Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 9

Sponsored Links

P9

Wani irin kallo Usman yake mata, amma ta basar ta ce “Mama kin san me yaya Usman ya yi?”

Mama ta ce “A a sai kin faɗa”

Usman ya ce”Haka muka yi da ke ruma?”

“Oho ni dai bana munafurci da rashin gaskiya, duk abin da aka yi mama bata nan sai na gaya mata, ba zan ga ana ba dai-dai ba mama bata sani ba na yi shiru”.

Kamar ya yi kuka ya ce”Amma haka muka yi da ke?”

Mama ta ce “Gaya mini ina jin ki”

Ruma ta kalli Usman ta ce “Sai dai ka yi haƙuri fa, amma wallahi sai na faɗa a gaban kowa da kowa, ba zan zuba ido ana abin da ba dai-dai ba”

Ba dan ya san idan ya yinƙura zai yi mata wani abu mama zata hana ba, da sai ya kife Ruma da mari, ya san idan ta ɗaga maganar nan akwai damuwa, zai sha faɗa da mita.
Uwa uba ga Yaya Umar a zaune a wurin, kuma ba shi da tabbacin iya abin da ruma ta gaya masa ta ji, shi kaɗai ɗin ta ji, dan kawai ɗaga kai ya yi ya ganta a tsaye lokacin da yake wayar.

Ta gyara zamanta sannan ta ce “Ɗazu, da ki ka aikeni kai tuwo gidan mai ƙuli, na ganshi a ƙofar gidan su wannan abokin nasa Yahaya, shi da abokansa sun dawo daga idi, ko gida ba su zo ba, ya zauna an fito da abinci sun haɗu suna ci, kuma kin hana hakan”

Ajiyar zuciya ya yi, yana hamdala da ba wancan zancen ta yi ba.

Mama ta ce “To wannan abun ne ki ke ta zuzutawa, ai shima ya zo ya ɗau abinci ya fita da shi sun ci tare”

“To mama sai aka ce ya je ya zauna a ƙofar gida yana cin abinci ai rashin kamun kai ne, kuma ke ki ka ce rashin kamun kai ne fa”.

Mama ta ce “To shikenan, za a yi masa faɗa”.

“To mama kiyi masa faɗan mana yanzu”

A fusace ya ce “Ke wai ni sa’an ki ne?”

Umar ya ce “Maganinku kenan da ku ke wasa da ita”

Can ta sake gyara zama ta kalli mama ta ce “Mama, kin san wani abu?”

“Ke na gaji da wannan shirmen naki fa” mama ta faɗa cikin ƙosawa.

“Mama ba shirme zan ba, ɗazu na ga Habiba a masallacin idi, da tsofaffin kaya na ganta”.

“To ina ruwanki? Kin ga ina rabaki da sabgar munafurci amma ba zaki dai na ba ko?”

Jiki a sanyaye ruma ta girgiza kai ta ce “Mama so nake a bata kaya ɗaya a cikin kayana” gaba ɗaya juyowa suka yi suna kallon ta jin abin da ta ce.

Huzaifa ya ce “Kina da hankali kuwa?”

“Amma dai ka san tun da nake ni ba mahaukaciya ba ce ko? Mama dan Allah a bata ita ma ta saka sabon kaya”

“Rufewa mutane baki, mara zuciya nan babarta ta zo ta ciwa mutane mutunci, amma ki ka cigaba da shishshige mata, ba za a bayar ba ɗin” Aliyu ya faɗa yana zaro ido.

Mama ta girgiza masa kai, ta dubi ruma ta ce “Allah ya kaimu gobe, sai ki zaɓi wanda zaki batan”

Murmushi ruma ta yi ta ce “Na gode mama, Allah ya saka da alkhairi, to zaki ɗan zuba mini naman kazar ita ma na kai mata ta ci, na san su basu yanka kaza ba”.

Yasir ya ce “Dama ta yaya zasu yanka, wannan babar ta su tana kiwon kaji kamar su kasheta, amma ba zata yanka su ci ba, bayan talauci har da son zuciya”

“Ka daina zagar mini babar ƙawa dan Allah”

Mama ta ce “Kin ga, tashi ki wuce ki je ki kwanta”
Ta miƙe ta shige ɗaki, mama ta mayar da idonta kan Aliyu ta ce “Aliyu, kar ku hora yarinyar nan a kan halin rowa, duk rashin jin ta tana da tausayi da son taimako, idan har abin da za ta yi bai saɓawa shari’a ba ku ƙyaleta”

Aliyu ya jinjina kai. Ruma kuwa ji take kamar ta janyo washegari, ta kai wa habiba wannan kayan, ita ma ta saka ta ji daɗi.

