Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 14

Sponsored Links

14

Buɗe baki Abdallah ya yi ya na kallon ruma, bil haƙƙi take maganar har cikin zuciyarta.

“Ke fa hankali bai wadaci ƙaramar ƙwaƙwalwarki ba, sai ki je allo ki zana babar wasu, idan aka zana taki zaki ji daɗi?”

“Ai ni na yi alƙawarin na daina dambe, ta zageni na kasa ramawa, saboda ashar take yi, ni kuma bana zagi, gaba ɗaya ta cuceni ta ɓata mini rai, ni kuwa ba ta san ba a taɓani a ci bulus ba, wallahi sai ta gane kurenta”

Abdallah ya girgiza kai ya ce “No, ki nemi wata hanyar dai, amma ban da iyaye, ba abin wasa bane”

“Iyaye ba abin wasa bane, ta ce mini mara tarbiyya babata tsohuwa, sai na ci buhun ubanta, ranar ma a sanyi ta sameni, da sai na tayar mata da aljanu na yi mata dukan tsiya, to bana som daga shigata makarantar a tsaneni ne, ayi mini mummunar shaida”. Duk yadda Abdallah ya so nusar da ruma, ta yi biris ta ƙi fahimta ta yi alwashin ramuwar gayya a kan abin da aka yi mata.

*****
Nasihar da takawa yake yi mata, a hankali ta ji ta ratsata sosai da sosai, daga ita har shi suna fuskantar jarrabawa daban-daban, wanda hakan yake jefa Ammi cikin damuwa.

Nusaiba ta kalli Takawa da Iman ta ce “Iman ‘yar gidan yaya, Ammi ta ki yayan ma naki”
Murmushi iman ta yi tana sake gyara zamanta.

Turo ƙofar falon aka yi, suka ɗaga kai gaba ɗayansu suka kalli ƙofar. Jabir ne ya shigo, da sallama a bakinsa. Suka amsa masa gaba ɗaya, hankalinsa ya na kan Iman ya na ƙare mata kallo. Hakan ya sanya ta haɗe rai tana ɗan kawar da kai gefe.

Yayi murmushi ya kalli Adam ya ce “Ni zaka yiwa haka, ka dawo amma sai dai na ji a gari ko ka neme ni”

Takawa yayi murmushin gefen baki ya ce “Ai idan ka san na dawo, zaka dameni ne ka sani yawo a gari, shi ya sa na yi shiru so nake sai na huta, shi ya sanya ma ban zauna a gidana ba, na yo nan”

Nusaiba ta ce “Uncle J, ina wuni?”

“Lafiya lau Nussy, Iman ba magana ne? ‘yar rigima”

Ba dan ta so ba ta ce gaishe shi, gaba ɗaya kwanan nan ba ta son abubuwan da Jabir yake mata, wanda ta kasa gane kan su.

Suna tsaka da hirar sai ga sallamar su Fauziyya da Ruƙayya, tare da Samha suka shigo falon.
Gaban Iman ya faɗi da ta ga Samha, musamman wani irin kallo da take bin ta da shi, da Iman ɗin ta kasa gane wane irin kallo ne.
Jabir suka fara gaisarwa, sannan cikin girmamawa suka gaida Takawa. Cikin halinsa na ko in kula da kuma tsare gida ya amsa musu.

Fauziyya ce ta gyara zama ta ce “Yaya ashe ka dawo, bamu san ka dawo ba, sai ɗazu Mummy ta ce mana, ai ka dawo”

“Eh na dawo” ya faɗa a taƙaice.

“Masha Allah, ya ibada?”

Ya amsa da “Alhamdilillah”

“To Allah ya sa an yi karɓaɓiyya”.

