kafin mufara ci”.

Wara ido yayi tare da kallon Asma’u da Bashir da suma Kallonsa suke,

“Toh ɗan Auta fara ɗana mana muji”.

Kai Bashir ya gyaɗa kana ya gutsiri loma ɗaya yakai bakin sa lumshe ido yayi tare da haɗa yatsunsa hannu biyu alamar jinjina kana yace.

“Kai amma miyar tayi daɗi gaskiya Yah Jameel na baka Award”.

Murmushi Ummi tayi tare da kallon M Jameel da Yayi wani irin kyau na ban mamaki tamkar wanda aka sanya shi a inji aka sake ƙenƙesashi ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.

“Uyummm toni nayi bashi ba”.

Dariya M Jameel Yayi wanda ya bayyanar da Fararen haƙoransa kana yace.

“Toh na yarda Ummi mu duka biyu mukayi”.

Murmushi Asma’u tayi tare da kallon M Jameel kana tace.

“Aikuwa Yaya Kayi ƙoƙari sosai amma muci kada yayi sanyi”.

Kai suka gyaɗa atare kana lokaci ɗaya suka sanya hannunsu akan tuwon tare da kai tuwon bakinsu  lokaci ɗaya suka kalli juna tare da sakin murmushi.

M Jameel kuwa murmushi ya saki tare da lumshe Idanunsa kana yace.

“Ina ma ace zamu kasance ahaka ko yaushe mu riƙa zama tare nuna cin abinci atare da nafi kowa farin ciki”.

Asma’u da takai nama bakinta ta kallesa kana tace.

“Yah Jameel zamu kasance atare mana Insha Allah”.

Kai ya Girgiza tare da cewa.

“Dole wataran fa zan barku sai dai ku zauna ku uku kuci abinci ba tare dani ba”.

Cikin sauri suka kallesa  Bashir yace.

“A’a Yaya Jameel mai yasa zakace haka insha Allah zamu kasance atare”.

Ummi kuwa Kallonsa kawai take.

Murmushi M Jameel Yayi tare da kurɓan drinks kana yace.

”Dole wataran zan barku zanyi tafiya gari mai nisa wanda zan kasance Ni kaɗai acan batare da kuba nasan zanyi kewar ku kamar yanda zakuyi nawa tunda Abba ya dage dole zan koma Marrocco”.

Kai suka gyaɗa tare da sauƙe ajiyar zuciya kana suka ci gaba da cin abinci batare da wanin su ya sake magana ba sai dai lokaci zuwa lokaci yakan kallesu tare da sakin murmushi.

 

Wayar M Jameel ne ya karaɗe wajen da ruri ahankali ya ɗauka tare da sakin murmushi kana yayi Picking tare da Sallama.

Daga ɗaya ɓangaren kuwa cikin sanyin murya Moddibo yace.

“J ina ka tsaya na jika shiru ko abinci banci ba, sannan kasan bani da lafiya ko dai har yanzu kana gidan Ummi ne?”.

Murmushi M Jameel Yayi tare da gyara zaman wayar akunnensa kana yace.

“Ayyah sannu A.J Please kaci abinci sannan ka sake shan maganin dana haɗa maka Insha Allah ina hanya”.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da sakin ajiyar zuciya kana.

“Toh shikenan sai kazo kace ina Gaishe da Ummina”.

Murmushi M Jameel Yayi tare da kallon Ummi dake sauraron duk abinda suke faɗa kana yace.

“Zata ji”,daga haka ya katse kiran.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“Ohh ina ga dai wannan ko kunyi Aure gida ɗaya zaku zauna bakwa iya minti talatin batare da kunga juna ba ko kuma kunji muryan juna”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Ai dai kam dole watarana arabu”.

Jinjina kai Ummi tayi,tana murmushi kana suka cigaba da cin abincin.

 

Bayan sun cinye tuwon farantin M Jameel ya Kalli Ummi tare da cewa.

“Ummi aƙara mana yau ina jin daɗin abinci ina so inci³ incika cikina dan ban sani ba sai kuma yaushe zan sake ci”.

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.

“A’a to ai ko yaushe ma kakeso ai zaka zo kaci”.

Lumshe Idanunsa yayi tare da buɗe su akan Ummi kana yace.

“Toh Ummi kwanan nan zamu fara batun aikin nan kinga in dan na tafi Marocco ai bazan dinga samun ciba”.

