A Rubuce Take Book 2Hausa Novels

A Rubuce Take Book 2 Page 31

Sponsored Links

Part 02

Page 31

Zuwa azahar abba mahmud ya iso,ba dadewa saiga uncle muhsin shima takanas,wanda sam baisan abinda yake faruwa ba sai sannan,suka zauna shida sauran qannensa biyu dake binsa dukka cikin falon ummu,ya dubi widad da fuskar nan tasa dake nuna tsantsar da gaske yake,ya kirayi sunan widad din,wadda duna daya ta yiwa fuskarsa yawun bakinta ya dauke tsaf!!,tasan waye abban,tasan halinsa sarai,baya daukan wasa ko raini,hakanan bayason rashin gaskiya kaf rayuwarsa

“Ki gayamin tsakaninki da Allah me ya faru?” Bakinta ne ya fara rawa,cikin kakkausar murya yace

“Ki nutsu kiyimin bayani,idan kuma baki da gaskiya ne kiyi gaggawar fadamin basai kin batawa kowa lokaci ba” ta rufe idanunta sosai tana son bawa zuciyarta haquri ta kuma dai dai tata,saita fara gaya masa komai daki daki harta kammala.

“Wayeshi abubakar din?”

“Abubakar dai fa daka sani” uncle bashir ya amsa masa,sake waiwayawa abba yayi ga widad

“Wannan abun da kika fada ayanzun idan baki qur’ani zaki iya dafawa ki sake rantsewa da hakan shine iya abinda ya taba faruwa?” Da sauri ta jijjiga kai

“Zan rantse abba wallahi zan rantse”

“A bani number wayar abubakar din” ya miqawa uncle bashir wayarsa,ya saka masa number abubakar akayi kiransa.

Yadda widad ta fada din haka shima ya fadi,abba yayi masa sallama ya kashe wahar yana duban widad idanunsa tsar a kanta

“Ashe kece duk kika jawa kanki wannan,ki gayamin uban da yace miki koni na mutu zaki fita daga gidanki kafin ki shaidawa mijinki,kadin kuma ya baki izni ta hanyar amincewa?”

“Nayi kuskure abba,kuma naga indai fita ta uzuri ya kama yana barina ko ban gaya masa ba,saidai idan ya dawo din saina gaya masa……. astagfirullah” ta fada a rude hawaye yana zirarowa saman kuncinta sannan ta fashe da kuka,har affan yana daga kai yana kallon fuskarta sosai,dukka saida kowa a wajen zuciyarsa ta karye, dukkaninsu sunsan halinta,bata qarya ko za’a yanka ne zata fadi gaskiya,tun tashinta haka take.

Sosai ran abba ya sosu,ransa ya kuma baci har ya gaza jurewa

“Wanne irin aure ne wannan kukeyinsa da zargi?,ina akace anayin aure da zargi irin haka,zina fa?”

“Wai ba zargi yakeyi ba,har hujja yana da ita”

“Idan ba zargi bane waye ya gaya masa?”

“Abokiyar zamanta ce” wani balaeen bacin rai ya tasowa abban, musamman shi da ya taba fuskantar halin makirci irin na mata

“Abokiyar zamanta?” Ya maimaita wani bacin ran yana ciyoshi,sai kawai ya kasa sake cewa komai saboda tsananin bacin rai,ya miqe tsam yana cewa ummu

“Ta zauna a wajenki ummu” daga haka ya fice,kowa a wajen ya fahimci yadda ransa yayi mummunar bacin rai,na biyunsa kuwa uncle muhsin ne,wanda shima ya miqe ya fita,ya kuma lalubi number abbas din ya kira.

Daidai lokacin da yake tsaka da aiki da dukkan qananun police dake qasansa da zasuyi aikin tare.

Cikin uniform dinsa dake qara masa kwarjini sosai,fuskarsa a dinke tsaf,a yau din baya ga yanayin aiki da yake sawa ya koma hakan,harda wannan qulalliyar damuwar dake qasan zuciyarsa,wadda ta koma masa abokiyar rayuwar ruhinsa,ya saka hannu a aljihun wandon uniform dinsa ya fidda wayar,ganin sunan muhsin din sai yadan gyara tsaiwarsa,tunda abun ya faru ko sau daya basuyi magana ba,sai ya juya a hankali ya taka yana fita zuwa qofar dan qaramin hall din da suke ganawar sirri.

Kan qaramar barandar dake wajen ya tsaya ya daga wayar,suka fara gaisawa kamar komai bai faru ba,sannan a nutse ya jefa masa tambayar abinda yake faruwa tsakaninsu da widad.

