Hausa NovelsWaminal Hoob Hausa Novel

Waminal Hoob 6

Sponsored Links

Waminal Hoob_* 6…..

PAID BOOK
Free page.

_Asmy b Aliyu_

Murja ta hada mata ruwan wanka ta fito ta samu Nooriyah duk ta takure kanta waje daya,murmushi murja tayi tana fadin ki saki jikin ki Dan Allah.”daga kai kurum Nooriyah tayi ,na tayaki wanke kanki ko xaki iya??murja ta fada tana kallon Nooriyah, kitayani bana iya wanke kaina ni daya yana dayawa……tare suka nufi toilet dakyar Nooriyah ta rage kayan jikinta murja ta fiddo mata da sabon towel ta daura ,ganin yawan kan Nooriyah sai da yaso ya firgita murja tana mmki tana karawa duk wannan tulin gashin na mutum dayane,ba laifi bayada wani datti sosai sabida duk Karshen wata farhaan na bata kudin saloon tana shiga wajen wata makociyarsu inya mura tana wanke mata.rabi kawai suka kai murja taji ta gaji ,dakyar suka samu aka gama.murja na xufa tana fadin”kibarsa haka xanyiwa Hajia magana kawai akaiki kiyi saloon.
Wanka murja tabarta tanayi,tana fita batool ta shigo dauke da kaya cikin leda.”Aunty murja Ammah bakuwa tayine??”mekika gani Autar Ammah.”nagan Ku Anan dakin inhar Ammah ta sa aka kawo bako anan wajen to nasan special ne,ina bakuwar batool ta fada tana bin dakin da kallo.Amsar kayan Murja tayi tana fadin”tana wanka ko xaki jirata.noo xamu fita tareda Aysha waxeer idan na dawo anjima ma gaisa da haka batool tabar dakin da sauri,Alwallah Nooriyah ta dauro Dan ta lura ana gabda sallar xuhur,da taimakon Murja Nooriyah ta busar da kanta da drayer……ga kayanan ki saka inji Hajia bara naje na hado maki Abinci,da haka murja ta nufi kofa.Dan ajiyar xuciya Nooriyah ta sauke farhaan ya sasu a matsala,dakin ta shiga karewa kallo komai na cikin dakin blue black ne har pentin dakin.bbu komai acikin room din sai ltalyn bed da mirror dressing dinsa,sai kuma wardrob dinsa mai gida biyu,da kuma doguwar soofa itama kalar blue black…..dakin yyi matukar yin kyau,ledar da Murja ta ajey mata ta jawo xuwa gabanta tun Kafin ta buda ledar taji tana wani kamshi na musamman,buda ledar tayi ta fidda Turkish Abaya kalar brown,masu wasu irin duwatsu gaban rigar sai Dan karamin mayafin abayar.sai bran da pant suma sabbi dal da kuma ,agurguje ta shiga saka kayan.tana cikin saka kayan aka wani bugu kofar ,ido biyu tayi dashi wani irin ihu ta saki gamida xubewa akasa tana wani kare kirjinta ,shima da sauri ya juya har yana buga kansa ga kofa.wani irin bacin rai ya saukarwa Nooriyah shi wannan mutunen bayada hankali xaya shigowa mutane a haka.”kuma ai lokacin haduwarsu baiyi ba,da sauri ta rarumi hijab dinta ta saka.juyawa yyi yana wani hade rai,gamida shigowa cikin dakin duka.karki bada hanyar da Ammah xata gano bbu auren soyayya acikin auren mu,haka karki fadawa kowa yarda Auren nan yake.”kibarsa mu ukku kurum yarda muka tsarasa ,juyawa yyi ya nufi kofa batareda ya kara kallon inda taketa ba…….da kallo tabisa ,
Tsaki tayi ta cire hijab din gamida saka doguwar rigar tamkar Dan jikinta akayi rigar tayi kyau sosai acikin kayan.da sallama murja ta shigo dakin dauke da katon tray,mai dauke da cima kala-kala da sauri Nooriyyah ta karbi tray din tana yimata sannu.kallon ta Murja tayi tana fadin”kinga shigowar babana kuwa?da ido Nooriyah tabita Dan bata fahimci xancenta ba,Dan murmushi murja tayi tana fadin Aliyu nake nufi ya shigo .”Ya fadamin Bayaso Hajia tasan ya shigo,,ya shigo har ya tafi.Nooriyah ta fada tana komawa gefen gado ta xauna,ya kuma kin xauna sauko kici abinci.bara na baki waje ,xan dawo anjima murja ta fada tana barin dakin.samun kanta tayi da fadin”nagode Aunty……….murmushi kurum murja tayi gamida ficewa daga dakin duka,
