Hausa NovelsMatar Makaho Hausa Novel

Matar Makaho 4

Sponsored Links

Page 4️⃣
Budurwa ce zata Kai kusan sa’ata cikin gadara da taunan cingum. tace amarsu ta ango karyawa ake ne? gashi nazo kallon dakin Amarya

***kala bance Mata ba

shema duk da baiji Dadin hakan ba Amma shuru yayi ba abinda yace ,haushi sosai naji Amma naja bakina nayi shuru don banda lokacin wannan Mai zubin karuwai, abinci muka cigaba da ciii ba Wanda ya kulata cikin mu biyun,

cikin bacin Rai tayi tsaki ta juya tafita. Koh ido ba mudu bane yasan kema ni ba sa’ar yinta bane kallo daya tamin ta gane ni ba kallan raini wayo bane Kamar yanda suka Saba Raina Masa,

**mamaki ne ya kamani, lallai sai nayi da gaske Zan iyya zama da Yan gidan nan. don dagani Basu da mutunci wallahi😒

Muna Gama karyawa ya mike ya dauki kwanukan da mukaci abinci harda nawa ha Hada ya fita dasu a kitchen ya Ajjye,

Dawowa cikin dakin Yayi cikin sanyin halinsa ya bude baki a Hankali ya furta Zan fita wajin sana’a Koh akwai abinda Zaki bukata,?

Kamar bazan tanka ba Amma na daure nace “babu”Koh zaka dawo kaci abincin Rana”? cikin natsuwa yace min ah..ah Zan saya naci sai yamma Zan dawo,

“har Ina ne wajen sana’ar taka” ? Cikin D’anjin Dadi jin Ina kulasa yace bakin titin kofar gida ta gefen shagonan, su haladu

** Ni Kuma Ina nasan wani Haladu bare shagonsa😏a Raina nake fada

Amma a zahiri cewa nayi “toh Inna Gama ka tura yaro yazo ya karba maka abincin”

da zumudi yace toh ……toh Zan turo bayan azahar. Ya sa Kai ya fita

***Daki na koma na bubbude akwatunan Kayana na bubbude kayan Ina jirawa a whtdp wasu a dressed mirror kayane na alfarma atamfufe dinkaku da Wanda ba dinkaku ba takalma da jakunKuna gyeleluka abaya material duka na shirya Kayana a nitse make-up kit na aje sa a drowarn mirror mayuka da turaruka na jirasu saman mirror. sauran kayan da suka rage na mai dasu cikin akwaiti ba wajen jirawa duk ya cika ba fili na rufe na Mai dasu saman whdrp “,

yarane suka fara shigowa ba sallama ba gaisuwa suka shigo mini daki harda Yan matan gidan suka cika dakin Wai sunzo kallon daki ga makwanta nata shigowa da sunan ganin daki Koh gulma ne oho, ana haka aka kawo NEPA Daya Daga cikin Yan matan ta Mike ta kunna TV

haka aka sake cika Wai ana kallo har baranda nidai abin daya isheni kawai na dauki wayata na fita waje,

” kitchen na wuce kazar jiya nake son hada miya dashi Amma kayan miyar jiya tayi kadan dole na shiga daki jakana na hannu mai kyau na dauka na fito waje budewa nayi na dau gudan dubu daya na aiki yaro a cikin Yan kallo kayan Miya Mai Dan yawa na Kara Masa da dubu biyu ya sayo harda kaza, don so nake na Kara na jiya bazai isaba ga yara a kofar.

Yaron na dawo mini da kayan Miya na fara aiki ba wance ta taimake ni Koh da jijjigen kayan Miya ne

shinkafa da miya na dafa Ina Gamawa na zuba a sabon kula Mai kyau na saka a basket da shukali da plt, na Koma dakin na bude freezer na dauki ruwan gora, na hada Masa a basket in na Ajiye, d’aid’ai yaron da Zai aika ya shigo na basa.

sauran abincin na zuba a babban faranti na hadawa yaran daban na sawa manyan daban daya ke nayi abincin da yawa sosai, Mika musu nayi ba kunya suka amsa gabaki daya Koh kwanukan Basu daga ba suka barsa a Inda suka ci sun batamin daki da datti sosai,

na ibi nawa na zauna a baranda kan darduma nayi Bismillah na fara ci ban tashi agunba saiga wani yaro ya shigo da sallama amsa Masa nayi, “waalaikumu salam”ya gaidani, “amsa wa nayi don naji dadin gaidani da yayi kaf yaran gidan da suka shigo ba Wanda ya gaidani Koh sallama babu,

Wai inji inji MAKAHO Mai mangoro aban abinci,

Wani Takaici ne ya kamani Wai sunan sama da MAKAHO ake kira “shap wallahih bazaiyu ba watoh nima haka za’a na kwatantani da MATAR MAKAHO Ina bazaiyu ba” duk Araina nake zancen nan.

