Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 38

Sponsored Links

Kamar sokuwa haka ruma ta bi bashir da kallo, daga bisani ta ja wani uban tsaki ta ce “Dan Allah ka daina raina mini hankali, wai komai nawa sai wannan mutumin ya shigo ciki, to wallahi ba shi bane ba, ɗana ne ba shi ne babansa ba”.  Ko cikin gushewar hankali takawa ba zai manta wannan muryar me shegen karaɗi da tsiwar tsiya ba. Shi kansa mamaki yake yadda aka yi rumaisa take shigowa cikin rayuwarsa a bazata. Ya ɗaga jajayen idanunsa ya na ƙare mata kallo.

Usman ya ce “Rumaisa, kin ga ki nutsu kin ji, shi a ina ki ka san shi?”

Ta kalli Bashir, sannan ta ɗan kalli takawa, ta girgiza kai ta ce “Ni ban san shi ba, ku karɓo ɗana ku bani, ba shine babansa ba, ni ba shi ta ce mini ba”.

Bashir shima ya ƙarasa gaban rumaisa ya ce “Rumaisa, ba cewa ki ka yi tace miki ita ‘yar turakin kano ba ce? Ta ce miki giwar Galadima ce sirikarta ba, to ai ga giwar Galadima nan, Adam kuma ɗanta ne” ruma ta yi shiru ta tafi tunanin abun da ya faru ita da Aisha.

Lokacin da ta kammala bawa Aisha labarin abun da ya faru a tsakaninta da Adam, ta din ga yi mata dariya ta ce “Kamar na san mutumin nan da kike bani labari”.

Rumaisa ta ce “Taɓ, aikuwa idan ɗan uwanku ne sai dai ki yi haƙuri dan ba shi da mutunci, bama ki san shi ba anty aisha”.

Aisha ta kalli ruma ta ce “Ɗan gidan marigayi Galadiman Kano ki ka ce ko?”

“Oho masa, amma dai kamsr haka aka ce”

“Amma da ƙarfin hali kike ruma, dan ƙarfin hali babban mutum ki yi masa wannan rashin kunyar?”

Ruma ta taɓe baki ta ce “Ai ni Allah kaɗai nake tsoro”

Aisha ta yi murmushi ta ce “To ki yafe masa mana my baby rumaisa” ruma ta daki ƙasa ta ce “Ai ko shine zai zo gabana ya ce na yafe masa ba zan yafe masa ba, kin ga rashin muntucin da yayi mini, har da ce mini ‘yar talakawa, yanzu da ciki ya fito mini da ya taɓa mini nono fa, ina zan saka kaina?”

Tayi dariya ta ce “Ai bai fito ɗin ba, kuma gaskiya kar ki yi masa sharri dan kin tsane shi, you are still a baby, ina wani nono a nan banda sharrinki ruma? Ko kwatan nawa ba su kai ba fa, ko ganinsu ba ayi”

Rumaisa ta ce “Wallahi sun fara fitowa, mama ta ce duk wanda ya taɓa ciki zai fito mini, kuma korata za su yi daga gidan su, yanzu da ya sa an koreni fa, ni fa bana son ma su fito, idan ba haka ba mama zata hanani yawo ba riga, yanzu ma hanani take yi”

Aisha ta yi dariya ta ce. “gaskiya ki daina zaginsa tun da dai ba a korekin ba, kin yi masa sharri, ina wani abun taɓawa a nan” tayi maganar tana sake tuntsirewa ruma da dariya.

Ruma ta ce “Wallahi ya taɓa, kuma idan Allah ya sa na bar nan idona idonsa zai gane bashi da wayo, ana i gobe zan zo katsina, yayi mini wanka da kwata a tsakiyar layi, wai har da cewa na yi masa sharri da nace ya taɓani, wai zuwa yayi ya duba ya ga ko akwai wani abu a ƙirjina ki ji ɗan iska fa”

Aisha ta dafe ƙirji ta ce “Wayyo zuciyata, haba baby rumaisa sunan mijina adam, kar ki sa kishina ya tashi. Amma ni nawa Adam ɗin shima yana da zafin zuciya, baya son raini ga miskilanci, amma idan ki ka fahimce shi, mutumin kirki ne, mai son kulawaga iya soyayya, sai dai….” ta ɗan yi shiru sai kuma ta ce “Ruma zaki auri Adam?”

Ruma ta waro ido ta ce “wane Adam ɗin? Ni da ban yi tsawo na girma ba za ayi mini aure?”.