Kai ta jinjina tare da faɗin.

“Ai in dai nan da ne ba nisa bane dashi idan ya kama sai inmaka miya da komai duk zan aika maka dasu idan yaso saika na sawa a fridge”.

Murmushi Yayi tare da cewa.

“Hmmyyym Ummina Allah ya ƙara miki nisan kwana mai amfani Allah ya barmu tare”.

Jingjna kai tayi tare da faɗin.

“Ameen Babana Allah ya ƙara maka nisan kwana inga har jikokin ka”.

Murmushi yayi tare da kallonta kana yace.

“Hmmm Ummina kenan.

Kin ko san in sha Allah ƴata ta farko sunanki zan samata,

Na kuwa tabbatar zata ga soyayya ko ƙuda bazan bari ya taɓa ta ba”.

Kallonsa Ummi tayi tare da cewa.

“Jamiluuu na”.

taja sunan tana murmushi haka nan take jin daɗin kiran sunan sa.

 

Bayan sun kammala cin abincin Asma’u ta miƙe tare da tattare Plate ta Kai kichen M Jameel kuwa da kansa ya mike ya ɗauki kular abincin ya kai kichen Ummi kuwa Kallonsa ta riƙa yi cike da so.

Bayan ya ajiye ya fito, woje ya nufa yana cewa

 

“Bari in ɗauko abu a mota”.

Toh Ummi tace kana ta meda hankali kan tv.

Jim kaɗan da fitar da ya shigo riƙe da kwalayen waya masu kyau.

Ƙirar Samson, kana ya  dawo ya zauna gefen Ummi Asma’u da Bashir suka zauna daga gefensa gyaran murya yayi tare da fuskantar Asma’u kana yace.

“Ga woyoyinku nan Asma’u yau dai na cika alƙawarin ko”.

Cikin tsananin jin dadi Bashir ya ruggumshi, yayinda Asma’u kuwa Ummu ta ruggume.

Cikin son juna suka rinƙayi mishi godiya tare da fatan al’khairi.

Murmushin jin dadi yayi tare da shafa kan Bashir kana yace.

“Asma’u yanzu ke wani irin makaranta kike so?”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Yah Jameel duk makarantar da ka zaɓa min ina sonta ina farin ciki da ita”.

Jinjina kai yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana yace.

“Zan kuwa zaɓa miki wanda ya dace dake  Insha Allah naga keda ƙawarki kusan ra’ayin ku ɗaya ko yaushe amman wannan karon an samu akasi ita Jenouelist take fata naga ke kuma likitanci kike son karanta”.

Kallon Bashir yayi tare da cewa.

“Kai kuma wani irin Makaranta kake so?”.

Murmushi Bashir yayi kana yace.

“Duk wanda ka zaɓa min Yaya”.

Lumshe idanu M Jameel Yayi tare da cewa.

“Insha Allah kuwa zan zaɓa maka ina ganin Law zaka karanta zaifi dacewa da kai”.

Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana ya tsira musu ido tare da cewa.

“Asma’u”.

Kanta ta ɗago tare da cewa.

“Na’am Yaya”.

Anutse ya kalleta cikin yanayin nutsuwarsa da alamun rashin wasa yace.

“Kinga ke ƴa macece ita rayuwar duniyar nan duk i da ƴa mace ta tsinci kanta ta tsare mutuncinta da darajar ta shine abu mafi daraja ki kiyaye tarbiyyar da muka sha wahalar baki nida Ummi kada ki kunya tamu kada kisa ta baƙin ciki”.

A hankali ya sauƙe numfashi tare da gyara zamansa kana yace.

“Saboda ke ƴa macece ke mukafi taraddadi akan ki kinga yanzu ga Bashir amma bana ta raddadi akansa kamar ke mace”.

Asma’u kuwa ƙasa ta sakeyi da kanta batare da tace komai ba sai wasa da yatsun hannunta da take yi.

 

lumshe idanunsa yayi kana yace.

“Burina da fatana inga mun kasance gida ɗaya muhalli ɗaya wallahi akanki da Bashir da kuma Ummin mu yasa nake so inyi Aure inga muna tare”.

Sai kuma ya kalli Bashir da shima yayi ƙasa da kansa kana yace.

