Hausa NovelsKanwar Maza Hausa Novel

Kanwar Maza 51

Sponsored Links

 

Dariya ce ta kuwa kufcewa ammi, ta ce “A’a rumaisa wannan maganar dai taku ce ba tawa ba”

Takawa dai ko kallonta bai yi ba, dan ya fuskanci yarinyar ba ta da kunya sam.

“Amma dai ammi ai ni ban taɓa ganin maza suna shayarwa ba, shi kuma ya ce mini haka, kuma dai na ga shima ƙirjinsa babu komai”

Ammi rasa amsar da za ta bawa rumaisa ta yi, can sai hankalin rumaisa ya ɗauke daga kan maganar.

“Ammi” ta faɗa a hankali.

“Na’am umman sabir”

Rumaisa ta washe baki ta ce “Wayyo daɗi, ammi na ji daɗi, Allah ya amsa dukkanin buƙatinki, na fili da na ɓoye ya biya miki buƙatunki na alkhairi, na ji daɗi da ki ka kirani umman sabir”

“Amin rumaisa, in dai kin ji daɗi, ina son ki din ga saka baban sabir a addu’a, Allah ya biya masa buƙatunsa”.

“To ammi, ai saboda ke zan yi masa addu’a ba dan halinsa ba”

“Subhanallah, meye da halin nasa?”

“Ba ki ga yadda ya tsaneni ba? Hmm baki san halinsa ba ne”

Wani ƙarfin hali sai rumaisa, mace da ɗan ta, amma tana faɗin ba ta san halinsa ba ne.

Ammi ta ce “Rumaisa takawa mutumin kirki ne, fiye da yadda ki ke tunani, kawai mutum ne mara son hayaniya da shiga sabgar mutane”.

“To ni dai saboda ke zan yi masa addu’a kawai”

“Yauwwa rumaisa, maƙiya sun saka shi a gaba, wai cewa aka yi shi ya kashe aisha ya yi tsafi da gawarta, kuma sabir ba ɗan sa bane ba”

Ruma ta waro ido ta ce “Wai dama da gaske yasir yake, muna tafiya a hanya ya gaya mini, Innalillahi kam bala’i, to shi kuma yayi shiru” ta yi maganar tana ƙare masa kallo.

Sai kuma ta sake cewa “To shine yayi kuka da aka faɗi haka? Na ga kamar idonsa yayi ja?”.

“A’a ba kuka ya yi ba, addu’a dai zaki din ga yi masa”

Ruma ta ce “Taɓ, ammi kin san wani abu?”.

Ammi ta ce “A’a”.

“Nifa wallahi dan mutanen duniya sun tsaneni suna yi mini sharri, in dai Allah yana so na shikenan, kin ganni a unguwarmu ce mini ake ƙanwar maza, wai idan na yi tsokana yayyena suna tare mini, eh wataran suna tare mini, idan aka koma gida kuma su hukuntani, har gida aka je aka cewa mama wai bani da tarbiyya, tun da ƴan unguwarmu suka yi mini tambarin rashin ji na daina jin nauyin kowa. Idan na yi musu abun arziki ba a zuwa a gayawa mama ko yayyena, da na yi rashin ji, za su zo su faɗa. Ni kuwa tun da na gane haka na daina saurarawa kowa, idan na yi tsokana ta ko a zaneni, ko…..

Jin zancen nata ba kai ba gindi ya sanya yasir cewa “Bari mu tashi mu tafi”.

Ammi ta girgiza masa kai, ta ce “Baka ga hira muke yi ba, ina jinki umman sabir”

