Amatulmaleek Hausa NovelHausa Novels

Amatulmaleek 55

Sponsored Links

YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

 

55
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI’IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

************
Zaman rashin Madafa sukai a asibitin har kusan 12 na dare kafin aka Husnah ta dawo daidai aka sallamesu suka dawo gida Babu me magana sbd yanda Husnah din take kaman wadda tayi gamo komai batace ba Idanuwanta sunyi jajir Bata iya cewa komai sai hawayen dake ciko idanuwanta tana hadiyewa hakama zuciyarta kaman zata qone take ji,
Zafi take ji,radadi take ji,qunci me girman gaske take ji hakama damuwa da ciwon zuciya takeji duk lokaci Daya.

Har suka iso gida maamah ce kawai take Dan tambayarta abinda ta sameta Amma Sam taqi magana Dan tana Bude Baki kuka zata iya fasawa me gigitarwa Dan haka ta zabi yin shiru Dan kada kanta ya juye.

Farha ce ta tuqo su a dawowa gida Dan haka tana parking Amatu ta fito jiki a mace ta budewa maamah kofa zata kamota Amma maamah din Husnah take kamowa Dan taimaka mata ta fito.

Tsayawa tayi jiki a mace tana kallo maamah din ta fito ta kama hannun Husnah kaman mara laka ta jata suka wuce gaba.

Numfashi me sanyi ta sauke kafin ta daga nata kafafun itada anty Farha sukayo ciki Suma.

Dayake hankalinsu khaltume Baya kwance da abinda ya farun basuyi bacci ba kowa na zaune Yana jiran tsammanin abinda yake faruwa na madame Abeeda har Husnah din,mum Aisha ce kawai a bedroom dinta hankalinta kwance tana baccinta Babu abinda ya dameta duk da taji abinda ya samu Husnah din a bakin khaltume.

Ganinsu ya Saka su khaltume Jin yar nutsuwa suna yiwa Husnah din sannu har suka Haye sama itada Maamah,

Shigowan Amatu da anty Farha ya Saka su dawo da kallansu kansu Suma suna musu barka da dawowa.
Kallan khaltume anty Farha tayi tace

“A hadowa Amatu abinda zata ci akawo daki tareda ruwan zafi ta Dan sha”

Gyada Kai khaltume tayi tana juyawa Dan ganin abinda zaa hada akaiwa Amatun wadda ta Haye batareda ta tsaya ba jiki a mace.

Maamah dakin Husnah suka shige tana sake kulawa da Husnah din wadda hawaye suka tsinke mata masu radadi suna sauka har gaban Rigarta batareda ta iya Bude bakinta har lokacin sbd bazata iya fadan abinda yake tafasa zuciyarta Yana tarwatsetaba.

Zaunawa maamah tayi tana rungumota kadan cikin kulawa da tausawa
Husnah dinma kwantawa tayi jikin maamah din tana sake fasa kuka me qarfin gaske mara sauti jikinta na Wani irin jijjiga.
Maamah sake rudewa tayi tana rarrashinta tareda dena tambayarta abinda ya faru fahimtar shine ke sake gigitata.

AmatulMaleek kuwa tana shiga dakinta toilet ta wuce Kai tsaye Tayo wanka da alwala ta fito.

Sallan ishai tafara yi kafin tana gamawa tayi Shirin bacci sai alokacin ta janyo wayarta ta kunna tana zaunawa bakin gado lokacin anty Farha na toilet.

Time tafara kalla kafin ta Nemo numbernsa ta tsaya tana kalla gabanta na faduwa jikinta na mutuwa da sanyi ta Saka kiransa a Karan farko na rayuwarta.

Acan bangarensa zaune yake gaban Abeeda a lokacin ana sake gasa mata qashin hannuwanta da qafafunta sbd su dan fara motsawa tinda dai ta Farka Kuma daidai gwargwado da sauki ta farfado Dan kuwa rashin motsawan ne kawai Se Cancer dinta da shima Yana Nan Amma dai saukin yafara shigowa na samun qwarin gwiwan kuzari Wanda ganin mijinta ne ya Sanyata Jin tanason yaqan ciwon ta samu kuzari da Dan qarfin komawa ga ahalinta.