Farar shinkafa ce da stew ,sai dayar cooler mai daukeda farfeson naman Rago,sai katon kwalin five alive.kadan taci abincin kasancewar ba mutum CE mai cin abinci sosai ba,tana idar da sallar axxahar barci ya dauketa akan carpet ba ita ta tashi farkawa ba sai kusan 5….Ahankali ta fara mika ta soma bude idonta tana karanto Addu’ar barci,ido biyu tayi dashi wani irin faduwar gaba ta tsinci kanta dashi,shima kusan hakane awajensa.baisan meyasa duk lokacin da suka hadu daita ba,xuciyarsa xata fara bugawa .baxata daina ba har sai lokacin da yabar wurinta,wani irin irritating look yake watsa mata fuska a daure yake fadin kin watse baki kina barci ,kinji sanyi A/c an samu banxa na baki minti biyar ki shirya farhaan na nemanki .”Ya fada yana bar mata dakin cikin takunsa na kasaita haushi da takaici suka cika xuciyarta lokaci daya,tambayar kanta take tsawon Mintuna nawa yayi yana kallonta ,tsaki tayi ta tsani ganin wannan fuskar tashi mai kama da kosai,haka kurum taji jikinta duka na kamshin turarensa,da dakin ma gaba daya.toilet ta shige ta dauro alwallar la’asar ,
Sai da tayi sallarta cikin natsuwa,tana linka sallayar murja ta turo kofar da sallama.Babana yana ta jirafa .”hijab dinta take kokarin sakawa kalar Ash colour Wanda ya Dan fara tsufa ,da sauri Murja ta karaso gabanta tana fadin”ki Dora mayafin Asama mana,ina ganin xaifi kyau………..wani iri Nooriyah taji aranta karo na farko da xata tsaya a haka gaban mutane ,ko acikin gidan kawu kullum tana sanye da hijab ko barci xatayi.
Da sauri tabi bayan murja,ta godewa Allah da ya kawota da batasan hanyar da xatabi ta koma wurin Ammah ba.
A falon Ammah suka samu Aliyu tsaye yana kaida kawo ,Ammah na xaune cikin soofas.da sauri Aliyu ya karaso gabanta yana fadin”kin kyauta shine kika shanya Aliyu waxeer har haka???”Ya fada sounding so cwt yana yimata wani irin kallo,dauke kai tayi ta isa gaban Ammah ta durkusa tana gaisheda Ammah.da murmushi Ammah ke fadin kin tashi barci jewel?”sannu da tashi ,cike da jin kunya Nooriyah ta daga kai.
Aliyu yana son magana dake kina da lokaci ko sai gobe.”cike da takaici Aliyu waxeer ke kallon Ammah.jira yake yaji me Nooriyah din xata fada sai yaji tayi shuru tana wasa da yatsun hannunta,Aliyu kuje karka wahalar daita da yawa.Rabin awa na baka ka dawomin da ya’ta .”Ammah ta fada tana barin su A falo.wani bacin rai ya sauka a xuciyar Aliyu waxeer me Ammah ke nufi??”me ma xai kaisa yawo da wannan bakar Yarinyyar………tare suka jera suka fice daga cikin parlon suna fita ya nufi part dinsa ita kawai binsa take xuciyarta na bugawa ,batasan meyasa duk lokacin da ta hadu da Aliyu waxeer ba ,xuciyanta tana hanata hutawa daga bugawa.aduk lokacin da suka hadu itada Aliyu waxeer ,batasan meyasa ba.ko farhaan da suke soyayyah batajin bugawar xuciyarta idan suka hadu,sauran kadan tasha kasa wajen kallon haduwar parlon Aliyu waxeer ,idan baxatayi karyaba wannan parlon har yafi na mahaifiyarsa kyau da tsaruwa sai kace akasar turai Dan kyau ,komai na cikin parlon Fari ne Sol”har ta da fentin parlon Fari ne wato Fari shi daine Fav din Aliyu waxeer. Farhaan ne yayi saurin tarota a hannunsa,wara ido tayi tana kallon farhaan shagari cikin kananun kayan da sukayi matuqar karbarsa,
Da sauri Aliyu ya juya xuciyarsa na tsananin bugawa bai kara koda second 1 a wurin ba ya nufi hanyar stair’s da ido farhaan yabisa yana sakin murmushi……Da sauri Nooriyah ta kwace kanta a hannun farhaan ,harde hannunsa yyi akan kirji yana binta da wani sanyayen kallo.