Samha ta gyara zama, ta na yiwa Adam wani irin shu’umin kallo, ta ɗan murmusa sannan ta ce “Takawa, ni fa kwance jaka na zo yi, daga zuwa wurin su Fauziyy, na ji suna cewa za su shigo yi maka sannu da zuwa, na ce bari na biyo su in yi sannu da zuwa, kuma a bani tawa tsarabar”
A hankali ya ɗago idonsa, ya kalli Samha, ya ɗan yi murmushi tare da girgiza kai amma bai ce komai ba.

Jabir ya dubi Iman ya ce “Iman, duk kin maƙalƙale mana shi, kamar ke kaɗai ki ka yi kewarsa, ki barmu mu ma mu gana da shi sosai mana” yayi maganar da sigar wasa.

Noƙe kafaɗa ta yi kamar ƙaramar yarinya, sai dai suna haɗa ido da Samha, samhan ta sake yi mata wani mugun kallo, da ya tilasta mata sunkuyar da kai.

“Jama’a ya shirin bikin Jamilu Turaki, Takawa akwai kilisa fa ranar Juma’a”

Adam ya girgiza kai ya ce”Kai, ƙyaleni da wata kilisa, duk na gaji, ni ban so ku ka san na dawo ba ma, ina buƙatar hutu sosai ”

“Amma ba dai ka na nufin, ba zaka yi hawan ba, Jamil ɗin guda?”

“Sai na yi tunani tukuna, idan ina da time”

Jabir ya ce”Ba ruwana, kai da shi”

Tsarguwa da rashin sukunin da idanun Samha suka sanya Iman ne ya sanya ta miƙe ta ce “Ni dai sai an jimanku, zan je na huta”

Samha ma ta miƙe ta ce “Mu je, ina son na gaida Ammi kan na tafi ” jikin Iman ya yi sanyi, dan ta san akwai wani abu a ran Samha data ce za ta bita ta gaida Ammi.

Suna shiga ƙofar da zata sada su da sashin Ammi, Samha ta riƙo hannun Iman, ta tsayar da ita suna fuskanta juna.

Cikin raunaniyyar muryarta kamar mai shirin yin kuka Iman ta ce “Me na yi miki?”

Samha ta ƙarewa Iman kallo, sannan ta ce “Wai wace irin yarinya ce ke, kin manta kashedin da na yi miki ko sai na sake nanata miki?”

Iman ta ɗan ɓata fuska, ta aro jarumta ta ɓoye tsoron ta ta ce “Anty Samha, ni babu komai a tsakanina da takawa, ki yarda da ni mana, ina jin sa kamar wanda muka fito daga ciki ɗaya, ni ba zan iya aurensa ba”

Samha ta ce “Ƙarya ki ke yi, ba wani ki na jin sa kamar wanda ku ka kwanta ciki ɗaya, ai ba ki da kimar da zaki kwanta mahaifa ɗaya da Adam, ko kin manta wacece ke?”

Iman ta girgiza kai ta ce “Ban manta ba, ‘yar karere ce ni, wadda ba ta da gado a gidan Galadima, wadda aka taimakawa aka riƙe, ina sane ba sai kin tuna mini ba”.

Samha ta yi wani murmushi sannan ya kuma duban Iman ta ce “Ƙwarai kuwa kina sane, ban da Ammi ta nace da a cikin barorin gidan nan ya dace ki tashi ba ‘yan gida ba, dan haka ki kiyayi shiga gonata”

“Amma ta yaya, a tare muka tashi da takawa, ta yaya za ki ce sai na nesanta da shi?”

Ta ɗage kafaɗa ta ce “Wannan matsalar ki ce, ba tawa ba, dan na ga alamar tun da ba ki samu wancan ba, wannan zaki hara ki shiga hankalinki”.

Iman ta girgiza kai ta ce “Ni babu abin da ki ke tunani tsakanina da takawa, amma ke ma Anty Samha bana tunanin zaki samu abin da ki ke so, akwai katangar ƙarfe a gabanki, kuma kin san takawa kin san halin sa sarai, ki bi a sannu” daga haka tayi gaba ta bar Samha a tsaye.

