Arubuce Ta Ke Hausa NovelHausa Novels

Arubuce Ta Ke 78

Sponsored Links

Page 78

Bakinta ya mutu murus,sai rawa da jikinta kawai yakeyi,abun ya bashi tausayi sosai,baiyi experiencing haka daga wajen hafsat ba a wancan lokacin,shi yasa a yanzu yake ganin komai daban,amma daya tuna banbancin shekarun sai ya fahimci dole a samu irin hakan,widad din yarinya ce sosai,dole tafi hafsat shan jiki.

Sau uku yana sauya musu ruwa mai dumi sosai,kusan duka dashi akeyin gashin,har sai daya kintaci lokaci sannan ya canza ruwa me kyau

“Zaki iya wankan da kanki?” Duk.yadda takejin nauyin ganinta da yayi a haka bata jin zata iya wankan da kanta indai toilet din takeso bari,don ko ina na jikinta rawa yakeyi,saita girgiza masa kai.

Da kansa ya wanketa tas kamar su mimi,ya nadota a towel ya fito da ita,wajen shiryawa ne ta riqe towel din tace zata iya da kanta,ya saki boyayyen murmushi,don dariya ta bashi,abunda take fa boyon a yau ya gansu ya ta kuma taba halalinsa son ransa,saidai inda ta bashi damar da haka zaiso,don bai gaji ba,yana jin kamar ma ba’a yi komai ba.

Bai matsa da yawa ba ya dauko mata komai ya aje mata kusa da ita ta yadda basai tayi tafiya me yawa ba sannan ya fice.

Kitchen ya wuce da kansa ya fara hada musu breakfast,duk bayan sakanni sai wani murmushi ya subuce masa,ya koma kamar wani zautacce shi kadai,wani irin wasai yake jinsa tamkar angon da yayi kwanan farko a gidansa,ji yakeyi kamar an canzashi,kamar ba shine abbas ba.

Lafiyayyen breakfast ya hada,ya shirya komai saman tray abun sha’awa kamar ba girkin namiji ba,ya jima da koyawa kansa girki,tun bai iya ba har dolen dole ta saka ya koya din,banda ya iya din ya tabbatar da tuni yunwa tayi masa illa indai don ta hafsat ce.

A cure waje daya ya sameta tana ta rawar sanyi,ya ajjiye tray din ya isa inda take ya fara qoqarin dagota cikin damuwa,sai ya samu kuka takeyi

“Ya rabb…..” Ya fada cikin tsananin damuwa,gaba daya jikin nata ya rikice da zafi,ga complain na ciwon da takeji

“Kiyi haquri kici.wani abu,sai muje kiga likita” ya fada a tausashe cikin sigar lallashi,gaba daya yayi wani mugun laushi.

Kafada ta maqale cikin salon rigima hawaye ya ziraro mata,sai da ya murde ya koma ainihin abbas dinsa sannan ta yarda ta tsaya,ya hada tea ya zuba komai a plate ya saisaita zafinsa,sannan ya matso kusa da ita hannunsa dauke da mug din

“Ehennnn…..oya,take it” da kadan da kadan take kurba bakinta yana rawa,bata wani sha mai yawa ba ta fara kelaya amai,sai data dawo da komai na cikinta.

Tsaf ya gyara wajen da kansa,sannan ya dauki waya yayi kiran samuel yace ya bincika asibiti mafi kusa dasu yayi musu booking,idan so samu ne asibitin Dr jessica

“Yes sir….zanzo na daukeka ne?” Sasssan da widad ke kwance ya kalla,sai ya girgiza masa kai hadi da cewa

“Nob,idan ka gama abinda nace maka shikenan,you can go”

“Yes sir” ya sake fada cikin girmamawa,wayar ya ajjiye ya soma takawa zuwa inda take kwance,ba samuel ba,koma waye bazai iya bari yayi driving widad din ba,yana jin kamar tsokar zuciyarsa ce ke rayuwa a wajen jikinsa.

Gaban gadon ya koma,a tausashe ya duqa gabanta,ya saka hannu ya nutse ya janye gashin kanta daya rufe rabin fuskarta baya,idanunsa a kan fuskartata daya wani taushi ta kuma canza lokaci guda.