“Adam da kuke faɗa, ki yafe masa ko dan albarkacin yana da sunan mijina”

Ruma ta turɓuna fuska ta ce “Ai wallahi ko yayanki ne ba zan yafe masa ba, da in auri Wannan gara na mutu ba aure, kuma ni miji kyakkyawa nake so, kuma mai kuɗi”

“In dai kuɗi ne akwai su ruma, kuma ai kyakykyawa ne”

Rumaisa ta dubeta ta ce “Ba fa mijinki ba, wannan da muke faɗa nake gaya miki, mai suffar mugwaye da wata banzar motarsa in sha Allah sai an sace motar ma”.

“In an saceta ma zai sai wata, kuma ya sai miki kema, banda faɗan rashin gaskiya ke fa ki ka fara zaginsa a social media, amma tsabar rigimarki kina ta zaginsa, kin ci sa’a da bai ɗaureki ba, ko ya sa a zaneki ba”.

“Oho ni dai ban yafe ba”

Tayi ajiyar zuciya ta ce “I love your confidence my dear, you can face the challenges. Jikina na bani wani abu game da ke, zaki iya ruma” tayi maganar tana jan kunatun rumaisa ta ce “Kamar haka mijina yake wasa da kumatuna”.

“Anty Aisha, yake taɓaki? Ba a wasa da maza fa” ba ta bawa ruma amsa ba, sai dariya da take yi mata, tana fatan Allah ya tabbatar da abun da take ji game da ruma.

Ranar da zata rasu bayan ta haihu, ta riƙe hannun rumaisa ta ce “Baby rumaisa, idan Allah ya sa kin kuɓuta, ni ‘yar gidan turakin kano ce, amma kar a nemi mahaifina kai tsaye a nemi sirikata, idan ba zaki iya riƙe jaririn nan ba, ki danƙa mata shi, Hajiya Binta giwar Galadima, uwar gidan galadiman kano, sirikata ce ita zaki danƙawa jaririn nan, ɗan ta shine mijina” a lokacin gaba ɗaya ruma ta manta da wani adam balle ta kawo shi a lissafi da aisha ta yi zancen galadima.

Ko da ruma ta zo nan a tunaninta sai ta tambayi kanta ‘Kenan da gaske shi ne mijinta?’ a zahiri kuwa ta fashe da kuka ta ce “Wallahi ba shi ne babansa ba, ni ba shi ta ce mini ba” a bata iya tafiya ta fara ƙoƙarin dirowa daga kan gadon tana miƙa hannu ta ce “Ni ku bani jaririna, ba ɗansa bane ba, ni ba ta ce mini in bawa kowa ba, ku bani ɗana” mama tayi shiru ta zubawa sarautar Allah ido.

Bashir ya miƙawa Adam hannu ya ce “Ka ga Adam, kawo yaron nan, gaba ɗaya a ruɗe take, kamar ba ta hayyacinta ne ma, kawo a bata shi kan muga yadda hali zai yi”.

“Bashir ka haukace ne? Taya ka ke cewa in baka ɗana ka bawa wani?”.

“Wallahi ba ɗansa bane ba, ku bani ɗana” ruma tayi maganar tana kuka.

Bashir ya karɓe yaron, ya miƙawa rumaisa, ta rungumeshi tana fashewa da kuka ta ce “Cewa ta yi idan ba zan iya riƙe shi ba, in bawa giwar Galadima ni ban santa ba ma, ban san a in da take ba, amma ni dai zan iya riƙe yarona, ai cewa ta yi ta bar mini shi har abada nice mamansa”. Gaba daya ɗakin aka zubawa sarautar Allah ido.

Ammi da tun ɗazu take zaune kamar an shukata, ta kasa magana sai tasbihi kawai da take yi, ta tashi sannu a hankali, ta je kusa da rumaisa suka matsa mata ta zauna.
Ta dafa kafaɗar rumaisa idonta fal hawaye ta ce “‘ya ta, nice giwar Galadiman kano mai rasuwa, Adam kuma ɗana ne, shine mahaifin wannan jaririn, kuma mijin Aisha”.

Ruma ta girgiza kai ta ce “A’a wallahi ba shi bane ba, ni fa ba zan bawa kowa ba, ni ta ce ta barwa shi”.

Ammi ta ce “To shikenan, na ji babu mai rabaki da yaronki, Ubangiji Allah ya baku lafiya gaba ɗaya, yanzu ki bayar da shi a mayar da shi sashen kula da yara”.

Rumaisa ta girgiza kai ta ce “Ba zan bayar da shi ba, haka kurum ya bishi ya sace shi, da in bashi ɗana gara na koma wurin ‘yan garkuwa da mutanen”.