Washegari da wuri ruma ta yi wanka, ta yi kwalliyar salla da ɗaya daga cikin kayanta, ta zauna ta ɗaukarwa Habiba set ɗaya na atamfa har da ribbon da abin hannu.
Mama bata hanata ba, ta ƙulle mata nama ta bata ta kai wa Habiban.
Har zata ɗauka ta fita, ta tsaya ta ce “Mama, dan Allah idan ta yi kwalliyar zamu je gidan ‘yan ajinmu mu yi wasa”.

Mama ta ɗan ɓata fuska ta ce “Amma dai kin san babna son wannan abun ko, ba na son yawace-yawace”

Ta ɗan marairaice ta ce “Dan Allah mama, kin san bana yawo, daga aike sai makaranta, yanzu fa salla ce”.

“Shikenan, na ji, saura kuma ki je ki zauna sai an nemo ki, ina da ina zaku je?”

Ruma ta lissafa mata, mama ta yi ajiyar zuciya ta ce”Yanzu ƙarfe goma da rabi, kar ki wuce sha biyu, idan ki ka wuce abin da zai zo biyo baya ba zai yi miki daɗi ba”.

Cikin murna ta ce “Mama da wuri zan dawo in sha Allah ” ta yi waje ta na murmushi.

Kai tsaye gidansu Habiba ta nufa, ko da ta je ta yi ta sallama, shiru ba a amsa ba.
Tsayawa ta yi a tsakar gidan ta cigaba da sallama.
Sani ne ya leƙo yana amsawa, yana ganin ruma yayi saroro ya ce “Ke uban me ki ka zo yi mana a gida?”

Hararsa ta yi ta ce “To ina ruwanka ai ba wurinka na zo ba, ba yayana yayi maka tsakani da ni ba, babu ni babu ba, ko kuma na kira shi, ya zo ya ƙara kumbura maka fuska”

Tana tsaka da maganar, sai ga babar Habiba ta fito daga banɗaki, tana ganin ruma ta tsuke fuska ta ce”Ke me ki ka zo yi mini a gida?”

“Gurin Habiba na zo”

“Da izinin wa ki ka zo wurin Habiban?”

Habiba ce ta fito daga ɗaki, hannunta riƙe da kwanon tuwo da miyar kuka, tana ganin ruma ta ce “Laaa ruma, kin dai na zuwa makarantar allo ”

Ruma ta ce “Ba na ganki a masallacin idi ba ki ka ƙi kulani”

Habiba ta ce “Wallahi ruma ban ganki bane ba? Ya salla?”

“Lafiya lau, wurin ki na zo, zo ki ji?”

Mamaki ya cika babar su Habiba, ta riƙe haɓa ta ce “Habiba, wato cigaba da shiga sabgar yarinyar nan ki ka yi ko?”

Habiba ta girgiza kai ta ce “Wallahi Ummanmu ba kulata nake yi ba, na daɗe ma bamu haɗu ba”.

Ruma ta miƙowa Habiba leda ta ce “Kawo miki na yi, ki zo ki karɓa ki gani”
Babu musu ta ƙarasa ta karɓi ledar, taga ɗinkakkiyar atamfa ga abin hannu da ribbon, sai kuma ƙullin nama.

Habiba ta ce “Ruma wannan na waye?”

“Naki ne, in gaya miki, kayan salla na  kala goma sha biyu da hijjabai, har da abin hannu da sarƙa, shine na ce bari na kawo miki ɗaya, ki saka mu je yawon salla”.

Babar su Habiba ta ce “Ba ta so ba zata karɓa ba, bana son shishshigi, ba ta kayanta ce muku aka yi tana buƙata? Ita ma tana da kayan salla”

Idon Habiba ya cika da hawaye ta ce “Wallahi Umma bani da kayan salla, ina son kayan dan Allah ki bar ni na saka”.

Ruma ta ce “Dan Allah Umma ki bari ta saka, mun shirya ai mun dai na faɗa, dan Allah ki bari ta saka”

Umma ta kalli yadda Habiba ta rungume kaya tana kuka, wai tana so, haka ta ƙyaleta. Habiba ta shiga ɗaki ta saka kayan, aikuwa tamkar dan ita aka ɗinka su suka yi mata kyau.
Sani ya din ga ce wa habiba mara zuciya.