*****
Kamar yadda ruma ta yi alwashi, haka ta yi, ta je ajinsu ta zana wata shirgegiyar mata a kan allo, ta yi labelling ɗin ta. Gefe kuma ta zana ƙarama wadda ba ta kai matar ba, ta yi labelling ta rubuta Asiya shu’aibu.
‘yan ajin suka dinga tuntsira dariya, saboda yadda zanen ya yi.
Ita kuwa Asiya ba ta san me aka yi ba, sai dai tana shigowa ta ga ‘yan aji suna kallonta suna dariya.
Saroro ta yi, tana son gane me suke yiwa dariya, ba ta kula ba ta je ta zauna, sai dai ta na zaman idonta ya sauka a kan allon, ta ga ta’asar da ruma ta yi.
A firgice ta tashi tsaye, tana zazzare ido “Uban waye ya yi mini wannan rashin mutuncin”

Ruma ta miƙe ta ce “I am madam”

“Saboda tsabar kin raina wa kan ki hankali, kina nufin wannan babata ki ka zana?”

“An zanata ɗin, ni ba cewa ki ka yi babata tsohuwa ce ba, ashe ma babata ta fi taki kyau”

Kan ruma ta farga, Asiya ta diro gaban ruma ta shaƙe ruma da hijjabinta. Kan ruma ta farga Asiya ta rufeta da duka, ta kaita ƙasa saboda ta rufe mata fuska da hijjabi. Kan ruma tayi wani yinƙuri, Asiya tayi mata duka.
Da ƙyar aka kirawo wani malami, ya janye Asiya daga kan ruma.

Malamin ya tasa su a gaba zuwa ofishin malamai, dan hukunta su, ruma ta shafa bakinta ta ji jini, tun da take a rayuwarta ko da za ta yi dambe a fitar mata da jini, to tabbas a duba wanda suka yi damben ta lallasa shi shi ma.
Gaba ɗaya Wani irin baƙin ciki ya mamaye ruma, gaba ɗaya ta rasa abin da yake mata daɗi, tun da take ba a taɓa galaba a kanta ba sai yau.

Ko da aka je staff room ana mayar da yadda aka yi, ruma taƙi magana, sai idonta da ya yi jawur, aka yo caaa a kan ruma, malamai suka din ga yi mata faɗa a kan bata kyauta ba zana babar Asiya da ta yi, suna kiranta mara ɗa’a.
Haryanzu malaman basu san wacece ruma ba, dan tun da Allah ya sanya ta zo makarantar ba ta taɓa gwada musu halinta ba.
Aka ce sai ruma ta bawa Asiya haƙuri, sannan za ta yi wankin banɗaki na sati guda, ita kuma Asiya zata yi sharar aji na kwana uku, saboda ɗaukar mataki da ta yi suka yi dambe da ruma.
Juyin duniya ruma ta yi magana taƙi, ƙememe taƙi bayar da haƙuri, dan haka aka sakata Kneel down har aka tashi a rana.
Babu abin da take tunani sai abin da za ta yiwa Asiya ta huce daga wannan baƙin cikin.

Ko da aka kaɗa ƙararrawa, ruma ba ta jira malaman su sallameta ba, ta tashi ta tafi aji ta ɗauko jakarta, Asiya ta din ga yi mata dariya har da gwalo. Wata nutsuwa ce ta shigi ruma a lokacin, dan a lokacin ji take da da wani abin dukan a kusa da ita, to tabbas sai ta illata Asiya.
Ta ɗau jakarta ta fice, har ta je gida kamar zararriya jikinta a sanyaye.

Tun da mama ta ga ruma ta shigo babu ko sallama, ga uniform ɗin ruma a duƙunƙune ga busashshen jini a gefen bakin ta, ta san yau ta yi halin na dambe, ga takalminta da jakarta a hannu ta shigo da su, gwiwar wandonta ta yi kaca-kaca da ƙasa.
Ta zubar da su a tsakar gida ta shige ɗakin mama kawai ta nemi wuri ta kwanta.
Ba ta tashi ba sai bayan azahar, ta tashi ta yi wanka, ta yi alwala ta yi sallar azahar, ta kuma neman wuri ta zauna a tsakar gida.