“Ina so inga lokacin tafiyarku makarantar kana inga lokacin dawowan ku a idona sannan insan kalar mutanen da kuke mu’amala dasu”.

Sai kuma ya juyo ya kalli Asma’u cikin yaƙini yace.

“Na yarda da ƙawancen ku da Khausar saboda tana da tarbiyya duk da kuwa tana da rawan kai”.

Numfasa yayi tare da kallon ta kana cikin raunin murya yace.

“Asma’u ki kula da rayuwarki sannan kisan irin mutanen da zaki dinga alaƙa dasu idan kuma har Aure kike so Asma’u ki faɗa min idan yaso idan kikayi aure sai ki cigaba da karatun ki agidan mijinki kada ki ɓoye min ki faɗa min komai ki ɗaukeni tamkar ƴar Uwarki mace”.

 

Cike da kunya Asma’u tayi ƙasa da kanta tare da girgiza kanta kana tace.

“A’a Yah Jameel nikam karatu zanyi”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Kin tabbatar ba Aure kike so ba sannan babu wanda kike so?”.

Cike da kunya ta girgiza masa kai tare da faɗin.

“Yaya Jameel Ni kuma wazan so kuma babu wanda ke zuwa gurina”.

 

Dariya M Jameel Yayi tare da kallonta kana yace.

“Mun shiga uku Ummi kadde ƙanwar tawa baƙin jini take dashi?”.

Murmushi Ummi dake aikin Kallonsu tayi tare da faɗin.

“Ba wani baƙin jini kawai dai dake tana kiyaye kanta ne babu wanda ke kawo mata wargi”.

Jinjina kai yayi tare da dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace.

“Toh shikenan Asma’u tun da dai kin bani tabbacin karatu kike so daga nan harki kai digir-gire ki gama har ki taka duk kan matakin da kike so nayi al’ƙawarin zan taimaka miki da duk kan ƙarfina da kuɗina muddin ina numfashi zan tsaya miki”.

 

Kallon Bashir yayi tare da cewa.

“Sannan kai kuma Bashir zaka karanci fannin Law tunda kana da ilimin addini ina da yaƙinin zaka tsaya akan gaskiya duk runtsi duk wuya kada Kabi bayan ƙarya ka kasance mai al’ƙawarin  da rikon amana aduk inda ka tsinci kan ka”.

Jinjina kai Bashir yayi kana yace.

“Yah Jameel Insha Allah Nayi alƙawari zan kasance ayanda kake fata”.

 

Hira suka cigaba dayi sosai irin wanda suka ɗauki tsawon lokaci basuyi irin saba wanda har dare yaraba basu lura ba.

Ahankali Ummi dake murmushi ta daga kanta Idanunta suka sauka akan agogon dake manne abango wanda ke nuni da ƙarfe sha biyu da minti goma,Cikin sauri ta kalli M Jameel tare da cewa.

“Jamilu”.

Anutse ya ɗago ya kalleta tare da cewa.

“Na’am Ummina”.

Ta sauƙe ajiyar zuciya tare da Kallonsa kana ta sake kallon agogon zuciyarta na bugawa tayi saurin dafe ƙirjinta kana tace.

“Ka kalli time fa”.

Cikin sauri M Jameel ya juya Kalli agogo tare da kallon Ummi kana…!

Cikin sakin fuska yace.

“Ummi yau anan zan kwana”.

Cike da mamaki Ummi ta juya ta kallesa, domin tunda Allah yasa tayi aure agidan mahaifin Asma’u bai taɓa kwana ba, sai dai yakan zo aduk sanda yaga dama, a hankali ta sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.

“Anan zaka kwana?”.

Kai ya jinjina tare da faɗin.

“Eh zan kwana Ummina”.

Kallon Ummi Bashir yayi cike da farin ciki ya langwaɓar da kai kana yace.

“Ayyah Ummi ki barshi kinga yanzu ma dare yayi ki gani fa sha biyu hadda kwata dare fa ya riga da yayi nisa”.

Cikin sanyin murya me ɗauke da farin ciki Asma’u tace.

“Gaskiya dai kam mu kwana kawai Yah Jameel, yau nayi matuƙar farin ciki zamu kwana agida ɗaya Allah ya nuna mana ranan Aurenka mu kasance atare na har abadan”.