Ta sake gyara zama ta ce “Tun da na fuskanci ƴan unguwar nan ba sa yaba mini a kan abun arziki, ya sanya na zauna a kan kalmar rashin ji, idan aka ce na yi abu bana jin shakkar in ce na yi ko kasheni za ayi, idan ban yi ba komai za ayi mini ba zance na yi ba. Allah kaɗai nake tsoro shi ya halicceni kuma jin tsoronsa dole ne. Wallahi ammi a kan gaskiyata sai da a kasheni, kin san bala’in da na gani a hannun ‘yan bindiga kuwa? Hmmm ai wallahi idan nice shi, zan kalli duk wanda ya ce na kashe matata na ce na kasheta idan kana da alaƙa da ita ka nemi shaida ka kaini kotu.
Ba dai baba mai farin rawani ne baban Anty Aisha ba, kuma ya ce mini ya san baban sabir ba zai cutar da anty aisha ba, to wallahi sai na kalli uban kowa na ce masa na yi ɗin. Ai su yadda na fuskanci mutane, idan suka yi maka ƙage, ka yi ƙoƙarin kare kanka, to zasu yi ƙoƙarin su ga sun sake binciko wani laifin saboda zasu gane ka tsorata, yaya usy ya ce mini, na koyi rayuwa nikaɗai a lokacin da babu wanda zai taya ni ƙwatar ƴancina, sannan na fuskanci abun da yake bani tsoro, aikuwa na ɗauka, ai tunda na gane ƴan unguwa sun gane lagona su kai ƙarata gida mama tayi mini faɗa na fetsare, ka kai ƙarata gobe na yi maka abun ya fi na jiya, idan ka kawo ƙarata aka tambayeni na yi in ce eh, zaɓi ya rage a kasheni ko a barni da rai.
Wallahi ammi idan ya ce wa masu cewa ya kasheta yayi ɗin, ya gani idan za a cigaba da takura masa, duk wanda ya damu ya kai ƙara, ko kuma tun da ɗan sanda ne ya kamosu ya yanke musu hukunci, su faɗi yadda aka yi suka san kasheta ya yi, ko kuma ya kullesu ba rannan wata haka ta yi ba, wannan kwamishiniyar ba aka ce wani ya ɓata suna ba, aka kai su gidan yari, ko decoration of character ko me ake cewa oho dai”.

Duk da damuwar da adam yake ciki, sai da ya tattara hankalinsa yana sauraron rumaisa, duk da ba kallon in da take yake yi ba. Shi wasu lokutan har tsoro take bashi, ta wani fannin maganganunta a kan gaskiya suke, da maganar hankali da shirme haka take kwaɓa kayan ta.

Ammi ta ce “Waii, rumaisa an gaisheki, ban taɓa ganin yarinya irinki ba, ke kuwa ya ƴan bindiga suka iya zama da ke?”

Ruma ta yi murmushi ta ce “Haka suka zauna da ni, amma na ci ubana ba ƙarya ammi. Ni fa tun da ga kano aka ɗaukemu da ƴan bindiga, har kaza suka sai mini da na ce ina jin yunwa, suka nuna mini wata jaka, cike da bullet, har da bindigogi, shugabansu ne fa ya zo in da aka yi garkuwa da mu, ya sakeni ni da sabir, shi wanda ya sai mini kaza, ammi garin da na je, idan ka yi noma ba zaka taɓa ba sai ƴan bindiga sun yi maka izini, ni na je na ɗauki masara aka je aka gayawa mai gari, da nake a gidansa.

Da aka yi garkuwa da ni, baki ji abubuwan da suka faɗa a gabana ba, na ce idan na kuɓuta sai na faɗa suka ce kona faɗa a banza, la’ila ha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimin, na yi ta karanta musu, ba ƙaƙƙautawa sai Allah ya kawo mini anty aisha, daga baya kuma muka kuɓuta ni da sabir”

Ammi ta yi wata irin ajiyar zuciya ta ce “Amma abun da mamaki, wannan wane gari ne haka?”

Rumaisa ta ɗaga kai ta kalli adam, sannan ta ce “Na manta sunan garin”

Adam tambayoyi ne fal a ransa, amma girman kai ya hana ya tambayi rumaisa, gashi ammi ta fara taɓo abubuwa masu muhimmanci, amma rumaisan ta kauce taƙi magana.

Ruma ta yi wa sabir kiss, ta miƙawa ammi shi ta ce “Ammi, bari mu tafi, kar mu yi dare ba mu je gidansu Hauwwaliya ba”.

Ammi ta ce “To madalla, Allah ya tsare dan Allah ku gaida mamanku, ku jira bari na baku kuɗin mota”.

Ruma ta ce “A’a muna da kuɗi, na ga kaya na gode sosai da sosai, baba mai farin rawani ma, ya bani kaya har da kayan gara masu daɗi da zuma da nono, da kilishi na gode sosai”

Ammi ta takura ruma, ta basu dubu biyar suka tafi.

Bayan tafiyarsu ammi ta kalli takawa ta ce “Adam, dan Allah ne ka fuskanta game da yarinyar nan, ji yadda take magana kamar ana karanta mata?”

“Ni banga komai ba sai shirme da rashin nutsuwa a tare da ita”.