Yadda ya gayawa uncle bashir haka ya gayawa muhsin din,ransa yabaci shima

“Yanzun ka yarda da abinda ita ta fada?”

“Bana ce ba,sai nayi bincike kawai,zan sake bincikawa yanzun haka ina katsina ne” kai muhsin ya jijjiga ransa a bace

“Saika gaggauta,saboda ran yaaya mahmud ya baci,kuma nasan halinsa sarai” daga haka ya yanke wayar,abbas din ya sauke wayar daga kunnensa yana kallonta,daga can qasan zuciyarsa ana gaya masa bakayi dai dao ba baka kyautawa,wani sashen kuma yana gaya masa shine dai dai,ya rufe idonsa a hankali yana jin kansa yana masa nauyi,a hankali sai ya fara jinsa kamar iska na kadashi hagu da dama,jinsa ya fara yin qasa hayaniyar dake kusa dashi ta fara komawa nesa dashi,sai kuma yaji kamar qafafunsa sun lanqwashe an turashi,ya tafi luuuuu zai fadi,mutumin dake dauke da posting later dinsa ta sauyin gurin aiki daga kaduna zuwa katsinar ya isa gareshi yayi saurin tareshi yana fadin

“Subhanallah, innalillahi wa inna ilaihi raji’un” sai ya fara neman dauki,wadanda ke kusa suka qaraso suka tayashi riqe abbas din daketa qoqarin daidaita numfashinsa ya kuma miqe ya tsaya da qafafunsa saidai abun yaci tura,sunqi sakinsa don sun tabbatar zai iya faduwa,dole aka dauko motar aiki aka sakashi a ciki suka wuce asibiti dashi.

Ummu tafi kowa saninta da sanin wacece ita,hatta da mahaifiyarta ba zata gaya mata wacece ita ba,zamanta wajen ummun an dan samu ci gaba kadan,ta lalubo abubuwan da takeson ci ta saka latifa na tanadar mata su,a yadda ummun ta lura sai taga kamar qaramin ciki ke sake wahalar da widad din,koda ta gaya mata a gigice ta daga kai ta kalleta cikin tashin hankali gabanta na wani irin faduwa

“Ciki kuma ummu?” Yadda taga hankalinta yayi mugun tashi saita saki murmushi

“Wai hasashe na ne,amma ba lallai ya zamana shi din bane” tabar widad din a haka,don ta fuskanci sanin tana da cikin kamar zai sake zame mata wata qarin damuwa akan wadda take ciki,sai kawai taci gaba da kula da ita a hakan.

Kwanansa biyu a asibitin yana jin jiki,a kwana na ukun yaji dama dama,ya kuma nemi sallama amma likitan yace bazai bashi yanzu ba,sai ya huta sosai,saboda stress yayi masa yawa,so yana buqatar ya samu hutu sosai.

Daga wajen aiki sun bashi kulawa sosai,sun kuma saka an saka komai a gidan da aka bashi zai zauna a zaman aikinsa,koda suka gaya masa shi sai yaji duka wannan ba damuwa bace a wajensa.

Ciki ikon Allah a kwana na ukun yaji ya fara damuwa da yanayin da yake ciki,zuciyarsa ta fara tuhumarsa,ko yaya widad take ba zaka iya zama da ita ba?,ya sadaukar da komai dominka fa. Maganar da wannan raunannan sashen na zuciyarsa ke gaya masa kenan,ya tuna wayarsu ta qarshe da muhsin,wadda daga ita bai kuma kiransa ba,ya kuma tuna yadda ya gaya masa abban ya dauki zafi,mutum me mugun karamci da kirki,sai ya miqe zumbur ya zauna saman gadonsa ya jawo wayarsa.

Kai tsaye ya kira kawu hassan,bayan sun gama gaisawa ya fara masa bayanin biko yakeso suje masa

“Ikon Allah,hafsatun abun yakai har da sake tafiya gida?” Kai ya girgiza yana jin zafi a ransa

“Ba ita bace,widad ce”

“Widad kuma?” Kawun ya tambaya cikin mamaki

“Eh kawu” shuru ya danyi sannan yace

“Allah ya kyauta,amma ya zama dole ka sake zama mai nisan haquri,su mata indai kace ba zaka dinga haquri ba,kowacce ma ba zaka iya zama da ita ba,ko ka auro saisun tafi,kuma zo mu zauna zo mu saba” ya danyi masa fada sannan yace zaiyi magana da ko sunusi ne sai su shiga kanon ko zuwa gobe ne,ya yiwa kawun godiya sosai,yace zai sanya a tura musu kudin da zasu sha mai

“Don qaniyarka muba iyayenka bane,har sai ka bamu kudin mai banda alkhairin da kake mana” wani busashen murmushi ya danyi kawai,ya sake masa godiya ya ajjiye wayar.