Murmushi M Jameel yayi tare da shafa sajensa kana ya tsira musu ido tare da lumshe idanunsa, a hankali ya sauƙe ajiyar zuciya kana yace.

“Asmeey zamu kasance atare in sha Allah zanyi Aure kana zaku kasance  gida me kyau da na al’farma da kwanciyar hankali, ni kaina bansan kamannin gidan ba amma na sani gida ne mai masifar kyau da ɗaukar hankali zan riska in sha Allah”,

Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da lumshe idanunsa kana yaci gaba da cewa.

“Wanda kowa ke burin samu, in Sha Allah zan sameshi, domin inaji ajikina na kusa isa wannan gidan kafin ku iso zan kasance cikin farin ciki amma idan ina tare daku zanfi farin ciki na zai fi nin kuwa”.

Cikin yanayin sanyin jiki ya tsira musu ido su duka ukun.

Ummi kuwa idanu ta zuba masa ko ƙyaftawa ba tayi wani irin yanayi takeji azuciyarta, wanda takasa tantance na menene.

Asma’u kuwa murmushi tayi tare da Kallonsa kana tace.

“Yaya Jameel Allah ya baka mace ta gari wacce zata kula da Ummin mu tamkar yanda kake kulawa da ita sannan ta ƙaunace mu tamkar yanda kake ƙaunar mu”.

Murmushi yayi kana ya lumshe idanunsa tare da cewa.

“Insha Allah Asmeey matar da zan Aura, macece wacce ta fito daga babban gidane masu tarbiyya da kamala, wacce zata riƙe Ummina daku tamkar Iyayen ta da kuma ƙannenta”.

 

Sai kuma ya numfasa tare da tsira mata ido.

 

Kai Asma’u ta gyaɗa murya cike da jin daɗi tace.

“Ni kuwa Yah Jameel Nayi maka al’ƙawarin zan kasance mata tamkar yar uwa Aminiya yadda kake fata har ma fiye da haka”.

Sassayan numfashi ya fesar kana yace.

“Alhamdulillah Asmeey idan kika min haka ko a ina na kasance zanyi al’fari dake sannan zanyi farin ciki”.

Sai kuma ya maida kallonsa kan Bashir tare da cewa.

“Yauwa kai kuma Bashir”.

Anutse ya ɗago kansa tare da faɗin.

“Na’am Yah Jameel”.

cikin sanyin murya yace.

“Bashir ka maida hankalin ka akan karatun ka, kada ka biyewa aboka nan banza kasan dawaye ya dace kayi abota kada ka biyewa matan banza da abokan baza kada kasa Ummi tayi Allah wadai da halayyar ka”.

Ƙasa da kai Bashir yayi yayin da Ummi kuma shiru tai tana mai jin daɗin Nasiyyar da yake wa ƙannensa.

A hankali ya numfasa kana yaci gaba cewa.

“Bashir aikin Law aikine mai matuƙar daraja da muhimmanci sai dai wasu sun ɓata aikin da cin hanci da rashawa da tauye haƙƙin masu gaskiya, da tozartasu, ina so kamin alƙawari kai zaka kasance mutum mai adalci da karamci akan aikinsa wanda duniya za tayi al’fahari da kai sannan Ummina tayi farin ciki da rayuwarka”.

Sai kuma ya ɗanyi shiru yana kallon yadda Bashir ke gyaɗa masa kai alamar nasihar na ratsashi, cikin yanayin lallashi da jan hankali yaci gaba.

“Dan Allah Bashir kada ka bari adalilinka Al’umma su la’anci Ummina suyi Allah wadai da haihuwarka da tayi”.

Cikin rawan murya Bashir yace.

“In sha Allah zan zama yanda kake da buri har ma fiye da haka Yah Jameel”.

Lumshe Idanu M Jameel Yayi tare da shafa sajensa kana cikin sanyin murya yace.

“Nagode Bashir tabbas ko bayan ba nan Idan ka kasance mutumin kirki zanyi farin ciki, sannan ka kula min da Ummina da Asma’u kada ka bari hawayen baƙin ciki ya zubo daga idanunsu ni dai burina kayi min wannan al’ƙawarin”.

Jinjina kai Bashir yayi tare da cewa.

“Nayi maka alƙawari Yah Jameel Ummi da Asma’u baza su taɓa baƙin ciki dani ba, kullum zan saka su farin ciki sannan zan kasance mai riƙon alƙawari aduk inda na tsinci kaina”.

