Amatulmaleek Hausa NovelHausa NovelsHausa Novels

Amatulmaleek 15

Sponsored Links

Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

15
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

**********
AmatulMaleek na barin bedroom din Naufal ya daure tareda basarwa yaqi bin bayanta da kallo sbd mum dinsa dayasan idanuwanta na kansa.

Qarasowa yayi kan kujera Dake dakin ya zauna ahankali tareda kallan kayan abincin Dake jere kan table Dake dakin.
Tukuna ya dago a lokacin ya Kalli mum din cikin share abinda take tinani a zuciyarta yace

“Mum bazan iya cin abincin me nauyiba zai dameni”

Kallansa mum Aisha tayi ta hadiye maganar dataso fada sbd kada ma ta ankarar dashi akwai Yan mata a gidan sai kawai ta share abinda ya faru ta Bude Baki tana ajiye wayarta Dake hannunta tana cewa

“Eh Nasa a kawo salad sbd nasan bazaka iya cin abincin Kai tsaye shi Daya ba.”

Numfashi ya sauke Yana gingina bayansa da kujera tareda Kai hannunsa ya lalaba jikinsa Dan dauko wayarsa Amma Babu Saiya Tina baida layin Nigeria shiyasa wayar nacan daki ajiye Saiya huta ya kira a kawo masa.

Shigowar Amatu ne ya katse yar maganar dasuka Shida mum dinsa
Bai dago ya kalletaba yaci gaba da maganarsa kamarma baisan da shigowa Wani Dan adam dinba.

Mum ma Bata Kalli Amatun ba harta qaraso ta ajiye bowl da salad din yake ciki ta juya tabar gurin.

Harta fice Babu Wanda yabi inda tabi da kallo itama Amatun abinda yake gabanta kawai takeyi Dan haka tana baro bangaren Kai tsaye kitchen ta nufa Dake palon Madame abeeda Wanda yanzu bangaren Husnah da Haydar ne kawai sai ita datake Dan kwana da Husnah Wani lokacin Amma dai tama Fi kwana a dakinsu na bangaren masu aikin tinda can suka taso Kuma acan maamah take haryanxu Dan haka batama Wani son zama cikin gidan tafison inda maamah take.

Abdul ma kusan yakoma dakin Haydar duk da kayansa suna dakin maamah har lokacin hakama Wani lokacin a dakin Shima yake zuwa yayi baccin ranarsa.

Girkin abincin dare data Dora ta duba Wanda na Dad din gidan ne Dan Yana gari Kuma maamah ce kawai ke dafa abincin dazaici Babu me Saka hannu Amma Kuma yanzu Amatu na kama mata duk da saidai ta kama mata Amma Bata bar mata girkinsa sbd kiyayewa da Kuma gudun ayi kuskure.

Tana dubawa tabar kitchen din ta nufi bangarensu sbd wanki takeson yi da yamman na undies nata da wasu kayan Maamah.

Tana shiga daki Bata Tararda maamah ba tana gurin mum Aisha Dan haka Bata damuba kayan da zata wanke ta shiga hadawa harta gama hadawa ta fito dasu zuwa Baya inda suke wanki maamh Bata dawoba.

Wankinta tayi ta gama sai guraren magrib ta shige taje tayi sallah tayi wanka ta fito sanyeda hijab dogo har qasa sbd jikinta ba Wani kaya doguwar rigar bacci ne a jikinta shiyasa ta Sako dogon hijab din.

Kai tsaye kitchen data San maamah na can ta nufa ta Tararda harta gama komai har an Kai dining room da Ash ke cin abinci da yaransa matiqar Yana gari to tareda ‘yayansa yake cin abinci yanzu Kuma dasu mum Aisha suka dawo to dining din ya cika kenan.

Itace ta kamawa maamah sauran ruwa da abubuwan da baa gama jerawa ba takai ta jera mata ta fito daidai shigowan Naufal palon su Husnah gaisawa kawai sukai ta wucewarta.

Qarasa tattara komai a kitchen din sukai suka gyaresa kaman baayi aikin komaiba a ciki suka tafi daki.
Suna shiga wanka maamah tafara yi da ruwan zafin da Amatu ta hada mata dayake Abdul Yana dakin Yana guga Dan haka maamah na gamawa Suma zama sukai cin abincinsu da kowanne dare tare suke ci.