A hankali ta bude idonta suka sauka cikin nashi,sai tayi saurin maidasu ta rufe,wani mugun kyau yaga ta qara masa a hakan

“Zaki iya tashi muje asibiti?” Fuska ta narke,ita kam gaba daya bata qaunar abinda zai sanya ta motsa,amma hakanan yayi mata dabara cikin lallabawa ya sanyata tashi ta saka hijab dinta suka fito.

Yana driving amma duk bayan wasu sakanni sai ya juya ya kalleta,ta tattare gu daya cikin seat din motar,sai ya miqa hannu ya kashe ac din motar,yadan qara speed don su isa da wuri.

Already samuel ya gama komai,dr jessica ce da kanta,cikin girmamawa ta nuna musu seat,ya zaunar da widad wadda taketa bi da kallo,cikin zuciyarta tana ta yaba kyanta,shi kuma ya tsaya daga bayanta kamar wani bodyguard.

Akwai sanayya tsakaninsu,don haka ta fara gaidashi cikin girmamawa,ya amsa mata tare da tambayarta aiki

“me yake damunki madam?” Dr jessica ta tambayi widad tana murmushi,idanu a narke ta maida dubanta ga abbas,saboda batasan kalar amsar da zata bata ba,sai ya share kamar bai gane tana kallonsa ba

“Uhmm,inajinki madam,fell free,kiyi bayani” ta fada tana jan takardar dake gabanta.

Bai ankara ba sai sheshsheqar kukanta da yaji,ya daga kai da sauri daga danna wayar da yakeyi yana dubanta,sai yaja kujerar kusa da ita ya zauna har gwiwoyinsu na gogayya dana juna

“Listen widad?,me kuma ya faru?” Muryarta a shaqe a kuma shagwabe qwarai tace

“Kaine” sosai sound dinta ya taba zuciyarsa,ya saki murmushi

“Okay,to ya isa,dr……she had her first night,she feels that the place is hurting her” kai dr jessica ta gyada sannan tace

“Muje na duba” bata gane me take nufi ba sai data hau gadon da take duba marasa lafiya bayan abbas ya taimaka mata,nan ta fara raba idanu,ta kuma narke masa tana hawaye sosai,don kunya takeji ta buda gurin kuma a sake gani?.

Da qyar yasha kanta yana riqe da tafin hannunsa cikin nata ha dr jessica ta gama dubawa ta koma kan kujerarta

“It’s bruises,you hurt her a lot sir,but ba damuwa,she will recover in a few days” ta fada tana jan takarda

“Saika qara haquri sir, she’s too young,dole ta samu ciwuka haka musamman idan ya zamana anyi gaggawa,but with time zata saba” tura baki widad tayi gaba,itama dr din nan bata da kunya,zata saba dame?,yayin da abbas yadan saci kallonta ya saki boyayyen murmushi

“Allah yasa” ya fadi qasa qasa,cikin ransa yake hasashen lokacin da widad din zata sallama masa ruhi zuciya da kuma rayuwarta,lallai da ya shiga jerin maza mafi sa’a a duniya.

Magunguna ta rubuta mata masu kyau,sannan ta basu wasu shawarwari har hakan yasa widad din tadan sake,saidai kunya kamar qasa zata tsage ta shige,tana ganin kawai abbas din ya gama kunyatata.

Ko a hanya da wani irin nutsuwa da takatsantsan yake driving din,dukka hankalinsa da kulawarsa yana kanta,haka da suka koma gida,ya sanyata gaba da tambayar abinda takeson ci,saidai taqi sawa bakinta komai don bata da appetite,gaba daya taste din bakinta ya gama daukewa,tana ta faman koke koke,ta narke masa qwarai,dama hausawa sukace mai neman kuka ne aka jefeshi da kashin awaki,tsohuwar rigima da kuma shagwaba gaba daya ranar bawan Allah abbas aka juyewa,shi kuwa ya sanya hannu bibbiyu ya karba,saboda a yanzun jinta yake dai dai da ruhinsa.