 

Murmushi M Jameel Yayi Idanunsa alumshe yace.

“Alhamdulillah³ Allah na gode maka”.

Anutse ya juya ya kalli Ummi data tsira musu Ido kana cikin sanyin murya yace.

“Yauwa Ummina faɗamin me kike buƙata ko kuma kike so arayuwar ki nayi miki?”.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tayi murmushi tare da cewa.

“Toh ni kuma meya rage arayuwa wanda baka yimin ba Jamilu?

Ai ni kam kayi min komai sai dai Ubangiji Allah ya maka albarka Allah yabaka ƴaƴan da zasu yi maka biyayya”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ameen Ummina amma yanzu baki da wata damuwa ko buƙata?”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Bani da wani damuwa ko buƙata aduniya Jamilu, domin kafin na buƙaci komai ma kiyi min”.

Hannunsa biyu ya ɗaga sama tare da faɗin.

“Alhamdulillah Allah Nagode maka ya Ubangijin Allah ka bani damar da duk ɓuƙatar da mahaifiyata take dashi kafin ma ta buƙata nayi mata shi”.

 

Murmushi tayi kana tace.

“Ameen Ubangiji Allah ya maka albarka Allah ya rufa maka asiri duniya da lahira Allah yasa ƴaƴan ka su ramamaka abinda kayi mana”.

Still Fuskarsa ɗauke da murmushi yace.

“Ameen ya Allah”.

Ummi kuwa ahankali ta daga kanta gani tayi har ƙarfe uku kallonta ta mayar kansu kana tace.

“Yanzu yaranan baza ku tashi kuje ku kwanta ba ku dubi time fa”.

Atare Asma’u da Bashir suka ce.

“Toh Ummi am gaba ɗaya yau bama jin baccin ma”.

Murmushi M Jameel Yayi kana yace.

“Ai dai kam”,

Ummi kuwa murmushi tayi kana suka cigaba da hira.

Jin ankira Sallar ƙarfe huɗu yasa Ummi kallon su tare da faɗin.

“Toh yanzu kam mutashi muyi alwala muyi nafillah mu rufe wannan daren da roƙon Ubangiji”.

 

Bayan duk sunyi Al’wala ne suka dawo falo duk suka shimfida Sallaya sukayi nafila raka’a huɗu-hudu.

 

M Jameel kuwa acikin sujjadar ta ƙarshene yace.

“Ya Allah katsare min Mahaifiyata da ƙannena Ubangiji ka zama gatansu anan duniya da lahira ya Allah ka tsaresu daga sharrin abin ƙi Ubangiji ka inganta rayuwar Asma’u da Bashir ya Allah ka tabbatarwa da A.J na al’khairi a cikin samun mace tagari wacce zata kula da ɗawainiyarsa ya Allah kabiyawa duk musulmi ɓuƙatar su na Alkhairi”.

Ko wannensu haka ya dinga addu’a saida aka kira Assalatu kafin suka miƙe Shida Bashir suka tafi masallaci Asma’u da Ummi kuwa anan suka Idar da Sallah.

 

Bayan sun dawa daga masallaci M Jameel ya kwanta akan 3sitter Ummi Atake Bacci mai daɗi ya ɗaukesa.

Ummi da Asma’u kuwa kichen suka shiga tare da soya musu soyayyen dankali da ƙwai kana suka tafasa ruwan tea da yaji citta da kanumfari sai kuma tayi musu ɗumamen tuwon jiya, ganin yadda yaketa zuba tururine yasa Asma’u tas hannun da nufin buɗe  murfin tukunya, zafin da taji ya ratsa ƴan yatsunta ne yasa ta saki karfin ya faɗi ƙasa tare da bada ƙara.

Cikin sauri Ummi ta kalleta kana cikin ƙasa da murya tace.

“Kai Asma’u kiyi a hankali mana kada ki tashi yayan ku, bakiga jiya bai samu bacci ba”.

Murmushi Asma’u tare da gyaɗa mata kai kana tace.

“Toh Ummi”.

 

Har misalin ƙarfe tara M Jameel bai far kaba Ummi kuwa toilet tashiga tayi wanka bayan ta shirya ta fito falon har zuwa lokacin M Jameel na bacci ahankali ta zauna agefensa tare da tsira masa idanu tana kallon yanda yake baccin cikin kwanciyar hankali tamkar yana murmushi kyawun fuskarsa ya sake nunkuwa fiye da ko yaushe.