Huzaifa ya ce “To fa ana wata ga wata”.

Ammi ta ce “To shikenan, rungume shi da kyau, kin ga bacci zai yi kema ki kwanta ki huta” a’a ba zan rufe idona in je ya gudu da shi ba.

Miƙewa Adam yayi jikinsa yana rawa, amma Ammi tayi masa wani irin kallo, tayi masa nuni da ya fita, yayi gaba ya tsaya ya waiwaya yana kallon rumaisa, da jaririnsa da yanzu ya shiga tunanin ina uwarsa? A wane hali kuma take ciki?”.

Suna tafe a hanya babu wanda ya iya cewa komai, sai Bashir da yake yi wa Adam nasiha “Adam dole sai mun bi yarinyar nan a hankali har yanzu a rikice take, kuma a cikin firgici ba ƙaramar azaba ta sha kan ta fito da yaron nan ba, kaga Yarinya ce ƙarama ikon Allah ne ya fito da su, dan ita ma ba gama sanin ciwon kanta tayi ba, a sannu zamu bita mu ji a ina ita Aishar take, sai mu zo mu yi shiri”.

Daga Ammi har takawa, babu wanda ya ce wani abu, kowa da abun da yake saƙawa a zuciyarsa, adam bai taɓa tunanin abubuwa su cukurkuɗe masa haka ba.

Suna zuwa gida ammi ta wuce part ɗinta, adam ma bai jira bashir ba, ya rufa mata baya.
A falo nusaiba ta tare ta tana tambayarta, “Ammi wai ina ki ka tafi haka, mun dawo daga islamiyya kawai muka tarar ba kya nan, kalli dare har ya fara yi fa” sai dai fuskar ammin ta nuna mata ba lafiya ba. Kan ta yi magana ta ga adam ya shigo ya bi bayan anmi, hakan ya sanya ta sha jinin jikinta.

A ɗaki ya tarar da ammi, ta ajiye carbin hannunta da mayafinta, hawaye tuni ya wanke mata fuska.

“Ammi dan Allah ki tsaya ki saurareni, kar ki yi mini haka”.

Ta kalli Adam ta ce “In saurareke ka gaya mini me adam, yanzu a duniya akwai abun da zaka iya ɓoye mini? Ta ina zamu kalli duniya mu fara bayanin abun da ya faru? Ta yaya duniya za ta yadda da cewar jaririn nan ɗanka ne? Da yaya zaka yi wa turaki bayanin abun da ya samu ‘yar sa, shikenan mun zama masu son kai kenan, idan maganar nan ta yaɗu ina zan saka kaina, ina ta ƙoƙarin toshe waccan kafar wannan ta ɓullo, adam kana me garin yaya haka ta faru ka ɓoye mini, ɗan da ba a san da cikinsa ba kawai mu ce ga ɗa meye shaidarmu ba ƙarya muke yi ba, ina ita Aishan?”

Adam da ya gama rikicewa ya ce “Dan Allah ammi ki fahimce ni, zan yi miki bayani bani da laifi, ba domin na ɓoye miki na yi duk abun da na yi ba”

Ammi ta katse shi ta hanyar cewa “To domin ka faranta mini ne? A tunaninka zan yi murna da hakan ne?”.

Ya girgiza kai tare da goge hawaye ya ce “A duniya bani da makusancin da ya fiki, daga ni har aisha, kin san komai Ammi, kamar yadda muke ta neman magani tsawon shekaru huɗu, aka dace cikin jikinta ya zauna, bayan ɓari da take ta yi babu ƙaƙƙautawa a dalilina, cikin nan  babu wanda ya san da shi, bayan ke sai mu, wanda hakan shawarar ki ce, har zuwa lokacin da kika bayar da shawarar ta je Saudiyya wurin ɗan uwanki kawu mahadi, ta zauna ta raini cikin a can, idan ya isa haihuwa ta dawo Nigeria, duk dan kaucewa hatsarin da ka iya faruwa da cikin, muka yi nesa da juna ni da ita.
Bayan na kai ta ta yi watanni huɗu, na sake komawa Saudiyya umara, na dubata, na dawo babu daɗewa ta ce mini ita ta gaji da zaman Saudiyya so take ta dawo gida. Ta ce mini wannan kakar ta ta, mariƙiyar mamanta babu lafiya, dan haka ita so take ta dawo ta je ta ganta, kar ta rasu basu gana ba. Gudun ɓacin ranki, ya sanya ta dawo babu wanda ya sani, sai dai a lokacin cikin yayi girma sosai ta sanya rigima a kan lallai sai ta je duba matar, an ce ba ta gane kowa, wankin ƙoda ake yi mata ma. Duk sauƙin kan Aisha, haka ta kafe a kan lallai sai ta je katsina duba matar, a daidai lokacin kuma ni tafiya Abuja ta kamani, bayan tafiyata ta sanya ɗaya daga yarana, masu tsaron lafiyarta ya kai ta katsina. Ta turo mini saƙo a waya tana bani haƙuri a kan ita fa ta tafi, ba zata iya jira na dawo ba, a tsorace take kar kakarta ta mutu. Bayan dawowata daga Abuja, sai samun saƙo na yi, an tsinci gawar yarona da motar, ita kuma ba a san in da take ba, tun da ga wannan lokacin nake ƙoƙarin gano in da take, har zuwa wannan lokaci, daga ni sai Bashir muke ta ƙoƙari, dan ko su Jabir basu sani ba, na san na yi laifi ammi amma ba da gayya na yi ba.