Abin ka da ƙuruciya, tuni habiba ta shirya a cikin kayan, duk da babar Habiba na jin haushin ruma, hakan bai hanata rawar jiki wurin raba naman kazar da ruma ta kawo ba, fan kuwa an daɗe ba a haɗu ba.
Daga haka suka fita nasu yawo.

Tamkar awakai haka suka dinga yawo, kusfa kusfa gidajen ƙawayensu, wasu a haɗu a rabu da su ƙalau, wasu kuma a ƙare da faɗa. Ruma ba ta tashi tuna kashedin mama ba, sai bayan azahar tana ta gararanbarta a gari.

A suwkane ta nufo gida, tana ta tunanin yadda za ta kare kanta a wurin mama, dan ta san zuwa yanzu ana can ana nemanta kamar kuɗin guziri.

Yaya Usman ta hango a tsaye a jikin wata mota, ya sha kwalliya, shi da abokansa, da alama fita za su yi.
Da gudu ta ƙarasa in da yake tsaye ta ce “Yaya ussy, me ka ke yi a nan?”

“Ban sani ba, wuce ki tafi gida, ki kai aiken da aka yi miki” abin da ya faɗa ne ya sanya ta fuskanci kamar mama ba ta neme ta ba, dan haka ta ce “Dan Allah ina zaka?”.

“Zamu ɗan fita chilling ne”

“Meye chilling kuma?”

Ya haɗe rai ya ce “Cewa na yi fa ki tafi gida ko?”

“Dan Allah ka yi haƙuri, zan bika dan Allah”

“Ke wai ni sa’an wasanki ne? Ba zaki wuce ki tafi gida ba?”

Ta sake marairaice wa ta ce “Dan Allah Yaya”

Riƙe rigarsa tayi tana kallonsa kamar za ta yi kuka. Tunawa ya yi da haushin ƙin tafiya da ita zai iya sanyawa ta tona masa asiri.

Yayi ƙasa da murya ya ce “To ki je ki tambayo mama, idan ta yarda sai mu tafi”

“Wallahi na san idan na tafi, tafiya zaka yi”

“Shegiya sai ka ce mayya, idan na tafi da ke a ina zan saka ki motar ba space” yayi maganar a ƙule.

“Sai na zauna a cinyarka” duk yadda ya so ya yakice ruma, taƙi ta nace, gashi ya san zai sha kunya, idan har ruma ta tona masa asirin yana waya da budurwa, dan ya san sai dai ya kasheta bayan ta faɗa zare idonsa ba zai hanata faɗar abin da ta yi niyya ba.

Haka ya sakata a motar, dama ta abokinsu ce, ita kaɗai a cikin maza, sai zaginta yake, amma ko a jikinta, ya sakata a gefensa.

Abokansa sai dariya suke masa, suna “Ka ga Ƙanwar maza, suke mulkin amma dole a biki ko ba a so” ba wanda ta kula a cikinsu suka tafi.

Wurin shaƙatawa suka je, duk abin da suka ci sai da suka sayawa ruma ita ma ta ci, da ta ji ta ƙoshi ta kalli Usman ta ce “Yaya ussy, a samo leda a ɗaure mini sauran na tafi da shi gida”

“Saboda kowa ma bashi da hankali kamar ke? Wallahi baki isa ba” ba dan ya ji daɗin fitar ba, ya azalzali abokansa suka koma gida, saboda yadda ruman ke ta zubar masa da mutunci a idon abokansa.

Ko da suka je gida, mama a kiɗime take, tun sha biyu ake nemanta ba a ganta ba.

Bin su da kallo mama ta yi, ta dubi Usman ta ce “A ina ka ganota?”

“Nima a hanya na ganta bayan la’asar, zamu fita da abokaina, ta nace sai ta bini, na kira Aliyu a waya na gaya masa muka tafi da ita”.

“Ku ka je ina?”

“Wurin wani cin abinci ne, ni da su Isma’il ne”

“Kuma ita kaɗai a cikin maza Usman, ka san tun yaushe yarinyar nan ba ta gidan nan, ka ga tashin hankalin da na shiga kuwa? Wallahi yau sai kin ci ubanki”
Abdallah ya ce “Wallahi mama ko ba ki daketa ba, sai na zaneta yau, ki yi mata bugun shekararriyar dawa, yarinyar nan ta ci a bata gado a Asibitin mahaukata”.
Mama a tsananin fusace ta janyo ruma, ta din ga turjewa tana ihu, mama ta zaro bulugari ta dinga bugunta da shi tana kurma ihu tana neman taimako.