Wayarsa Dake hannun Mr Jameel ce tafara vibrating na shigowan Kiran Amatu Wanda ya Saka Mr Jameel Dan hadiye yawun mamaki Dan kuwa duk da ASH be fadaba Bai Kuma nuna ba yasan yana cikin yanayi na rashin Jinta dannewa yayi sbd bawa madame Abeeda tata lokacin nasa.

Kasa barin Kiran ya yanke yayi Dan haka ya Dan qaraso jikin kofar dakin yayi knocking ahankali.

Dayake angama har an rufe gaba Daya jikin Abeeda din sai nurses da zasu fice suka Bude kofan dakin tareda ficewa shikuma ya Dan shigo a hankali ya sake kallan Madame Abeeda da idanuwanta ne Kawai suke kallansa da kulawa sosai ya sake mata ya jiki.

Matsowa kadan yayi gurin ASH din da girmamawa yace

“Kanada call”

Kallan wayar da aka miqo masa din yayi yaga kalmomin L.A a rubuce Wanda yake nufin little Abeedah.

Hannu ya miqa ahankali tareda karban wayar Yana miqewa a natse ya San dafa hannun Abeeda ahankali cikin kulawa yana kallan ciki idanuwanta da sauti me sanyi yace

“Zan amsa kira zan dawo” ya nufi kofa kafin ya Isa Mr Jameel yayi saurin Bude masa ya fice Shima ya fice tareda Jan kofar dakin.

Kiran tini ya Yanke Dan haka Kai tsaye txt ya tura mata akan zai kirata.

Dawowa yayi aka qarasa abinda zaayi na ranar ya wuce masaukinsa

Ko bayan Daya Isa wanka Shima ya sake yi ya zauna a natse ya sake Saka Kiran wayarta Amma tini ta kashe wayarta ta kwanta jiki ba qarfi.

Washe gari haka ya sake Saka Kiran Amma wayar a kashe hakama anty Farha Bata tareda ita tana spa ita Kuma tana school Dan haka kwata kwata Bai samu ji daga gareta ba.

Zuwa lokacin nutsuwarsa gaba Daya ta tashi daga kansa daurewa kawai yakeyi Amma kusan duk notin Kwanciyan hankalinsa sun kunce Mr Jameel ne kawai yasan Hakan Dan haka ya shirya tsaf umarni kawai yake jira ya Siya musu tickets din dawowa tinda madame Abeeda dai sedai ace alhmdlh ba laifi komai Normal ne.

***Husnah kwana biyu ta gama komawa kalan tausayi tausayi takaici takaici sbd ta gama ruda maamah ta daga mata hankali gaba Daya akan komai Daya danganci ASH da Amatu da Kuma mahaifiyarta sbd ta rasa ta inda zata fara ihu tana cewa Ashe ba ASH ne Dad dinta ba sbd tsoron abinda su mum Aisha zasu iya fadawa Dad din idan ya dawo dakuma firgita da abinda yayiwa Naufal akan lamarin fyaden Amatu tana tsoron itama abinda zai mata sbd laifinta babba ne.

Amatu data shiga damuwan ganin halinda Husnah ta jefa maamah na damuwa da kunci rokon maamah ta ringa yi akan ta cirewa kanta damuwa madame Abeeda na Nan lafiya kalau hakama Babu abinda zai faru inshallah.

Anty Farha dataga maamah na Neman Saka Amatun cikin tsaka me wuyar damuwa sai kawai ta tattara Amatun suke koma gidanta itama maamah din sai Bata Hana ba sbd ganin Amatun na sake rikita yanayin Husnah.

Komawanta gidan anty Farha itama shine natsuwan data samu gashi sun Dan samu break daga school Dan haka ta sake ta samu hankalinta ya kwanta.

Kwanansu biyu a gidan anty Farha ta Siya musu ticket suka wuce Lagos bayan anty Farha ta sanar da maamah din bikin auren qanwarta da suke uwa Daya Uba Daya zaayi,
Har cikin Rai maamah taji dadin tafiyan tasu Dan haka ta amince sbd a ranar suke tsammanin dawowan ASH gidan gwara Amatu ta tafi kawai har bayan kwana biyu.