Shigen ba karamin kyau yyi mata ba,lumshe ido yyi ya kara budewa akanta.ta Dan turo baki tana fadin baka fadamin xaka xoba.ko awaya.”nima Ramawa nayi na shanyaka ,meyasa xaka aikosa kasan bayada kirki.”ta karasa maganar tana wani hade rai ,hade hannu yyi alamar yana Neman Afuwa xama sukayi acikin fararen soofas din da suka kayata parlon na Aliyu,ya dafe kansa dake yimasa ciwo tun Daren jia sabida maminsa tayi Rantsuwa ayau xaibar kasar nan .”Ba haka yaso ba sai yaga Auren Noory dinsa da Aliyu ya tabbata ,jirgin karfe 6 xanbi xuwa cyprus……. Wani mummunan faduwa gabanta yyi har hawaye sun cika idonta cikin rawar murya take fadin”Baxa ka bari sai an daura auren ba??”ta fada hawaye na sauka a fuskarta ,kuka kuma noory??”bafa mutuwa zanyi ba,xan dawo nan da watanni shidda Kafin mu idar da gamawa gabaki daya,ina jin tsoron duniar nan Farhaan .shigowarka cikin Rayuwata Alkhairi ne Farhaan ina addu’a Allah yasa wannan Auren kar yaxamo silar tarwatsa farin cikin mu,ina sonka farhaan!!”Dan Allah karka manta dani ko na sakan dayane cikin rayuwarka,
“Waye kika taba ganin ya manta da xuciyarsa kin manta ke xuciya ta CE gabaki dayanta ,ki kwantar da hankalin ki bbu abunda xai faru ,kuma ae xamu rika waya wannan karon harda vedio Call .xaki rika ganina nima na ganki…….”haka Farhaan yyi xaune sunata hira,
Ga Aliyu yaki fitowa shi xai saukesa a airport ,
Acan kuma bangaren Aliyu waxeer wanka ya shige yana sakarwa kansa shower,wani irin numfashi yake saukewa xuciyarsa na bugawa da karfi tamkar xatabar kirjinsa ,da ya runtse idonsa Nooriyah yake hangowa tana sakarwa farhaan sanyayyen murmushi baisan meyasa hakan ke hurting dinsa ba,meke damunka ne da lamarin Yarinyyar nan Aliyu waxeer??? Xuciyarsa ta fada masa tsaki yaja a karo na farko yana basar da tunanin Nooriyah aransa,koda ya gama wanka ransa a bace yake,agurguje ya shirya cikin blue din jeans,da farar shirt mai dogon hannu sosai yyi kyau acikin shigen ,turarukkansa ya saka masu tsadar gaske,
Agaban mirror dressing ya tsaya yana gyara sumar kansa tamkar ta macce wadda ta taru sosai akansa,wani irin faduwa gabanta ya shigayi da sauri da sauri kamshin turarensa ya sanar mata da xuwansa,Kafin takunsa ya fara ansa amo acikin kunnuwanta,Runtse ido tayi gagam tamkar mai Asmaa ta rika Jan numfashi tana dafe da xuciyarta dake tsananin bugawa ,da sauri farhaan ke tambayarta lfy???dai-dai isowar Aliyu waxeer cikin parlon bude ido tayi suka sauka cikin nasa,
Da sauri ya jaye nasa idon ya wani hade rai.
Ya maida idonsa cikin na farhaan yake fadin”baka duba tym ne besty.?mikewa yyi hannunsa xube cikin aljihun wandonsa ,yana bin Nooriyah da wani irin kallo itama kallonsa take idonta na cika da hawaye.mika mata hannun sa na dama yyi Ahankali ta samu kanta da Dora hannunta cikin nasa,lokaci daya Aliyu yabi hannayen da kallo xuciyarsa na bugawa.,,mikar daita yyi tsaye gamida jawota jikinsa duka abunda baitaba yiba,tun haduwarsu.suna hada ido da Aliyu gabanta yyi wani irin faduwa ganin yarda idonsa ya koma mata kalar red,dauke kanta tayi ta mayar kan farhaan .Hannayensa yasa ya rike kugunta ,cikin tsawa Aliyu waxeer ke fadin”meye Haka farhaan???”shi kansa baisan meyake fada ba ,baisan lokacin da maganar ya fito ba.da sauri farhaan ya saki Nooriyah yana shafa kansa yake kallon Aliyu da wani irin yanayi………….Idan Ammah ko wani ya gani fa??shirin mu xai wargaje duka.Ka sallameta pls mutafi,Aliyu ya fada yana barin wajen.dafe da kirjinsa dake Neman tarwatsewa ,Ahankali farhaan ya rika daga mata hannu .hawaye taji suna cika idonta, xubewa tayi daya daga cikin soofas din parlon Aliyu.sosai hawaye ke gudu akan fuskarta,A mota ma Aliyu kin kula farhaan yyi baisan meyasa yake jin haushinsa ba.murmushi Farhaan yyi yana riko hannunsa yake fadin fushi kayi ne besty?”