Mama ba ta saba tarbiyya da duka ba, amma idan ta kai bango jikin mutum yana gaya masa, sai da Usman ya ƙwaci ruma da ƙyar a hannun mama.

Tun daga ranar, mama ta ce ba zata bata sauran kayan sallar baz gashi an aiko mata da kayan salla daga can garin su, ga dangin mahaifin su ma, sun ɗinko mata kaya, sun aiko mata da su, duk mama ta ce ba zata sake sakawa ba ta gama kwalliyar salla.
Washegari ta na ji ta na gani mama ta shirya, ta tafi cikin gari, ta bar ruma a gida.

Gidan duk ya yi mata babu daɗi, sai faɗace-faɗace take da su Yasir.
Suka gama suka fice suka bar ta a gidan. Ta ji babu daɗi rashin tafiya da ita da mama ba ta yi ba, gaji da zama ta tashi tana neman abun yi.
Ɗakin ‘yan mazan ta shiga, ta fara gyara musu ta ci karo da shaddar yaya Umar ya saƙaleta.
Wani tunani ta yi, ta kwaso shaddar ta fito da ita tsakar gida. Ta zuba ruwa a bokiti ta tuttula omo ta zunduma shaddar nan a ciki, ta koma ta cigaba aikin gyaran ɗakin.
A ƙalla shaddar nan ta kai awa biyu a ruwa, ruma ta fito ta jagwalgwala ta shanya. Ai kuwa shaddar nan gaba ɗaya ta daina wannan shining ɗin da take yi saboda azabar omo.

Aka jima, ya haɗa wuta a dutsen guga, ta hau goge masa ita.

Abdallah ne ya dawo, ya tarar da ruma ta duƙufa tana guga.
Ya tsaya yana ƙoƙarin gane me take gogewa.

“Wai meye wannan ki ke gogewa haka?”

Ta ɗago ta kalleshi ta ce “Kayan yaya Umar ne, na ga ya saƙale su a ɗaki, na san wankewa zai yi, shi ne na wanke masa nake goge masa”.

Abdallah ya ce “Innalillahi wa Innalillahi raji’un, ruma da me ki ka wanke shaddar nan haka?”

“To za ayi wanki ba da ruwa da omo bane?”

“Uban waye ya ce miki ana wanke shadda da omo?” Ai suna cikin maganar ruma ta ƙone gaban rigar.

Dafe kai ta yi ta ce “Innalillahi, na shiga uku, Abdallah ya zan yi na ƙona masa shadda?”

Abdallah ya ce “Maganinki shegen karambani, kya san mai zaki gaya masa”

Hannu ruma ta ɗora a ka ta dinga kuka, dan ta san yau kashinta ya bushe, sai yadda Allah ya yi da ita.

Haka mama ta dawo ta tarar da ita, tana ta uban kuka, Abdallah ya gaya mata abin da ta aikata.

Cikin kuka ruma ta ce “Dan Allah mama ki bashi haƙuri, yau na san na mutu wallahi, dan Allah mama kar ki bari ya dakeni ko ya saka ni punishing”.

“Ba ruwana, ai nima ba jin maganata ki ke yi ba”.

Abu kamar wasa, har bayan la’asar ruma ba ta ci ko Abincin rana ba, sai kuka take yi.

Huzaifa ya ce “Ni ne mutum na farko da zai sanar da mai sunan Baba wannan taɓargaza da ki ka aikata masa”

Duk da mama a ƙule take da ita a kan laifin da ta yi mata jiya, amma hakan bai hanata saka ruma ta ci abinci ba, amma ruma taƙi ci sai aikin kuka. Ita kanta mama na tausayawa ruma hukuncin da zata fuskanta a wurin Umar idan ya dawo ya tarar da ɓarna da ta aikata masa, sai dai ita ta janyo kanta, rashin jin ta ya yi yawa.

Mai sunan Baba bai dawo ba sai bayan sallar magariba, tun da ya shigo ta sake takurewa tana uban kuka.
Ya dube ta, cikin kakkausar muryarsa ya ce “Kukan me ki ke yi?”

Huzaifa ya gyara zama, ya wassafa masa ɓarnar da ta aikata.
Duk da babu isasshen haske a tsakar gidan, ta tsorata da kallon da ya yi mata.