Jirgin yamma suka bi Dan haka Koda suka Isa anyi magrib
Anty Farha ce a gaba sbd sanin zaa daukansu.

Amatun tana gefen anty Farha din sanye cikin doguwar Riga mara Fadi kusan daidai shape dinta me kyau kanta nade da mayafi mara nauyi,
handbag dinta me shegiyar tsada ce kawai a hannunta sai wayarta
Hasken fuskanta me kyau da fresh ne kawai yake daukan idon Wanda ya kalleta.

Mr Jameel ne yazo daukansu airport Wanda ya Sakata cikin matsanancin mamakin Daya Saka gabanta faduwa jikinta gaba Daya na daukan sanyi lokaci Daya tana tabbatarda ASH Yana Lagos din kenan Kuma yasan da zuwansu.

Kasa cewa komai tayi bayan sanyin da jikinta ya qara lokacinda ta Bude Baki a natse ta gaisa da Mr Jameel din ta shiga mota batareda ta iya qara cewa komaiba.

Anty Farha ce ta shigo motar itama kafin Mr Jameel yashiga yaja suka bar airport din zuwa masaukin ASH da zasu ajiye Amatun su wuce inda ze Kai Farha nata masaukin itama gidan sister dinta.

Suna isowa shine ya Bude mata motar ta fito a hankali cikin nutsuwa har lokacin Bata iya cewa komaiba Se anty Farha datake kalla wadda ko a jikinta Dan itama hutun takeso daga pressure din gidan ASH TALBA da Bata qarewa Dan haka hutawa zatai a Lagos din sai ta kwana biyu.

Mr Jameel ne yake janye da luggage dinta ita da anty Farha na bayansa anty Farha na mata maganar da kwata kwata Bata fahimta sbd tinaninta da bugun zuciyarta dayayi Nisa da sauyawa.

Wata lafiyayyar luxury lodge ce Sukazo wadda take kusa da ruwa dan haka takeda sanyi a yanayinta.

Security da tsarin gurin kawai ze tabbatarda su waye da waye suka Kai matsayin zama gurin.

Babu hayaniya Dan haka har suka Isa dakin Babu motsi ko wulgawan kowa.

Mr Jameel ne ya Ciro card din hannunsa ya Bude dakin tareda juyowa ya miqawa Amatun card din ya tura mata luggage dinta ahankali zuwa cikin dakin.

Anty Farha ce ta Dan shafa fuskanta ahankali cikin kulawa tace

“Take care little Amah,sai munyi yawa”

A handkali tana Jin jikinta na sake mutuwa hakama zuciyarta na sake sauya dokawa ahankali ta shiga dakin Wanda yake suite ne na Wanda ko acikin masu kudin su masu kudin ne.

Tana shigewa Mr Jameel ne ya janyo kofar ya rufe tareda juyawa ya Kalli farha suna magana cikin murmushi suka bar gurin zuwa mota Dan itama yakaita.

AmatulMaleek kuwa tsayawa tayi a gurin ta tana kasa motsawa tsawon mintina komai Bata ganewa ma sosai sbd sanyin da jikinta yaketa sake yi.

A hankali ta daga qafafunta tareda nufar luxury sofas din Dake tsare a wadatacciyar tsararriyan palon,

Ko taku uku bataiba taji motsi a hanyar lungun da lafiyayyar gadon dakin take daga boye baa ganinta sbd cikin glass tsarin dakin turawan Russia.

Dakatawa tayi batareda ta juyoba sedai bugun zuciyarta dayake qaruwa ahankali ahankali sbd Jin takunsa Yana nufota Kai tsaye hakama qamshinsa dayake shiga hancinta bayan tsawon kwanaki.

Ahankali ya iso bayanta idanuwansa Dake cikin radadi da kasalan buqatan ganinta suna kallan bayanta Yana isowa taji hannuwansa ahankali suna zagayota ya rungumeta ta bayanta Yana lumshe fararen idanuwansa ahankali tareda sauke ajiyan zuciya me sanyi a bayyane.
##MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070

Back to top button