“Mutuniyar, wai ya aka yi ne? Zo ki sayo mana kifi mu ci Abinci, tun da na dawo nake cigiyarki” yayi maganar yana leƙa fuskarta.
Maimakon ta amsa masa kawai ya ga hawaye a fuskarta.

“Ke, menene mama ce?”

“Yaya Usy”

“Na’am rumaisa”

“Ni za a daka a hana kuka? Zuciyata zata fashe” tayi maganar tana sake fashewa da kuka.

Rarrashinta ya shiga yi, yadda ya ga tana neman ta shiɗe, idanunta duk suka yi ja.
Ya din ga lallaɓata ta gaya masa abin da ya faru.

Mama da take jin su ta ce “Allah ya ƙara miki, Allah ya sa yau da ki ka samu wadda ta zane ki, ba zaki sake dambe ba, dama ban da iskanci meye na zana uwar wani, idan ke aka zana taki uwar zaki ji daɗi?”

“Mama cewa fa ta yi babata tsohuwa”

“To sai me? Tsufa ai arziki ne, ruma ita duniya ‘yar siyasa ce, ba komai ƙarfi yake baka ba, amma kin kasa gane hakan”

Wani irin kallo take yi wa mama, wato ita mama ko a jikinta kenan.

Usman ya kawar da fuskar ruma daga kallon mama. Abu ne mawuyaci ruma ta yi fushi, ko an ɓata mata rai sai dai ta yi kuka, idan ta gama kuma shikenan ya wuce sai a shirya, amma yadda idanunta suka yi yau ya tabattar masa da ta kai maƙura a ɓacin rai, ba a taɓa defeating ɗin ta ba sai yau. Irin zuciyar mai sunan baba ce da ita, idan rai ya ɓaci silently suke fushi, sai dai suna shiga mawuyacin hali, har gara shi Umar yana shouting wasu lokutan, amma ruma gaba ɗaya kasa komai take idan tana cikin matsanancin ɓacin rai. Wata irin ajiyar zuciya kawai take yi.

“Yaya ni raguwa ce ko? Aka zageni, a kan gaskiyata kuma aka hukunta ni, ni ko?”

Usman ya yi ƙasa da muryarsa ya ce “Ke ba raguwa ba ce, kowa shaida ne, kamar yadda nake gaya miki, ki fuskanci duk wani abin da yake baki tsoro, gaba da gaba na tsaya miki”

Ta ɗaga kai ta kalli Usman, ya jinjina mata kai alamar ƙwarin gwiwa, ta jinjina kai ta mayar da kai ta kwanta a jikinsa, tana cigaba da ajiyar zuciya.

Duk wanda ya shigo ya ga ruma a haka, sai ya tambayi ba’asin meyafaru, ko ba ta da lafiya ne?
Mama ta ce “Ina fa, lafiyarta ƙalau, yau bori ne ya kar boka, ta tsokano wadda ta fi ƙarfinta, aka naɗa mata duka, shi ne take nema ta suma ki cigaba kar ki fasa halinki”

Aliyu ya tsaya a kan ruma ya ce “Ke, ki na wani sokwancin ki ka yadda aka dake ki har ki ke wa mutane kuka?” Ruma ta yi shiru ba ta amsa ba.