“Dan Allah yaya ka yi haƙuri, ba a son raina na aikata hakan ba, wallahi kawai niyyata na baka mamaki, na wanke maka na goge maka ban san haka abin zai zama ba”

Kalmar ta bashi mamaki sai da ta saka Aliyu dariya, ya ce “Lallai kin bashi mamaki kam”

Yadda ta firgice ne, ya sanya Yasir ya ce “Dan Allah yaya ka yi haƙuri, kuskure ne, tun da tsautsayin nan ya faru ba ta ci Abinci ba”

“Zaka ɗau hukuncin da zan yi mata kenan?” Yayi maganar ba tare da ya kalli Yasir ba.

Yasir ya ce “Eh ni ka hukunta ni a madadinta, a tsorace take”

A ɗan tsawace ya ce “Tashi ki ɗauko mini kayan na gani”

Sumi-sumi ta tashi ta je ta ɗauko kayan, ta miƙa masa.
Ya karɓa ya duba, gaba ɗaya kayan sun tashi daga aiki, jikinta sai rawa yake yi.

“Tun da ki ke na taɓa saka ki wanki?” Ta girgiza kai.

“To Meyasa ki ka wanke nawa kayan?”

“So nake nima na yi abin arziki, ban zaci zai zama na tsiya ba”

Ya girgiza kai ya ce “Zubo mini Abinci” ta tashi tana ta tsuma, ta je ta zubo abinci ta kawo masa tana kallonsa.

Ya karɓi Abincin, ya ajiye a gabanta ya ce “Ci Abinci”

Fuska duk hawaye ta ce “Dan Allah ba zaka saka ni kama kunne ba?”

Ya girgiza mata kai ya ce “Ba zan saka ki ba” yayi maganar yana ɗebo Abincin ya kai bakinta.

“To ka haƙura?” Ya jinjina mata kai alamar eh.

“To dan Allah ka yi haƙuri, tsautsayi ne”

“To, ci abinci” sai a lokacin ta ji ranta ya yi sanyi, har ta fara cin abinci, babu wanda bai yi mamakin yadda mai sunan Baba ya ƙyale ruma ba, basu taɓa kawo zai rabu da ita ba.

Sai da ta ci ta ƙoshi sannan ta ce “Me sunan Baba”

“Na’am”

‘Dan Allah ka yi haƙuri, zan karɓi kuɗina na wurin mama sai na saya maka wata “murmushin gefen baki ya yi ya ce ‘To Shikenan”.

Bayan yaya Umar ya fita, Huzaifa ya lallaɓa ya bi ruma ɗaki yana cewa “Ruma, wace addu’a ki ka yiwa mai sunan Baba ya ƙyale ki ne? Zo ki gaya mini”

Usman ya ce “Wallahi nima na yi mamaki duk ɓarnar nan da ta yi masa ya ƙyaleta”

Babu wanda ta kula a cikinsu ta kwanta tana yiwa Allah godiya.

Hidindimun Salla suka wuce, aka koma makaranta, ruma ta koma makaranta, sai dai fafur ta ƙi zaman ajinsu, wai malaminsu baya son ta, wani malam Habibu ɗan mai makarantar ta liƙewa, duk ajin da za shi ya yi ƙari sai ta bishi, gashi ta maƙalewa Auwal, yaya sama yaya ƙasa haka take kiransa saboda yana sayen tsami gaye da goriba ya bata.

Yanzu ma ‘yan ajin su Yasir suna jiran malam Habibu ya zo yayi musu ƙarin Alqur’ani, sai ga shi ya shigo shi da ruma.
Yasir yana ganinta ya tsuke fuska, dan tun wancan hansfreen da ta yi masa a gida, ya hanata zuwa ajinsu, amma sai gata.
Malam Habibu ya zauna, ya ce ta shiga cikin mata ta zauna. Aikuwa ta shiga ta zauna, ta nutsu kamar gaske aka yi ƙarin nan aka idar.
Aka zo kowa yana biyawa, aka zo kan Yasir shi ma ya biya, sai cewa ta yi ‘Inyee ashe ka na ja, hmm da ba ka iya ba wallahi da sai na faɗa a gida, in ce kai ma baka iya karatu ba”

Dariya ‘yan ajin suka hau yi suna kallon Yasir, ya sunkuyar da kai yayi mata shiru.