Nan ma Aliyu yaki kulasa har lokacin yaki saukowa,koda suka isa a air port akwai sauran mintuna xaman su sukayi a mota farhaan na Dan Jan Aliyu da hira kafin a fara kiran sunaye,,
Da an daura aure wani satin xan koma London ,,da sauri farhaan Ya kallesa yana fadin da wuri har haka???toh ya xakayi da nooriyah wani kallo Aliyu yayiwa farhaan yana fadin”tare aka haifemu da xata riqa bina duk inda na shiga bakin aikina xan koma ,ga kuma wasu kudi da suka bata a companyn waxeer dake kasar London ga kuma aikina.”Yana aiki da airport din (LHR)London Heathrow airport, duk da yanzu wani Dan siyasa dake kasar ta London ,ya dauki Aliyu waxeer aiki a karka shin sa.abunda yasa ya Dan kwana biyu a Nigeria shima baya kasar Yana kasar Indian,
Ajiyar zuciya farhaan ya sauke ,xaiyi magana Aliyu ya daga masa hannu yana fadin”xamuyi magana besty,kusan tare suka fito daga motar side hug farhaan yabasa,
Daga kai Aliyu yyi yana fadin”ka kula da kanka……..sai da yaga shigar Farhaan acikin jirgi shima ya juya ya nufi motarsa.cikin gari ya shiga bai dawo gida ba sai bayan magrib ,da mmki yake kallon compaund dinsu ganin motar mum dinsu farhaan,mmki yake Mai ya kawota gidan su a irin wannan tym din.”Jin yyi xuciyarsa na tsalle bai gama dawowa normal ba ,sai ga Kiran Ammah ya shigo a wayarsa.dagawa yyi batareda yayi magana ba ,kana ina??”Yaji Ammah ta fada tamkar yace mata baya gida sai yaji baxai iyaba.ka shigo ga hajia Maryam ta shigo da haka Ammah ta kashe wayar ,cikin takunsa na kasaita ya shiga parlorn Ammah dauke da sallama a bakinsa,da fara’a Mami ta amsa tana fadin”Aliyu yaushe ka xama surikina ban sani ba.”Dan sosa Kai yyi ya xube agaban Mami yana gaisheta da ladabi Mami ta amsa tana fadin”nayi fushi Aliyu wannan satin ake daura maka Aure ko ka sanar Dani,ko a bakin farhaan banji xancen Auren kaba…….
Mami ta karasa xancen tana kallonsa,Dan shafa kansa yyi gabansa na faduwa yake fadin”Am sowiee mami Auren ne yaxo a haka,da mamaki Mami ke fadin”Amma wacece wannan Mai sa’ar haka ??Ammah ta fadamin bada Areefa Mansoor ba.dan shafa sumar kansa yyi yana murmushi batareda yace komai ba,wayarsa ce ta fara ring wani irin ajiyar xuciya ya sauke ko wanene ya cecesa daga tambayoyin Mami,da sauri ya Mike ya nufi hanyar barin parlorn nan Mami ta juya suna magana da Ammah akan yarda xaa gudanar da bikin Aliyu,kasancewar Mami da Ammah kawayene tun su Aliyu na kanana ,Wanda sanadiyar yaransu Allah ya hada jinin su.