“Ina fatan dai ba a gaban wadda ta dake kin ki ka yi kukan ba? Wallahi da ina gidan nan sai kin fita kin rama, dan ubanki yaushe ki ka koma shashasha har aka dakeki aka fitar miki da jini, ‘yar uban waye da baki taka mini ita ba”

Buɗe baki mama ta yi, ta kalli Aliyu ta ce “Gadanga, maimakon ku tayani yi mata faɗa, ku ke mara mata baya? Ba sai ku ce Allah ya sa hakan ya zama silar shiriyarta ba”

Aliyu ya girgiza kai ya ce “A’a Addu’a ce kawai za ta shiryata, amma ba a daketa a waje ta tsaya tana kuka ba, babu rago a gidan nan, ko ɗan uban waye ta daka zamu bada haƙuri, amma wallahi aka kuma dukanki a waje, ki ka zo mana gida ki na kuka, sai na ƙara miki wallahi, idan mazane kawai ban yadda ki yi faɗa da maza ba, ki zo ki gaya mini, amma mace dai ‘yar uwakki, ki tattaka mini kowacece”

Aikuwa mama ta haɗasu gaba ɗaya ta din ga faɗa kamar ta ari baki.

“Kaf cikinku babu wanda na sha wahalr rainonsa kamar ruma, amma kuna zigata ta ɗauko magana, rainonta dai-dai yake da rainon fitinannun yara maza huɗu, maimakon ku tayani dawo da ita hanya, amma ku ke ingizata”

Gaba daya suka yi wa mama shiru, ta yi ta banbaminta ta yi ta gama.

*****
Karkarwa jikinsa yake yi, tamkar zai hau bori, jikinsa sai wani ƙaƙƙamewa yake yi, tamkar ba jikin ɗan Adam ba.
Wata matashiyar mace ce zaune a kan gadon, tana kallonsa, ido fal hawaye, ya yin da shi kuma ya cigaba da tunkararta.
Girgiza masa kai take yi, amma ta kasa motsawa balle ta gudu.
Yana zuwa ya zauna a gabanta ya tsura mata ido, ya miƙa hannunsa kan cikinta, take jikinta ya hau rawa ta rintse idanuwanta, tana zubar da hawaye. Sautin muryarta ne ya dakatar da shi ga aikata abin da yake ƙoƙarin yi
*Sarki ka ganni, ya na ga sarki da ƙananan kaya, sarki ka kalleni* tamkar a zahiri haka yake jin muryartata a cikin kunnuwansa, a hankali ya buɗe ido ya na ƙarewa ɗakinsa kallo. Sai a lokacin ya gane mafarki yake yi, ba zahiri bane.
A hankali ya tashi ya zauna, ya yaye bargon da ya rufa da shi, ya kalli agogon da ke kafe a jikin bangon ɗakin. Ƙarfe tara da rabi.
Ɗan guntun tsaki ya ja, me yasa yake yawan jin muryarta ne? Anya ba aljana ba ce ita ma?. Gabansa ne ya faɗi da yayi wannan tunanin, da kuma tuna matsalar da yake ciki, yake ta neman mafita a kanta.
Saurin girgiza kai ya yi, ya sauka daga kan gadon, ya wuce banɗaki.

****
Cikin matsanancin razani ta ƙwala ihu “Wayyo Allah mama” a gigice mama tayi kanta tana faɗin “Ke lafiyar ki kuwa?”

Tashi ta yi zaune ta na rarraba ido, tana kallon ɗakin.

“Lafiya menene?”

“Mafarki na yi na tsorata”

Mama ta ja tsaki ta ce “Ba dole ki dinga mafarki kina tsorata ba, tun da ba kya Addu’a kwanciya bacci”.

“Wallahi mama na yi”

“Ke ki ka sani dai, ko a garin neman maganar ki ruma, kya tsokano abin da zai dinga tsorata ki, ya hana ki bacci tashi ki je ki yo alwala, yanzu za a kira sallar asuba.
Haka nan jiki babu ƙwari, ta tashi ta yi alwala ta gabatar da raka’atanul fajr, sannan ta yi sallar asuba.
Jikinta duk yayi sanyi da mafarkin da ta yi, amma ta kasa tuna me ta gani a mafarkin ya tsorata ta.