Kowa ya gama biyawa, ruma ta ce “Malam nima zan karanta”

Ya ce “To bisimillah”

Abun mamaki sai ga ruma ta karanta shafi guda, duk da tana yi ana cin gyaranta, amma ta kai shafi guda, ba ƙaramin mamaki ta bawa Yasir ba, yarinyar da ta ce ita gejinta aya biyu kawai.

Ɗari biyar malam Habibu ya bata, tare da jinjina mata, dan babu wanda bai san ruma ba ta ja ba.
Da ya kammala ƙarin ya ce ta ta so su tafi, amma ta kalli yadda Yasir ya haɗe rai ta ce “Malam ni ka bar ni a nan ajin”

Malam Habibu ya ce “To shikenan, duk malamin da ya zo ace masa ruma ajiyata ce, sanna ba ruwan kowa da ita kar a takura mata”

Suka ce to.

Yasir kuwa kamar ya zo ya rufeta da duka, dan ba zata taɓa zama shiru ba.

Ruma ta shige cikin ‘yan mata, suna hirarsu, ita kuma tana shan farar ƙasarta, amma duk tana jin me suke faɗa.

Yau har aka tashi tana ajin su Yasir, sai da aka tashi ta bar ajin.

Ta je ta samu tsohuwar da take sayar da kayan yara a a ƙofar makarantar, ya titsiyeta wai sai ta bata farar ƙasa kyauta.
Duk shegen son kuɗi irin na iya, sai da ta bawa ruma farar ƙasarar nan, saboda shegen surutun ta da nacin tsiya.

Ta karɓi farar ƙasarta ta yi gida, haryanzu makarantar nan ba ta da ƙawaye, a cewarta ɗaliban ba su yi mata ba, kuma ba komai bane su ɗaliban sa’aninta kowanne ya mayar da hankali a kan karatunsa ne, ita kuwa ruma ‘yar abi yarima a sha kiɗa ce.

Tun da ta je gida take tafa hannu tana masifa, “Wallahi an mini laifi a gidan nan, kuma sai kowa ya hallara zan faɗi me aka yi mini” jin kowa ya shareta ya ƙi kulata ya sanya ta ce “Mama yanzu dan Allah abin da ake yi mini a gidan nan ya dace?”

“Da aka yi miki me?”

“Mama a gabanki ‘ya’yanki suke ce mini ƙwaila, amma baki taɓa hana su ba”

Mama ta dubeta ta yi murmushi cikin manyance ta ce “To ba ƙwailar bace ba?”

Ruma ta buɗe baki ta ce “Au mama har da ke?”

Aliyu ya ce “To meye dan an ce miki ƙwaila, ai ƙwailar ce”

Ruma ta ce “Kutt, ƙwaila fa wadda ba ta da nono kenan?”

Aliyu ya ce “Innalillahi wannan gingimemiyar maganar fa”

Mama ta ce “ke waye ya gaya miki haka?”

“‘yan ajin su Yasir ne suke faɗa, matan nan ina jin su da kunnen nan nawa, sun zaci bana jin su”

Mama ta ce “To ke nonon ne da ke da ba za ace miki ƙwaila ba?”

“Mama gori dai ake yi mini kenan? Sai in je wurin Mai furar nan na bakin hanya, na sayo nonon, na zo na ƙulla a leda na dinga sakawa” cike da takaici mama take bin ruma da kallo, ta ma rasa me zata ce mata. Usman yana tsakar gida, sai ƙyaƙyata dariya yake ƙasa-ƙasa lamarin ƙanwar nan ta su sai Addu’a kawai.

Aliyu ya ce”Ke da ki ke ƙanwar maza, me zaki yi da wannan abun? Ki yi zamanki a haka ai sai kin fi kyau”

Ta ce “Kuma fa haka ne” ta cire rigar islamiyyar, daga ita sai vest, ta sinsina rigar ta kuma cewa “Mama, dan Allah yaushe zan fara warin hammata, ina son idan na cire riga na sansana na ji tana ɗan warin nan da ƙamashin turare ”

“Fitar mini daga ɗaki dan ubanki, shashasha mara alƙibla fita ki bar mini ɗaki”.

 

 

AYSHERCOOL
08081012143
[08/07, 4:58 pm] JAKADIYAR AREWA:                   ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER’S ASSOCIATES

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Ku yi subscribing  YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.

*A TAIMAKA AYI SUBSCRIBING YOUTUBE CHANNEL ƊINA NA COOL HAUSA NOVELS, KO IN KOMA POSTING SAU ƊAYA A SATI 😒*

Back to top button