Mikewa nayi na dauko masa basket in, basa nayi ya wuce

azahar yayi Amma kaf yaran gidan ba Wanda yayi Haraman Sallah Nima bance musu kome ba, na mike na dauro Alwala na koma dakin Hijab na dauka na fitoh waje nayi sallah na kwanta a sallayan Ina Danna waya,

Mutane Basu bar mini kofa ba har na Gama Tuwon dare na kwashe sukaci tukun suka fara watsewa daya bayan daya. Har suka watse suna fita na share dakina na goge, dakin Yayi kaca kaca sosai chanja zanin gado nayi yara sun kakama mini na jikin gadon da hannu yayi daud’a na fesa Turarukan daki na wanke dakalin kafun naji kofar yamin dama daman shekan iska Mai Dadi, wanka na shiga a gurguje nayi alwala na fada dakin na shirya nazo daukan turare Naga an min satan Mai Harda turare,

Raina ya kara baci don na tsani mutun ya dauki abuna ban basa ba, na kudurta Araina bazan sake Basu wannan fuskan ba tunda basuda mutunci gobe ba shegen da zai shigarmin kofa😂( tab kofarki Koh na makaho) Kaya nasa na jona wayata a cherge da laptop duka,

**na koma gefen gado na zauna

tunani na shiga yi lallai rayuwa ba tabbas yau Koh mutun daya daga cikin dangina Koh kawaye, babu Wanda yazo. watoh tunda talaka na aura kenan,?

alhalin duk wance tayi aure zuwa ake washe gari kallon gida da masu sallaman Amarya, a ranan. Amma ni ba Wanda yazo kallon daki ma bare sallama uhmm,

Karfe biyar da rabi MAKAHO ya dawo gida da kwandon abinci a hannu sai sandar jagoransa da lalube yakai kulan kitchen ya aje, wanka yayi ya fada dakin Yana shiga na fita na basa waje ya shirya,

Tana fita ya lalube Ghana must go insa ya dauki Kaya yasa ya fitoh waji lalube yayi ya dauki buta ya Kama alwala. ya wuce masallaci,don har an Tada sallah,

**lokacin Nima sallah na Tayar ,Bai dawo ba sai da ya hada da isha’i Tukun ya dawo,

*** abinci na zuba Masa
***na Koma Kan gado na zauna TV na kunna na kamo Tashar Arewa 24 Ana cikin Shirin kaddaran rayuwa. bayan ya Gama cin abincin, kwanukan ya dauka yakai kitchen hade da wanke hannu ya Sha ruwan Randa, ya shigo dakin,

cikin lalube ya lalubo kujira ya zauna a hankali cikin magana Mai sanyi yace nagode da abinci yayi Dadi sosai Allah ya biya.” Amin” nace hankalina nakan TV,

jawo laidar da ya shigo da ita baka yayi ya fitar da sabulu da omo. sai wata laidar mangoron yako, ya Miko mini ta inda yake tsammanin saitin nake,

Cikin sanyin jiki da zullumin zata Amsa kuwa?

Yace ga mangoro ba yawa

***ban gwatselesa ba na karba na mike naje na bude firij na aje.

fita waje yayi, ya hada kayansa daya jika a ban daki da safe da Wanda ya cire dazun ya wanke ya shanya ya sake dawowa dakin yayi cikin magana d’ari..d’ari yace Koh Zaki kawo kayanki Mai datti na wanke miki,

***cikin mamaki nake kallonsa Wai ya wanke mini Kaya, lallai da wani idon Zan basa Kayana na fada a Raina, Amma a zahiri nace “ah ah na gode Zan bada wanki inya taru” baice kome ba ya lalube kujira ya zauna kawai yayi shuru ya kurawa TV da yake aiki ido kamar Mai kallo,

***abin har yaso bani dariya Amma na maze. muna zaune har goma, bacci na faraji,
mikewa nayi na chanja kaya zuwa na bacci, kashe TV da glop nayi na Kara gudun fanka zuwa 3 Addu’a bacci nayi na shafa na kwanta,

a hankali ya Tashi yaje ya rufe kofar duk Ina jinsa dawowa yayi kwanta, kwanta a kujira addu’an bacci yayi shima ya shafa.

**Nima gyara kwanciya nayi,
Tun daga jiya zuwa yau, a Takure nake Sam ban Saba kwana da namiji a daki ba, Amma ya zanye, dole na kwanta tunda daki D’aya ne bare na koresa falo.

Misalin karfe biyu na dare ya farka………

My WhatsApp number
08084453785
[9/27, 4:10 PM] +234 806 983 1049: 🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀🍀
🧑‍🦯 *MATAR MAKAHO* 👨‍🦯 *
~ Na ~

🍃 *Rukayya Ibrahim* 🍃

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za’a ga mistake Koh typing error Amin afuwa 👌
Free book🤧

Back to top button