 

Asma’u data fito daga kichen ta kalli Ummi kana ta saki murmushi tare da cewa.

“Kayyy Ummi irin wannan kallon sai kace kin samu TV ”.

Sai asannan Ummi ta ɗauke Idanunta daga kansa ta mayar kan Asma’u tare da yi mata daƙuwa.

Murmushi Asma’u tayi kana tace.

“Ai gaskiya ne”.

Bashir daya shigo Bedroom din yayi dariya kana yace.

“Gsky dai Ummi kwanan nan kina yawan kallon Yah Jameel ko dan yafi mu kyaune?”.

Wara ido tayi tare da sakin murmushi kana tace.

“Waya faɗa maka yafi ka kyau ai kafisa”.

Murmushi yayi kana yace.

“Ummina kin dai faɗa min inji daɗi ne kawai”.

M Jameel kuwa cikin bacci yake jiyo hiransu sama-sana ahankali ya motsa.

Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da kallon sa kana tace.

“Toh katashi kayi Breakfast. Idan yaso sai ka koma baccin”.

Cikin sauri ya buɗe Idanunsa tare da Kallon Ummi kana yace.

“Uhmmm Ummi sai anjima”.

Kansa ta shafa kana tace.

“A’a tashi kaci abinci, bana son bacci da yunwa Babana”.

Hannunta ya riƙe kana yace.

“Naji daɗina Ummina ta kirani da Babana Abbana ya kirani da Babana”.

Miƙewa yayi ya zauna tare da cewa.

“Ummina banyi wanka ba sannan banyi brush ba ba zan iya Breakfast ba”.

Girgiza kai Ummi tayi tare da faɗin.

“Aikam dai gashi tun ɗazu na bawa Bashir kuɗi ya sayo maka Brush kafin ka tashi ga Brush ga Maclean kayi”.

Miƙewa yayi kana ya ɗauka, toilet dake falon yashiga ya wanke bakakinsa.

Asma’u kuwa tun shigansa toilet ta Miƙe tankwaso musu kayan Breakfast ɗin yau ma kamar jiya haka atare sukayi Breakfast ɗin.

A hankali ya kai kofin tea bakinsa sai kuma yayi sauri ajiye cup din jin wayarsa ta hau ruri Asma’u dake kusa da wayar ta miƙa masa karɓa yayi tare da sakin murmushi kana yayi Picking tare da cewa.

“Assalamu Alaikum A.J”.

Daga ɗaya ɓangaren Moddibo ne yace.

“J yana jika shiru gashi Innayi ta haɗa mana Breakfast na kasa ci ni kaɗai”.

Murmushi M Jameel yayi tare da kallon Ummi, Asma’u,da Bashir kana yace.

“A.J gani tare da Ummina da Asma’u da kuma Bashir muna Breakfast tray ɗaya kamar yanda mukayi jiya, ina jin farin ciki inaji kamar wani gurbi na cike wanda ban samu damar cike saba tsawon shekaru”.

Lumshe idanu Moddibo yayi kana ya gyaɗa kansa tabbas ya fahimci farin cikin da M Jameel ke ciki ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa.

“Shikenan hakan yayi kyau bawa Ummina mu gaisa”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da miƙawa Ummi wayar.

Cike da so Ummi tace.

“Babana na ƙwace maka Amini ko?”.

Murmushi Moddibo yayi wanda take iya jiyo sautin sa kana cike da ladabi yace.

“Ayyah Ummina bakomai ai kawai ina kewar sa ne Ina kwana?”.

Murmushi tayi tare da faɗin.

“Lafiya Lau ya Innayi?”.

Ahankali yace.

“Tana lafiya tace agaishe  ki”.

Daga haka sukayi sallama tare da katse kiran Bayan sun kammala Breakfast ɗin Asma’u ta tattare kwanikan kare da kaiwa kichen kana ta dawo ta gyara wajen.

M Jameel kuwa jingina kansa da guiwar Ummi yayi kana suka cigaba da hira cike da tsananin ƙaunar junansu…!

 

 

 

 

*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*

 

 

By

*GARKUWAR MARUBUTA*

Leave a Reply

Back to top button