Ammi ta ce “No, maganganunta abun dubawa ne, a duk lokacin da duniya ta nemi juya maka baya, ka kama Allah ka nuna musu zaka iya rayuwa kai kaɗai, kar ka yi ƙoƙarin lallai sai an yadda da kai”

Ya numfasa ya ce “Ammi wannan shirmenta ne kawai na ƙuruciya, da rashin sanin ciwon kanta, yaushe ta zo duniyar balle ta san me duniyar ke ciki, tana tunani ne a iya ƴar ƙaramar duniyar ƙwaƙwalwarta, bari na tafi masallaci “.

Ammi ta ce “Shikenan Allah ya taimaka”.

Sai dai maganganun rumaisa suka cigaba sa shiga suna fita a cikin kwanyarsa, kamar maganganun ta na bisa turba.

Rumaisa sai da suka je gidansu Hauwwaliya, ƙafar Hauwwaliya ta yi kyau sosai, suka din ga murna da ganin rumaisa, ana yin sallar magariba, Yasir ya tasata a gaba suka tafi gida.
A hanya yasir ya yi ta yi wa rumaisa faɗa a kan tsinannen surutunta yayi yawa, ko a jikinta tun da muradinta ya cika.

Bayan sallar magariba, Adam da kansa ya je gidansu Jabir, ya tarar da shi da Jamil suna tare.
Jabir ya ce “Ka gama jan ajin ka neme ni kena?”

“Jan ajin me fa?”

“Ai ka fini sani, ka ce zamu haɗu amma na yi ta kiran wayoyinki ka ƙi ɗagawa”

Adam ya ce “Ba ƙin ɗagawa na yi ba, kaɗaici nake buƙata ne, abubuwa sun sha kaina da yawa”.

Jamil ya ce “Ai kai dama yanzu sai ana yi maka uzuri”

“Hmm baku ga abun da yake ta yawo a social media ba, game da mutuwar aisha? Wai yanzu rahoton cikin gidana shine labarin yaɗawa a media dan a ɓata mini suna”

Jamil ya ce “Ni kaina abun ya girgiza ni, na rasa yadda aka yi maganar nan ta fita a haka, tun ɗazu ni da Jabir abun da muke tattaunawa kenan, yadda za a shawo kan matsalar nan, amma ya kake gani, me ka shirya gayawa duniya domin wanke kanka?”

“Ba ni da isasshen lokacin da zan ɓata wurin ƙoƙarin wanke kaina a idon duniya, ina da abubuwan yi da yawa a gabana, kuma ba za a kawar da hankalina a kan abubuwan da na sanya a gaba ba, duk wanda yake ganin yana da wani ƙorafi, ko son tuhumata a kan mutuwar matata, idan yana da shaida ya kaini kotu” yayi maganar yana jin kamar za ayi masa kallon wawa abun da ya faɗa.

Jabir ya waro ido ya ce “Yanzu kana nufin haka zaka zuba ido a cigaba da ɓata maka suna?”

“Idan sun gaji zasu daina, idan kuma basu gaji ba zasu cigaba, idan na cigaba da ƙoƙarin wanke kaina, za su cigaba da ƙoƙarin kaini ƙasa, idan na tsaya a kan ƙafata na cigaba da karɓar duk abun da za’a ce kaina, wataran gaskiya zata yi halinta”

Jamil ya ce “Amma kana ganin hakan mafita ce adam? Duk abun da ya shafeka ya shafi masarautar garin nan ne fa kai tsaye”

Adam ya ce “In da nake godewa Allah kenan, atleast masarautar nan wani immunity ne a gareni”

Su da suka san Adam da saka abu a rai, da shiga damuwa sun yi mamakin yadda yau ya nuna halin ko in kula da wannan lamarin.

Jabir ya ce “To, bari mu ga zuwa yaushe wannan mafitar taka za ta kawo sauyi ga lamarin nan, amma a ganina kamar kasada ce hakan, Allah ya yi mana jagora”

Adam ya amsa da Amin, ya miƙe ya ce “Bari zan shiga gari na ga Bashir, gobe in Allah ya kaimu zai bar gari, ina da muhimman abubuwan da zamu tattauna”.

Jamil ma tashi yayi ya ce “bari nima na gangara gida, na gaida Alhaji, sannan na wuce gida sai sa safenku”.

Jabir ya ce “To Allah ya bamu alkhairi”

Kamar yadda Jamil ya faɗa, gida ya wuce ya je ha gaida mama da turaki, sannan yayi aniyar tafiya gidansa, Samha ce ta bi yo shi, tana kiran sunansa.
Ya tsaya yana jiran isowarta, ko sa ta ƙaraso, hannunsa ta ja ta ce “Mu je motarka mu yi magana” bai musa mata ba suka wuce motarsa, suka shiga.
Shiru ne ya ɗan ratsa, daga bisani ya ɗan numfasa ya ce “Ina jinki”

Ba tare da ta kalleshi ba ta ce “A duniya bayan mama bani da wani kamarka yaya jamil, mama ta kasa fahimta ta, ban sani ba ko kai zaka fahimceni, domin kuwa kaine dai-dai da zamanin da muke ciki”

Jamil ya ce “Haka ne, ina saurarenki”.