Babu wanda Ruma ta kula a ajinsu, ta nemi wuri ta yi zamanta ta yi shiru, tana ta takura ƙwaƙwalwarta, ta tuna mafarkin da ta yi ya bata tsoro, amma ta kasa har aka kusa tashi, hankalinta baya tare da ita.

Asiya ce ta zo kan ruma ta tsaya, ta riƙe ƙugu ta ce “Ki je ki wanke banɗakin da aka saka ki, ko na je na faɗa” tamkar ruma na jin tsoron Asiya, haka ta tashi jiki na rawa zata fita daga ajin, sai dai ta yi burki a gaban allo, ta ɗaukko chalk a aljihun rigarta, ta sake zana wata shirgegiyar matar, wadda tafi ta jiya, ta yi labelling ɗin ta.
Ta waiwayo kuma tana kallon Asiya, tare da jiran ko ta kwana.

Aikuwa kamar ruma ta san a rina, Asiya ta kuma nufo ruma, tana zuba ashar, kan ta ƙaraso ruma ta yi ciki da ita, suka faɗa kan wasu ɗalibai.
Hannun Asiya ɗaya ta samu, ta din ga duka kamar ta samu ɓarawo, sai da ta tabattar da ba zata iya kai duka da hannun ba, sannan ta koma fuskarta.

An kai ruwa rana kan a ƙwaci Asiya daga hannun ruma, sai a lokacin ruma ta ji hankalinta ya kwanta, baƙin cikin da ya tokare mata zuciya ya sauka.
Babu wata-wata, malamin su ruma ya saka su kneeldown a rana, ba tare da ya tsaya ya ji ba’asin ma meyafaru ba.

Tun a lokacin Asiya ta ji ba ta iya motsa hannun da ruma ta din ga jibga, ta din ga jin kamar ba a jikinta yake ba.

Suna Kneeldown ruma ta riƙe ƙugu ta ce “Ke kin isa ki dakeni na ƙyaleki, hmm baki sanni bane, kuma wallahi ban huce ba, zaki ga abin da zan yi miki, ki dakeni ki zageni, sannan ki zaci kin ci bulus, ai faɗa ni da ke daga yau har ranar busa ƙaho, ba dai uwata ce tsohuwar banza ba sai ka ce babata sa’arki ce ba? Ai ki yi mini komai ban da taɓa uwata, ban taɓa zagin uwar wani ba, kema babarki  jibgegiyar bayerabiya masu kashi a leda”

Gigicewa Asiya ta yi, tana kuka tana son kaiwa ruma duka, amma ta kasa sarrafa hannunta ga ciwon da jikinta yake yi mata.
Ruma ta durƙusa ta dinga dumbuzar ƙasa hannu bibbiyu tana watsawa Asiya a fuska. Ban da kuka babu abin da Asiya take yi.

Ranar ma sai da aka tashi sannan aka sallame su, aka ce gobe da safe za su cigaba da punishment.

Rumaisa ta riga Asiya tafiya, ta je ta samu hanya, ta tattara duwatsu, ta tara su a cikin jakarta. Ta kuma datsar Asiya a hanya, ta dinga kabbara tana jifanta. “Sheɗaniya gara na jefeki na huta, na ga haka ake yi idan an je makka a jefi sheiɗan, gobe ko cewa aka yi ki kalleni, ba zaki sake ba balle ki dakeni”

Sai da ruma ta gama abin da Allah ya nufeta da yi, sannan ta wuce gida. Yau kam bakinta har kunne, jin ta take wasai ba ta da wata damuwa ko banza ta rama abin da aka yi mata har da riba, malamai kuwa ko zasu kwaɗata su cinye bai dameta ba.

Abdallah ne yake ta shiri, ruma sai tambayarsa take ina zashi?.

“Ke wai kin aikeni ne?”