Shifa yace baxaayi wani taro ba kawai a daura aure akawo masa Amaryarsa.”da mamaki Mami ke. fadin shine Kuma xaki biyewa shirmen Aliyu.”shi yaji xai iya Ammah ta fada tana basar da hirar gamida dauko wata hirar,
Washe gari Khaleel waxeer ya iso shida Mai dakinsa laylah waxeer part din Ammah aka tarbesu ,cike da damuwa Ammah ke bin laylah din da ido ,ganin shekara kusan 3 har yanxu Layla din Koda batan wata Bata tabayi ba,sosai Ammah ta damu akan hakan,Haka Yan uwanta suna Maganar rashin haihuwar matar Khalil din,Bayan sun kammala cin Abincin.Ammah ta Kira murja tana fadin taje ta sauko da Nooriyah xata gaisa dasu Khalil da mamaki Laylah ke fadin har iyayen nata sun kawota kenan Ammah.”da murmushi Ammah take fadin Nina bukaci hakan me yayi saura jibi xaa su shiga lalle,kusan minti goma sai ga Nooriyyah tana saukowa akan stairs itada murja wacce ke take mata baya,tana cikin shigar doguwar rigar atamfa kalar red and yellow wacce tayi matukar dacewa da kalar fatan jikinta,sai wani irin sheki take acikin kayan sai babban mayafi Wanda ta axa akan kafadarta,
Babu kwaliyya a fuskarta ,duka xuba mata ido sukayi daga Khalil waxeer har matarsa Laylah baki bude duka suke kallonta,ganinta bakar fata dukansu tunani daya suke yaushe Aliyu waxeer ya sauya tunaninsa akan bakar fata.?””xubewa tayi akan carpet tana gaishesu cikin sanyi muryarta, Layla ce ta amsa cike da tambayoyi a bakinta ,
Da murmushi Ammah ke fadin tashi ki xauna cikin su Nooriyah Yan uwanki ne……..da murmushi Laylah ke fadin Amaryar mu gaskiyya kina da sa’a da kika samu Aliyu waxeer a matsayin mijin Aure ina maki fatan Alkhairi acikin Rayuwar Aurenku.”murmushi kurum Nooriyah tayi batareda tace komai ba, Khalil ne ya Mike yana fadawa Ammah xasu wuce part dinsu suyi wanka.a fito lafia
Abinci dare na jiranku karfe takwas na dare”.mun gode Ammah Allah ya kara nisan kwana ya fada yana kallon laylah ,kusan tare suka fice daga part din na Ammah,tamkar jira laylah keyi su fito ta kalli Khalil da sauri tana fadin”Wai da gaske leel Aliyu ne xai auri wannan Yar kauyen??”ko kadan Bata dace da taxama matar Aliyu waxeer ba wlhi.”Laylah ta fada tana dakune fuska,Wai taya ma xaayi Aliyu yaso bakar macce??”Khalil ya dage kafada yana ware mata ido yake fadin”Waike me ya dameki kiyi Abunda ya dameki plz ya fada cikin Dan daga murya,shuru Layla tayi tana bin Khalil din da ido…..kamar yarda Ammah ta fada bayan ishai sai ga Khalil waxeer shida Aliyu sai Kuma Layla dake bayan su taci ado cikin wani tsadadden less Wanda yayi mugun karbarta ,dama laylah badai gayu ba.tayi simple make up Wanda ya Kara fitowa da Asalin farinta dama farace sosai,da fara’a Ammah ta tarbesu,.wannan karon Ammah Bata tura murja xuwa ta taho mata da Nooriyah ba Aliyu ta kalla ta fada masa yaje yaxo da Nooriyah xasuci Abincin dare tare ,shaye da toka Aliyu ke fadin Ammah plz…wani kallo da Ammah tayi masa yasa ya Mike da sauri ya nufi part din da Nooriyah din take,da ido laylah tabisa.tsaye yyi ajikin kofar yana sauke ajiyar xuciya baisan meyasa duk lokacin da xai kusanceta ba yake jin bugun xuciyarsa na karuwa,yafi minti biyu tsaye a kofar dakin kafin yayi knocking ,gamida tura kofar .gefen bed ya sameta ta buga uban ta gumi sanye take da hijab,tsaki yaja aransa .tana cikin daki Kuma sai ta saka hijab sabida kauyanci,gyaran murya yyi ta dago dara-daran idanunta ta xuba cikin nasa,yana wani daure fuska yake fadin,kixo Ammah na nemanki.”Ya fada yana nufar kofa har yakai kofa ya juyo da sauri yana fadin Kuma ki cire wannan hijab din,Yar kauye kawai…..”Ya karasa maganar fuska bbu walwala da mamaki take kallonsa,saka hijab din shine kauyanci,ki fito yanxu malama kina Bata mana lokaci ya fada da Dan daga murya.mikewa tayi tsaye ta nufi kofa sanye da hijab dinta baki ya bude yana kallonta…..

 

Back to top button