“Yaya jamil game da takawa ne”

Ya dubeta ya ce “Takawa again, me kuma ya faru?”.

“Maganar nan ce dai ta shekarun baya, tun da Aisha ta mutu ina son maye gurbinta, na so na je wurin baba da kaina, amma sai na ga rashin dacewar hakan, ka taimaka yaya kai kaɗai zaka fahimci halin da nake ciki”

“Wai ke samha ba zaki ƙyal adam ba kamar baki da zuciya? Duk cikin tarin samarinki babu wanda zaki fitar ki aura sai shi dai?”

Kamar ta fashe da kuka ta ce “Da zan iya cire shi daga zuciyata da tuni na yi, dan Allah ka taimakeni yaya jamil”

Jamil ya ɗan yi shiru sannan ya ce “Zan fara yi wa adam ɗin maganar na ji mai zace”

Da sauri ta ce ‘A’a dan Allah kar ka gaya masa yanzu, turaki zaka fara yi wa zancen”

“To amma kin san magana yanzu ba zata yiwu ba, tun da haryanzu ana cikin alhinin mutuwar nan”

“Ohhj God, to sai zuwa yaushe kenan?”

‘dole ki yi haƙuri, lokaci ya ɗan tura kaɗan”

“To shikenan na gode, ina saurarenka ka gaida gida ” ya jinjina mata kai, ita kuma ta buɗe motar ta fita, tana jin a jikinta kamar a wannan karon za ayi nasara.

Kamar wutar daji, haka Zancen mutuwar aisha, ya cigaba da zaga gidan jaridu, da kuma kafafen watsa labarai, yayin da ta ɓangarensa yaƙi cewa kowa komai, kuma yaƙi magana da kowane ɗan jarida.
A yau babu tsammani, mai girma turaki ya karɓi baƙuncin wambai da misalin ƙarfe tara na dare.
Turaki yayi mamakin ganin ɗan uwan nasa a wannan lokacin, amma ya ɓoye mamakinsa, ya karɓe shi.

Wambai ya ce “Na san zaka yi mamakin ganina a wannan lokaci, sai da ba komai ne ya kawoni ba, illa zuwa in sake tabattar da abun da kunnuwana suke jiye mini, kuma ka yi burus, ba ka ce da ni komai ba”

Cikin rashin fahimta, turaki ya ce “Meke nan kake nufi?”

“Maganar rasuwar ƴar wurinka aisha mana, ko kai ba ka jin jita-jitar da ke ta yawo a kan mutuwarta?”

Turaki yayi murmushi ya ce “Alhamdilillah, da kai da kanka ka ce jita-jita ne, nima haka nan na tsinci zancen”

“Turaki na zuwa na yi domin mu yi wasan barkwanci ba, gaskiyar lamari zaka sanar mini, gaba ɗaya mutuncin masarauta na nema ya zube, martaba da kimar gidanmu adam na ta cigaba da rusata sa shi da uwarsa, wannan wane irin abu ne?”

Turaki ya girgiza kai ya ce “Na san mai ɗakina ce ta je ta gaya maka wasu abubuwan, maganar da ke yawo a gari, tabbas aisha ta mutu a hannun ‘yan bindiga, amma ba adam ne sila ba, ko ya kasheta ya sha jininta ba kamar yadda maƙiya ke ta kwarmato, kuma yarinyar da aka tsaresu tare ta zo da yaron wurin aisha”.

“Turaki kana nufin goya masa baya wurin ɓoye laifinsa, dan me za a ce a ƙasar waje ta mutu a ɓoye gaskiya, wannan banzan aikin da yake yi na shishshigi ga manyan ƙasar nan da kawo ƙarshensu, ai gashi shi zasu kawo ƙarshensa, ko iya wannan labarin an yi mana mummunan tambari, a ce an samu babbar zuriya kamar ta mu da ƙarya. Dan haka dole a hukunta adam, sai ya yi wa duniya bayanin yadda matarsa ta mutu domin wanke ahalinmu daga mummunan zargin tsafi da kisan kai, ga uwa uba ayar tambaya a kan yaron da ake ce nasa ne, na baku awanni arba’in da takwas, idan har bai yi abun da na ce ba, matakin da zan ɗauka a kan sa ba zai yi muku daɗi ba.
Kai banda tsabar rashin sanin ciwon kai, kamar ba ƴarka ba wane irin abu ne haka?”