Suna farawa Basu Wani yi Nisa ba Haydar ya shigo dakin sanyeda kananun kaya fatar jikinsa na daukan ido sbd kusan kayan Shan iska ne three quarter da shirt mara nauyi qamshinsa na Dan tashi na tirarensa me tsada Dan kuwa kusan komai dayake amfani dashi odar mahaifinsa ne.

Idanuwansa akan Amatu Data dago itama tana kallansa cikin Jin sanyin ganinsa
Shima numfashi ya sauke Yana Jin sanyin zuciyarsa da ganinta kawai da yau kusan ya wuni baiyiba ya qaraso ya zaune gefenta Yana gaida maamah Dake tambayarsa yau ina yaje Bai zauna gida ba sosai.

Amsawa yayi da daukan spoon da Amatu ta aje Bataci abincin dashi ba ya Saka cikin plate dinta yafara ci Yana bawa maamah amsa da cewa tareda Mr Jameel suka fita Dad ya sakasu zuwa Wani guri.

Kan Abdul Dake tambayarsa yanda ta kaya da abubuwan yace masa zai masa bayani daga baya,
Kan Amatu da ita shi ta kalla ya Maida idanuwansa Yana murmushi yace

“Amah ki qara mana abincin Nan bazai ishemuba zanci da Dan yawa”

Abincin Amatu take kokarin Kara musu maamah tace

“Kaida zakuci abinci da Dad dinku Karka cika cikinka anan”

Abincin yaci gaba da ci Yana cewa

“maamah ko naje can naci idan banci tareda Amah ba bazan koshi ba Dan haka saina ci nata cikin yake cika”

Dariya maamah tayi Abdul kuwa harararsa yayi Amatu Kuma kallansa tayi tana cewa

“Zaka tashi daga Nan yanzu kuwa”

Wani Mayen murmushi ya Sakar mata Yana cewa

“Maamah Amah fa tawa ce da gaske nakeyi Babu Wanda zaa bawa”

Dariya kawai maamah ta sake yi sbd tasan kuruciya ce kawai ke damunsa Ina shi Ina Amatun datake yayarsa Kuma Amah ko yanzu ta samu Miji zaa iya mata aure shi kuwa yanzu yake ma a harkar karatu bare aure.

Ganin dariyar maamh yasa Haydar din sake kallan Amatu yace

“Ko bazaki aureni bane?

Rasa abin fada masa Amatu tayi ta juya tana Neman abin jifansa dashi da Bata samu ba ta juyo tace

“Tashi bazanci abincin dakaiba Kaci a gurin Abdul”

Abdulhameed Daya Fi kowa sanin yanda Amatu take a zuciyar Haydar da gasken gaske cewa yayi

“Karma yazo mun Nan bazanci tareda Shiba anjima kadan shiryawa zakuyi kece Zaki fara cemun munafuki Dan haka ku qarata can Yana zuwa Nan fasa masa hannu zanyi”

Hakan Daya fada yasa Amatu jifansa da mugun kallo itama tana cewa

“To koma gurin maamah Kaci Dan bazan ci da kaiba na fasa”

Maamah ma cewa tayi ta gama ita Kam Dan haka sedai ya dawo gurin Amah din tasa.

Marairaice fuska da idanuwa yayi Yana cewa

“Anty Amahn Haydar Talba”

Hakan Daya fada ya sata dariya Bata shirya ba Dan haka dole ta barsa sukaci abincin Yana sake bayyana musu yanda Amatu take a zuciyarsa da gaske Amma duk suna dariya kawai sbd sanin wasa yakeyi dakuma kaunar datake tsakaninsa da Amatun datafi ta kowa.

Harsuka gama kusan tayata cin abincin kawai yayi bawani abin kirki yaci ba suka fito ya rakata takai komai kitchen suka dawo ya rakata har kofan shigewa daki ta shige ya juya zuwa lokacin yasan kowa ya hallara a dining room, Kai tsaye can ya nufa Yana zuwa ya Tararda kowa a dakin shi kadaine Baya Nan Kuma Allah yasa Basu faraba zamansu kenan Dan haka cikin Nutsuwa ya qaraso Shima tareda kallan Naufal yace

“Yaya Naufal barka da fitowa,
Mum Aisha Ina wuni?ya gajiya?