Shuru yayi ya jingina da gadon idanunsa a rufe,wata zuciyar na gaya masa ya kyauta,wata kuma tana tuhumarsa,kanme zai dawo da ita bayan babban laifin data aikata?,bata cancanci ya zauna da ita ba,ya rasa wanne matsaya yake a cikin biyun?.

Sai da yayi sallar azahar hafsat ta fado masa a rai,ya dauki wayar yana duba ko akwai kiranta amma babu ko daya tsahon kwana ukun,mamaki ya kamashi,sai ya fara neman layinta.

Sai data kusa da tsinkewa sannan ta daga,murya a daqile tayi masa sallama,ya amsa sa muryarsa mai laushi

“Sai yau ka tuna damu,ni kamar ma mu ka kama a hotel din nan” ta fada cikin gatse,sai yayi shuru yana jinta ransa na masa zafi,batayi dogon nazarin taji sauyi a muryarsa ba ta dora

“Duk masifar ta dawo kanmu,kwana uku kayi tafiya amma ka kasa neman matarka daka bari da yaranka” kansa ya girgiza yana jin ciwo a ransa

“Ke bakisan ki kira mijinki kiji ya ya isa ba?,idan kinji shuru bakisan ki karashi kiji me yake faruwa dashi ba?,bani da lafiya ina asibiti kwana uku amma rashin kulawarki yasa bakisan da hakan ba,da irin wannan halin naki wataran sai an kawo miki gawata unexpected” sai kuma jikinta yayi sanyi,ta danyi shuru sannan ta fara magana

“Ni wallahi bansan baka da lafiya ba,sannu Allah ya sawwaqe ya baka lafiya”

“Ameen” ya amsa can qasa,duk wani karsashinsa babu,sai yaji baya buqatar dogon magana da ita,ya tambayi yara ta hadashi dasu.

Kusan su suka debe masa kewa,yayi hira dasu mai tsayi sannan yasa suka kaiwa mamar tasu wayar,ta tambayeshi wanne asibiti yake,daya gaya mata ya dauka zatayi batun zuwa ganinsa,amma sai tace masa kawai Allah yasa kaffara,akan haka sukayi sallama,sai ya kashe wayar,widad ta fado a ransa,yayi imanin inda itace da yanzun haka ta rude masa gaba daya,ya mirgina kansa gefe yana jin zafin zuwanta hotel,sai yaji ko sunansa bayason ji.

*********Sai da ya gama shirin fitarsa kasuwa sannan ya fito gaba daya,ya samu baqin da akace masa suna jiransa a falon saukar baqi na gidan.

Sukayi gaisuwar mutunci sosai,ya shaida kawu hassan don haka bai buqaci sanin daga ina suke ba,haquri suka bayar kan su din basusan me yake faruwa ba sai daga baya,suka kuma gabatar masa da buqatarsu na abasu bikon widad din tare da alqawarin hakan ba zai sake faruwa ba.

Gyara zamansa sosai abba yayi

“To naji dadin zuwanku,don dama inata shawarar neman daya daga cikinku,batun ya sake faruwa ko kada ya sake faruwa dama bazai sake din ba,saboda a yanzun bana buqatar kowa ya nemi bikon widad,abinda nake buqata don Allah,ku gaya masa ya rubuta takardar sakin diyata ya aikomin da ita,ko ya turomin ni tunda yana da number ta,magana ta biyu kuma,ku gayawa ita abokiyar zaman tata mai shaida da shaidu cewa,ta shirya shiga kotu dani uban widad bisa qazafin zinar data yiwa diyata,zamu shiga kotu har sai gaskiya tayi halinta,walau gaskiyarta ko kuma gaskiyar tawa diyar” dukkansu sun girgiza sun kuma ji babu dadi,don basu zaci wannan hukuncin daga wajen abban ba,sai suka fara qoqarin bashi haquri

“Ai baza’ayi haka ba alhaji”

“Me zai hana ayi haka?,na gama magana kuyi haquri bana maimaici,ya bayar da takarda ita kuma ta shirya shiga kotu,’yata ba mazinaciya bace,ba kuma zata sake zaman zargi ba” daga haka ya musu sallama cikin girmamawa yabar musu falon.

Dole bayan sun gama jimanta maganganun a tsakaninsu suka fito,kowa sai da ransa ya baci dajin cewa wai hafsat ce ta gaya masa anyi haka harda bashi shaidu,kawu hassan bai rufeshi da komai ba,ya kirashi yayi masa tatas,ya kuma bashi saqon abban ya kashe wayarsa abinsa.

*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)

Back to top button