“Adam nika ɗai zan fuskanci wannan bayanin naka, duk mutane sun san da cewa tana Saudiyya, babu wanda ya san ta zo Nigeria haka zalika babu wanda ya san tana da cikin ma, kawai sai mu ce ga ɗa to ita tana ina, na gaya maka bana samunta a waya, amma ka yi ta yi mini ƙarairayi, dama akwai abun da zaka iya ɓoye mini Adam? Me zaka cewa Turaki?”.

A raunane Adam ya ce “Ko babu wata cikakkiyar shaida,ni na san da cewa ɗana ne, babu yadda za ayi yarinyar nan ta san wasu abubuwan idan ba gaya mata tayi ba, amma ammi ni yanzu ba abun da mutane zasu ce ne ya dameni ba, samo aisha ne ya dameni, babu wata hujja da nake jira yaron nan nawa ne, ko a fuskarsa kamanni na ne, sannan da kaina zan gayawa turaki komai, duk hukuncin da zai yi mini zan ɗauka”.

Ammi ta yi ajiyar zuciya ta ce “Zan cigaba da yi maka Addu’a, Allah ya kawo mana mafita, amma yarinyar nan ka bita a hankali dan Allah, in sha Allah yadda jaririn ya kuɓuta, ita ma zata kuɓuta”.

Adam ya jinjina kai kawai, ya tashi ya fita daga ɗakin, su Nusaiba suna falo a tsaye cirko-cirko, adam ya zo ya fice.
Cikin rige-rige suka tafi ɗakin Ammi, amma suka tarar ta shiga toilet, ko da ta fito umarni ta basu, na su je su kwanta sai da safe, dan kar su bi diddigin abun da ya faru, sai dai a tsorace take da abun da ka iya faruwa idan zancen nan ya fasu.

A asibiti kuwa, Aliyu ne ya dubi rumaisa ya ce “Ke dai a rayuwarki ba a taɓa rasaki da matsala, an samo uban yaro kin ce ba shi ne ubansa ba, sai ki nuna mana waye ubansa?”

Usman ya ce “Ai ko da uban me ki ke yawo, sai an mayar musu da ɗan su”

Mama ta ce “Yanzu dai a bar wannan maganar, Allah ya dawo mana da ita, daga dawowarta sai a bari ta sarara kan a hau yi mata faɗa, Ali ku je gida haka, kwa sanar da mutane an ganta”

Mai sunan Baba ya ce “Eh amma kar su sanar da Asibitin da take, kar azo a takura mata, ko ayi ta surutu saboda jaririn nan, a bari komai ya daidaita”

Mama ta ce “To hakan ma babu laifi, kar ku gayawa Abubakar a daren nan tun da ba a samu wayarsa ba, ku bari sai da safe kar ya ce zai bsro dutse yanzu”

Usman ya ce “In sha Allah”

Mai sunan Baba ya saka hannu, ya karɓi jaririn da ga hannun rumaisa, sai bin sa take da ido, kar ya fita ya bawa Adam yaron, ya ƙarewa yaron kallo ya ce “Bari na bawa nurses ɗin nan, su mayar da shi ɗakin da ake kulawa da sh, mama gobe in Allah ya kaimu zan zo mu koma ki ga likitan ki”

Mama ta ce “Ga mara lafiya ni ina zani? Dama rashin lafiya tawa saboda ita ne”

Ya ce “Duk da hakan, yakamata ke sai da safe, ki nutsu ban da gardama da taurin kai ki yi addu’a ki kwanta ki huta”

Kamar ba zata amsa ba sai kuma ta ce “Dan Allah mai sunan Baba kar ka bawa kowa shi, wallahi zan iya rasuwa idan aka rabani da shi” bai ko waiwayo ba ya fice daga ɗakin.