Turaki ya ce “Da Adam da A’isha, duk tsatso ɗaya ne, kuma ƴaƴanmu ne, dukkansu…..

Bai ƙarasa ba, wambai ya ɗaga masa hannu tare da faɗin. “Ba nasiha nake buƙata ko tunatarwa ba, martabar ahalinmu da sarautarmu nake ƙoƙarin karewa, dan haka ayi abun da muka umarta, ko a ga ba dai-dai ba”

Turaki yayi ajiyar zuciya, ya bi wambai da kallo, da ya tashi fuuuu ya fice.

Yayi ajiyar zuciya yana jin wani irin matsanancin tausayin Adam.

Duk wannan kumfar bakin da wambai yayi, ya biyo bayan ziga da kuma famfon da Mummy ta je har gida ta yi masa tare da taimakon hajiya sauda, shi kuma kamar kullum ya hau kai ya zauna ba tare da bincike ba.

Rumaisa har islamiyya ta koma, in da malamai da ɗalibai suka din ga yi mata barka da arziki na kuɓutowa daga hannun ƴan bindiga, sai dai a wannan karon ma, duk yadda ƴan bugun ciki, suka so ta basu labarin abun da ya faru da ita ƙi ta yi, wasu har suna cewa rumaisa ta koma saliha.
Bayan tashi daga islamiyya, ta wuce gidansu habiba, dan tun da ta dawo ba ta je gidan su habiba, suka rungume juna suna tsalle a tsakar gida.
Daga bisani suka zauna suka hau hira, mamansu habiba ta zubo musu ɗan wake, suka kewaye suna ci suna hira.

“Ruma ina yaya Aliyu ne?”

Ruma ta kalleta ta ce “Meyasa ki ke nemansa?”.

“A’a, tun a asibitin nan ban kuma ganinsa ba”

“To meye haɗinki da shi, to idan son sa ki ke yi, zaki dinga sai mini kayan daɗi kina bani”

Waro ido habiba ta yi ta ce “Astagfirullah, dan Allah ruma ki daina yi mini haka, baki san kirkin da ya yi mini ba lokacin da nake zuwa gidanku da ki ka ɓata, mai sunan baba yayi ta hararata, shi yake rarrshina ya dawo da ni gida”.

Ruma ta kwashe da dariya, ta ce “Allah sarki habibata, kamar ba nan muke kwasar dambe da ke ba, ke ni shawara zaki bani ma”

“Shawarar me” habiba ta yi maganar tana suɗe hannunta.

“Mutumin nan da ya ƙwace mini jaririna, wai ya zan yi da shi ne in karɓo ɗana?”

“Wai ƙwace jaririn suka yi gaba ɗaya to saboda me?”

“Saboda wulaƙanci mana, kullum da tunanin yaron nan nake kwana nake tashi, babarsa fa cewa ta yi ta bar mini shi, amma ya ƙwace mini shi. Habiba kin san in da kotu take? Ƙararsa zan je na kai, ba dama an ce zulai ta kai ƙara kotu alƙali ya bata ɗan ta ba, to nima kotu zan kai shi”.

Habiba ta ɗan yi shiru ta ce “Tsoro nake ji ruma, kin san ba a wasa a kotu”

“Na sani, ai ba wasa zamu je ba, ƙara zamu kai”.

Habiba ta ce “To, a unguwar su babanmu akwai kotu, dama za ayi sauka a gidan, sai ki zo mu je”.

Ruma ta yi murmushi ta ce”Amma na ji daɗi habiba, Allah ya kaimu in sha Allah sai an bani ɗa na, bari na tafi gida” ta miƙe suka fita tsakar gida suka wanke hannu, ta yi wa maman Habiba sallama sannan ta tafi gida.

Idan har da wanda za’a zarga a kan mutuwar aisha, to ba kowa bane ba face ni mahaifinta, domin ni na ɓoye ainihin abun da ya faru, adam ba matsafi ba ne, bai kashe aisha ba, kuma bai yi tsafi da gangar jikinta ba, a madadinsa, ina mai baiwa al’umma haƙuri na ɓoye haƙiƙanin gaskiyar abun da ya faru.

Mummy ta yi jifa da wayar hannun ta, bayan kammala karanta abun da turaki ya sanar da ƴan jarida, ya wanke adam.

Ayshercool.

Back to top button