“A’a, amma dan Allah ka gaya mini”

“Cikin gari zani ziyara”

Ta haɗa hannayenta biyu ta ce “Dan annabin rahama ka tafi da ni” hararta ya yi ya cigaba da shirinsa.
Ta dinga bin sa tana lallaɓa shi, har ya amince zai tafi da ita.
Mama ta ce “Hmm in dai ruma ce zata baka kunya, Allah ya sa kar ta ɗauko maka magana”

“Ta ɗauko ma, dakuwa zata yi wallahi”

Ruma ba ƙaramin daɗi ta ji ba, ganin ta a cikin gari cikin ‘yan uwa, akwai ‘yan uwan mama sosai a cikin gari, sai dai mama ba ta zuwa da ita, saboda ta din ga neman magana da dukan ‘ya’yan mutane kenan.

Akwai wata ‘yar cousin ɗin mama, da rashin jin su ya kusa zuwa ɗaya da na ruma, duk da ruma ta fita. Ta ce “Ruma, zo mu je yakasai, akwai ƙawata a gidan Turakin Kano, jikarsa ce biki ake a gidan, kuma za ayi kilisa, kan Abdallah ya dawo mun je mun dawo, mu je mu ciyo banza”

Ruma ta ce “yauwwa hauwwaliya, yi sauri ki shirya mu tafi kan ya dawo ya hana ni zuwa”

“Ke har da babbar leda zan ɗauko, idan mun ci mu ƙullo sauran”

Haka suka shirya, suka yi sallama a kan zasu je biki su dawo.

Suna tafe a hanya suka sai masara, suna tafe suna ci suna hira.

Tabbas idan ka ji wane ba ƙarya ba, gidan ya tsaru yayi kyau sosai da sosai, gini ne na sarauta da aka ƙawata da kayan alatu, ruma sai rarraba ido take yi.

Ƙawar hawwaliya ta din ga murna da ta gansu, ta kai su wani falo suka zauna.

Ruma kuwa hankalinta na kan wata mata, da ta sha ado sai kai wa take tana komowa tana wani hura hanci, tana dakawa mutane tsawa.

Ruma ta ce “Taɓ, wai wacece waccan?”

Yarinyar ta kalli wadda Ruma ta nuna ta ce “Laa Anty Samha ce, ƙanwar mama ce, ba mata bace ba ta da aure”.

Ruma ta ce “too na ganta wata gwabjejiya, sai masifa take yiwa mutane, ni na zaci matar sarki ce ma, yakamata a samu mai kwaɗeta ya zata din ga hantarar mutane?”

Hauwwaliya ta daki cinyar ruma ta ce “Ke, ƙanwar mamanta cefa”

Yarinyar ta yi murmushin yaƙe ta ce “Bari a kawo muku Abinci, sai mu je wurin kiɗan ƙwarya da kilisa”

Ruma ta miƙe ta ce “Hauwwaliya, ni dai zan je wurin da na ga an ɗaure dokuna na kallesu, idan an kawo Abincin ki ƙulle mini nawa a ledar da ki ka zo da ita” buɗe baki Hauwwaliya ta yi, da jin hansfreen da ruma ta yi musu.

Kai tsaye ruma ta fito tana cigaba da kallon gidan, da yadda manyan mata ke shiga suna fita, da shiga kala-kala.

“Ke ba kya gani ne, meye haka?” Ruma ta ɗaga kai ta kalli wadda ta daka mata tsawar. Matar da take ta hantarar mutane ce.

“Eh bana gani, sandata na fito nema, ke da ki ke gani meya hana ki kauce?” Ruma ta yi maganar tana tsare Samha da ido.

Wata mummunar faɗuwar gaba ta ziyarci Samha, da ta yi tozali da idanun ruma, ga ta ƙarama amma wani abu mai kaifi ne a idanun ruma.
Ruma ta raɓata ta wuce abinta. Da sauri Samha ta bi bayan ruma, amma ta nemeta ta rasa.