Girki kusan kala uku yayi mata amma tace bata ci,daga qarshe sai daya hade girar sama da qasa ya zaunar da ita ya dinga bata da kansa sannan ya samu taci,ya bata maganungunan tasha bayan ya tilasta mata ta shiga ruwa.

Saman cinyarsa ya dora kanta,taso ta zame amma ya hanata,yanason kawo kusanci sosai a tsakaninsa da ita,ya kuma fidda dukka wani tsoro nasa daga zuciyarta daya dasu a daren jiya,sai tayi likimo ta lumshe ido tana sauke ajiyar zuciya,ita kanta tana matuqar son kwanciya a jikinsa,bata taba jin wani guri da take jin wani nutsuwa da kwanciyar hankali idan tana gurin ba irin cinyar tasa,amma for now tsoronsa takeji, tsoronsa takeji sosai,gani take kamar idan tayi bacci zai sake maimaita mata abinda ya aikata mata jiya.

Sannu a hankali bacci mai dadi yayi awon gaba da ita,ya sauke ajiyar zuciya yana gyara mata kwanciya sosai yana kallon fuskarta, murmushi ya sake subuce masa,yakai.hannu zai shafi lips dinta sai kuma ya janye hannu da sauri gudun kada ya tasheta.

Wuni guda ranar suna tare cikin gidan,kwata kwata ma ya manta da wani batun aiki,sai da aka nemeshi a gurin aikin sannan ya bada excuse din yana da patient.

A daren duk yadda taso bijirewa kwana dakin haka ya mata dole ta kwana a dakin kuma cikin jikinsa,dukkansu shi da itan wani irin ni’imtaccen bacci ne yayi awon gaba dasu.

Ko cikin duniyar baccinsa ya tabbatar da cewa wani gagarumin ci gaba da sauyi ne ya tunkaro rayuwarsa,sauka da shigar numfashinsa cikin wata irin nutsuwa.

Washegari bayan sun idar da sallar asuba,dukkansu shi da ita suna saman abun sallah,kowanne jinsa yake kamar a wata sabuwar duniyar,musamman abbas da yakejin jiki da qirjinsa wasai,babu komai a ciki sai wata irin mahaukaciyar soyayyar widad din.

“Ina kwana?” Ta fada qasa qasa kanta a qasa tana murza tafin hannunta.

Gaba dayansa ya waiwayo,sai ya saki murmushi,ya cira hannunsa a nutse ya miqa mata yana cewa

“Zo nan mu gaisa da kyau” manyan idanunta da suka dan fada kadan ta daga ta kalleshi,sai ta noqe kafada,don gaba daya tsoronsa takeji

“Please mana baby doll” ya fada da wata irin kwantacciyar murya,qas ta sakeyi da kanta tana tuna kalaman mommynta,sai ta miqe a hankali ta fara takowa zuwa gabansa.

Da idanu ya bita,yana jinta tana tsarga masa har cikin jinin jikinsa,yabi takunta da kallo,akan tsari take ajiye qafafun nata kamar wadda ake qirga ma adadin takunta.

A gabansa ta tsugunna tana watsa masa qamshin jikinta,lumshe idonsa yayi zuciyarsa na bugawa,duk yadda taso daurewa ya kauda kai ya gaza,sai yasa hannunsa ya fusgota a tausashe yayi masauki a jikinsa.

A tausashe ya maida hannuwansa ya rungumeta

“Kin tashi lpy my baby?,ya jikin?” Ya rada mata a hankali cikin kunnuwanta,har sai da duk wata tsiga ta jikinta ta tashi,ta lumshe idonta gabanta yana bugawa da sauri da sauri

“Da sauqi”

“Ma sha Allah……haka nakeson ji,Allah yayi miki albarka” har cikin zuciyarta taji sanyin addu’ar,ya motsa bakinsa zaiyi magana,kafin yace komai wayarsa dake gefe ta dauki ringing.

A nutse ya sauke idanunsa yana duba mai kiran,hafsat ce,sai ya tsaya yana kallon wayar kamar mai son karanto dalilin kiran nata ta cikin wayar.
[3/18, 3:05 PM] +234 903 685 1413: *H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K’addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Leave a Reply

Back to top button