Husnah kuwa kallanta kawai yayi tareda jefa mata kiss na kumata daga inda yake kafin ya zauna Kofar palon Dad dinsu ta Bude wadda take kawosa dining room din daga palonsa na farko Dan haka dukkaninsu kallan kofar suka juya sukai ahankali kafin qamshinsa ya huro musu cikin gurin Yana gauraya gun gaba Daya.

Sanye yake cikin Ash wandon Fendi fa farar rugby shirt sai black Lorenzo slippers marasa nauyi da tsadan gaske,

Idanuwa Naufal ya zubawa ASH TALBA Wanda ya kasance tamkar Wani madubi a idanuwansa da zuciyarsa,
ASH TALBA namiji ne Daya amsa sunan Maza ba muna Maza ba,
Namiji ne da kallo Daya zama masa kasan namiji ka kalla Tako wanne bangaren,
Babu Wanda ze kallesa yace shine ya haifi matashin saurayin Dake gabansa Haydar Talba,
Namiji ne da ko shi dayake amsa sunan matashi me lokacinsa zai rissina masa sbd ko karfinsu bazaa hada ba tinda daga karfin jiki harna zuci,harna Imani,harna komaiba ita dukiya da kwarjini tareda wata irin nutsuwa da aji bama zai hada kansa da the grt ASH TALBA ba da ake fada,
Tako Ina Ash namiji ne tsayayye da babu abinda yake masa shamaki.

Lafiyayyar fatarsa data ke daukan idanuwansu ya kalla ganin wato shi Hutu da jiqa cikin arziki da nutsuwa Wani abu ne na daban da idan Allah yayika cikinsu basa boyuwa,
Ya rasa Menene ya Saka akoda yaushe ASH TALBA da komai nasa daban ne,
Komai nasa unique ne,
Duk abubuwan tsadar rayuwar su Naufal yake Siya Amma haryanxu inda ASH yabi ya wuce ma yafi qarfin gwajinsa,
Duk shekarun Nan Babu abinda yake ran mahaifiyarsa bayan ya zama tamkar the grt ASH TALBA,shi kansa babban burinsa ne ya zama kamar Ash Talba Amma bayajin Hakan zai iya yiyuwa Dan kuwa izza da asalin kwarjini da haiban tareda kamewansa duk a jininsa suke hakama shi arziki irin wannan na Ash din Allah ne kawai zai baka irinsa ka samu zamowa.

Duk Izgilancinsa da nasa zafin Kai a gaban Ash Jin yake ya zube qasa warwas shiyasa Baya iya ko kallan cikin idanuwansa duk tsanani kuwa,
Ita kanta mum Aisha datake ‘yar uwarsa kwarjinsa durqusar da ita yake a gabansa Dan haka take gujewa tsayuwa a gabansa a duk lokacinda zata zartar da hukuncinta acan cikin gida Dan Bata iya kallansa a fuska ta aikata abinda take aikatawan.

Gaba dayansu dauke idanuwansu daga kansa sukai har ya iso a natse ya zauna tareda dagowa ya Kalli Naufal da shine ya fara gaidashi Yana masa barka da fitowa.

Fararen idanuwansa masu kwarjini ya saukar akan Naufal din da nutsuwa harma da kulawa yace

“Yaya gajiya?

Murya a natse Naufal ya amsa Yana sake gaidasa tareda sake jajanta masa jikin aunt Abeeda harma da mata adduar fatan samun lafiya.

Amsawa yayi a natse Yana kallan abincin da Husnah take serving nasa a taqaice yace

“Ya Isa”

Tambayan Naufal din yafara yi sama sama akan komai na karatunsa Daya kammalo Shima Yana basa amsa a natse cikin Kamala Dan dole idan zakayi magana da ASH din ka nutsu.

Abincin suka fara ci Babu me magana hakama kowa da kusan abinda yake ransa tsakanin mum Aisha da Naufal Wanda yakoma Wani irin kamilallen mutum,
Itama mum Aisha gaba Daya a jiqe take da zufa kada Naufal yayi abinda zai fara batasa a idanuwan ASH.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Leave a Reply

Back to top button