Kai tsaye burgar dawakin da suka wuce ta je ta tsaya. Ta tarar da wani dogari yana basu Abinci.
“Sannu da aiki”
Ya kalli ruma ya ce “Yauwwa sannunki”
“Dan Allah ina dokin sarki a nan?” Yayi murmushi ya ce “Nan babu dokin sarki, na ‘ya’yan sarki da manyan Hakiman fada ne”
“Dan Allah ka cewa sarki ya bani doki ɗaya”
Yayi dariya ya ce “Ke idan aka baki doki ya zaki yi da shi?”
“Hawa zan din ga yi mana” ruma ta din ga yiwa dogarin nan surutu, sai da ya gaji sannan ya ce “To ai Shikenan, yanzu dai fita za ayi da su, za ayi kilisar angwaye”
Ta jinjina masa kai, ta koma gefe ta tsaya, tana kallo aka shirya dawakan, aka yi musu kwalliya sannan aka fita da su.
Hauwwaliya ce ta fito ita da ƙawar ta ta tana faɗin “Ke ruma, tun ɗazu jira nake ki dawo, amma ki ka ƙi komawa”
“Ke ƙyaleni, kallon dokuna nake”
Ƙawar hawwaliya wadda suke da Turaki, ta ce “Mu je to, sai mu kalli kilisar”
Suka fita daga cikin gidan gaba ɗayansu, kan barandar wani gida suka je suka tsaya, suna tsumayin a fara kilisar.
Abin yana burge ruma sosai da sosai, duk wanda ya zo wucewa sai ta ɗaga masa hannu tana tsalle.Tun da suke wucewa babu wanda ta kira sarki, sai da ya zo wucewa tare da ango.
“Sarki mai koriyar alkyabba, a dawo lafiya, dan Allah ka bani kyautar doki, ko kuma ka ɗanani a kan dokinka!!!”
(Wannan ‘ya ni kaina tana bani ciwon kai 😒 in kun ji ni shiru ku dinga yi mini addu’a, Allah ya ƙara mini lafiya 🙏)

Mai nema daga farko, ya duba watpad Please 🙏
Ayshercool
08081012143
[21/07, 10:53 am] JAKADIYAR AREWA:                 ƘANWAR MAZA
Na Aisha Adam (Ayshercool)

MIKIYA WRITER’S ASSOCIATES

*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHI YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA? TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN FATA NE? KO KUWA SO KI KE FATARKI TA DIN GA SHEƘI TA NA HASKAWA? MAZA KI GARZAYO WURIN MEENA DOMIN SAMUN MAFITA*

*Royal jelly big 22000*
*Royal jelly 30 pieces 2200*
*Royal jelly small one 60 pieces inside the pack 3000*
*Vitamin C-100, 2700*
*Vitamin E big 3000*
*Pesona 2300*
*Dara 2300*
*Cantik ayu 2300*
*GLUTA white 2700*
*Khusus ibu 3800*
*Sugar wanita 3500*
*Majakani 3 in 1 3200*
*Eve Care 3700*
*Juliet eve 11,500*
*Phyton buster 18,000*
*Phyton collegen 18,000*
*Glute sparkling 18,000*
*7 days ginger oil for hair 1,200*
*Papaya oil for breast 1,200*
*Garlic oil for hips 1200*
*Vitamin C serum 1,500*
*Vitamin E serum 1,500*
*Busty blend 2800*
*Gluta prime 2800*
*Collegen+C 3800*
*Yan uwa abun fa da yawa bazan iya kawosu gaba daya ba amma muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

 

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels
*Wai ina da ku fans, ace haryanzu ban haɗa 1k subscribers a channel ɗina ba, anya akwai amana kuwa😒*

Ku yi subscribing  YouTube channel ɗin
@Cool Hausa Novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro.

 

*Ina yiwa ‘yan uwa musulmi barka da shigowar, sabuwar shekara musulunci, Ubangiji Allah ya sada mu da alkhairan da yake cikinta, akasin haka kuma Allah ya iya mana*

 

Back to top button