Mama ce ga rungumota tana rarrashinta ta ce ‘Ba wani zai bawa ba kin ji, ki yi haƙuri ɗakin da ake kula d shi zai kai shi” rumaisa ta yi lamo a jikin mama, can ta ce ‘Mama”

Mama ta amsa mata da na’am.

“Ba mafarki nake ba ko, ba zan kuma farkawa na ganni a dajin ba, na ga kun daɗe a wannan mafarkin nawa”.

Mama ta shafa bayanta ta ce “Ba mafarki bane ba, duk muna tare da ke”.

“Mama kin ga yadda ki ka rungumenin nan? Haka maman yaron nan take rungumeni tana rarrashina idan na tunaki ina kuka, sarƙarta da zobuna ne a cikin ɗankwalin nan, ɗan kunnen da ki ka cire a kunnena shi ma nata ne, mama ba zan manta da ita ba” rumaisa ta yi maganar cikin kuka.

“To ya isa, ita ma in sha Allah zata kuɓuta cikin amincin Allah” rumaisa ta cigaba da kuka, dan ba wanda ta gayawa aisha ta rasu.

Aliyu suna zuwa unguwarsu, ya wuce gidan su Habiba, lokacin kusan ƙarfe goma na dare, ya aika yaro ya ce yana sallama da Habiba.
Maimakon Habiba sai babarta ta fito tana masifa, wani watsatstsen ne ya zo neman habiba a wannan daren, yar habiban guda nawa take?

Tana ganin Aliyu ta yi sak, ta ce “Ya aka yi ne, ko laifin ta kuma yi maka, ko ƙanwar ta ka ta kuma duka ka zo rama mata, duk da ance an yi garkuwa da ita”

Ya ce “Ba ɗaya, wani abu zan gaya mata”.

“Wani abu ne kenan?”

Aliyu ya ce “Shikenan tun da na ga hankalinki bai kwanta ba”

Sai kuma ta ce “A’a, bari na taso ta” ta koma cikin gida, mintuna uku sai ga habiba ta fito tana mutsutsuka ido.

“Habiba” ya kira sunanta, ta kalleshi ta ce “Yaya Aliyu ina wuni”

“Albishirnki” yayi maganar cikin murmushi.

Ta ɗan yi saroro ta ce “Goro”.

“To zaki bani goron nan, Alhamdilillah addu’a ta karɓu, rumaisa ta kuɓuta yau, tana asibiti ma”

Gigicewa ta yi ta ce “Innalillahi, dan Allah da gaske, dan Allah kar ka ce da wasa kake yi, dan Allah mu je in ganta”.

“No, ba a zuwa wurinta yanzu, ba ta da lafiya, amma zan zo da kaina na kaiki ki ganta”

Hawaye ta fara matsewa tana “Allah sarki ƙawata, Alhamdilillah, Allah na gode maka”

Ya ce “Maza ki je ki cigaba da baccinki, Sai da safe”

“Dan Allah yaushe zaka zo ka kaini na ganta, gobe?”

“A’a zan zo dai, ki je ki cigaba da baccinki” yayi maganar yana ɗaga mata hannu ya tafi.

Ta shiga gida da gudu tana murna.

Adam kuwa yana zuwa ɗaki ya zauna ya fashe da kuka kamar yaron goye. Wai matarsa ce ta haihu a daji a hannun ‘yan bindiga, ko a yaya ta haihu oho, ko a wani hali take sanin gaibu sai Allah.

“Why aisha, meyasa ki kasa jira na dawo ki ka tafi? Duk yadda muka tssra rayuwa bayan kin haihu, ƙarshe a tsinto mini ɗana babu ke, haba aisha kin ga sakamakon rashin jin magana ko, matar da ki ke so ki je ki duba ita bata mutu ba, amma ke kin shiga wahala. Amma bakomai, Allah ya sa kina cikin ƙoshin lafiya, zan fito da ke ko da zan rasa rayuwata ne!

ƘANWAR ₦500 ne, via 0009450228 Aisha Adam jaiz bank, sai a tura shaidar biya ta 08081012143*

Ayshercool
08081012143.

*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI’IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA’A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA’IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA’IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni’ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau’in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*

*₦500 ne, via 0009450228 Aisha Adam, jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143*

Back to top button