Hausa NovelsWaminal Hoob Hausa Novel

Waminal Hoob 2

Sponsored Links

_Asmy b Aliyu_

Areefa!!”Ya fada yana sauke numfashi ,kara damke hannunsa Farhaan yayi ,Aliyu na girgixa kai yake fadin “nasan Yarda Rayuwa take xo muna ne Farhaan,A tare take tabamu a tare muke Raba duk wata kaddara da xata samu dayan mu”……..Banda wannan besty ban dashi karka bari na dauki abunda baxan iya karasawa ba Dan Allah.”Aliyu ya karasa maganar cikin karaya,Hawaye suka cika idon Farhaan lokaci daya.idan ban samu Noor ba zan iya mutuwa besty.”ya fada yana sauke numfashi ,nasan Areefa mansoor xata iya kisan kai akan ka ,zamu taru duka mu fada mata gaskiyya,bana son wani Abu ya samu Noor dita.”
Kansa ya Dora kan sitarin motar yana sauke numfashi gaba daya Farhaan din ya gama dauresa,ya tsani ganinsa cikin damuwa.tun suna yara haka suke tare suke Raba damuwarsu,yana dago kansa yaga Farhaan ya xuba masa ido,shaye da toka Aliyu ke fadin kan wannan Noor din xaka bi ka wani daga hankalin ka.”bana son wannan Noor din taka,gata yar baka.”Aliyu waxeer ya fada yana sakin daria,
Wanda yayi ne Dan Farhaan din ya sake……duka Farhaan ya shiga kai masa yana fadin bana son wulakanci dama nasan Nooryna batayi maka ba ae.”ko bayan Aurenku ban yarda ka wulakan tamin baby ba.tada motar yayi sukabar wurin……

???
Cikin sanyi ta take nufar motar Farhaan, kureta da ido Aliyu yayi. ya tsani koda cin karo da bakar fuskarta ne , da ya yarda ya kalleta gabansa ke faduwa,saboda bakin ta.irin yaran nane da baxasu wuce cwt 16 ba,kuka kikayi ko Noor?””Farhaan ya fada yana kafeta da idonsa,lokaci daya kuma yake karantar yanayin ta.
Ahankali ta shiga girgixa masa kai haka tana wasa da dogayen yatsun hannayenta,
Gefe Aliyu ya koma ya xuba masu ido,kare mata kallo yake daga sama har kasa,ko kadan bbu wata wayewa a tattare daita sai tarin kauyanci da gidadanci ,gaskiyyar Mami ne,Asiri!””ya fada yana hade rai,
Yes Asiri akayiwa Farhaan dinsa,idan ba Asiri ba taya xai so wannan bakar kuma yar tallakawa likis.!”………Jin yayi Ahankali Ransa na baci ,xuciyarsa na narkewa.sai da Farhaan ya Dan tabosa ,meyasa kake haka Besty ina jin Noor na gaisheka kaki ka amsa ko fuska kaki ka sakar mata,haka xakuyi xaman Auren.”kana iya hango wani yanayi acikin kwayar idon Aliyu,da alamar shi kuma Farhaan kallon da Aliyun keyiwa Noor yana tabasa….kallon kyama da tsana,
“Besty xo muje nayiwa Noor bayani agabanka ya fada yana Jan hannun Aliyun batareda ya yarda sun hada ido ba,
Hawaye na xubar mata take girgixawa Farhaan kai,cikin sanyin murya da gigita take fadin baxan iyaba Farhaan.”baxan iya wannan Auren ba,wannan wane irin Aure ne?ta fada tana jin wani irin ciwo aranta,
Ni baxan aure sa ba kawai mu hakura Farhaan,wannan itace kaddarar mu baxan iya auren Aliyu waxeer ba.”Yafi karfina ta kowane fanni na Rayuwa,
A fusace taji an fisgota tamkar Ya riko takarda haka yake jinta a hannusa,hannu yasa xai xabga mata mari yaji an rike hannun,
Afusace ya turata yana huci tamkar zuciyarsa xata fito sabida bakin ciki,
Farhaan ne yayi saurin tarota da tasha kasa.
A fusace ya juya ya nufi Mota ,ya mata key anan yabar wurin da wani irin speed yana badesu da kurar wajen,Ahankali Noor ta kwace kanta daga rikon da Farhaan din yay mata nan ta xube a kasa tana sakin marayan kuka,hannu ya saka yana squeezing sumar kansa,cike da bacin rai yake fadin”laifinki ne Noor meyasa xakiyi Rejecting dinsa haka,
Kin San ma waye Aliyu??
Baki San taya ma na lallabasa ya yarda xai aureki ba .”saboda ya tsaneni haka bana da gata kou.”Ta fada still hawaye na xubar mata,
Auren Ku na Dan wani lokaci ne sabida kawu nayi haka,sabida kar ya Aura maki kabeer nayi haka,kinfi son ki auri kabeer ki xauna da shi fiye da bestyna?”Ya fada a tsawace,bata taba ganin Farhaan haka ba.tsawon haduwarsu na shekara daya,
Motar kawunta taga tana tahowa ,ta masu jigilar xuwa garuruwa……da gudu ta nufi hanyar gida ,A fusace Farhaan ke kallon motar ,kallo-kallo suka tsaya yi shida kawu balele dake maxurai.
Koda minti daya bai kara wajen ba ya taka xuwa bakin titi da kafa……..tunanin sa daya ta yarda xai kara shawo kan Aliyu xaiyi wuya ya kara sauraren sa,
??
Yarda ya wani shigo falon a hargitse ,yasa Ammah da batool da suke xaune a falon suka bisa da kallo lokaci daya.kai tsaye kitchen ya nufa sai gashi dauke da bottle water a hannunsa,cikin kyawawan kujorun da suka kawata falon kalar maroon yayiwa kansa masauki ,kafa kai yayi sai da yaji babu komai ya dire kwalbar,har yau mahaifiyarsa kallonsa take tana mamakin yanayinsa……..hannu yasa cikin sumar kansa mai kama da ta labarabawa yana hargitsata ,kasa daurewa Amma tayi tana fadin”kai lafian ka??
Kurawa mahaifiyarsa ido yayi na Dan wani lokaci ,
Aliyu bana son iskanci!!”
Ya mutse fuska yayi yana fadin babu komai Ammah na gajine,
Dan ka gaji shine xaka shigomin falo a haka.”
Tashi kabarmin falo,ammah ta fada tana Dan daka masa tsawa,.
Babu musu ya mike yabar falon Dan yasan sarai Ammah bata daukar raini ,akwai yar tafia daga part dinsa xuwa na Amma.hango motar Areefa mansoor yayi tana parking yayi mamakin ganinta yanxu,
Kananan kayane ajikinta Wanda sun Dan kamata,sai Dan karamin veil da tayi Rolling kanta dashi,tun kafin ta karaso yakejin mayen kamshinta,
Tana karasowa ya shiga dube-dube kar batool ta gansu,yana daure face yake fadin meyasa bakyaji Areefa??Dan bude ido tayi tana fadin “me kuma nayi ,kin San Ammah bata son wannan shigar meyasa kikayi?”ya fada da xafin rai,dage kafada tayi tana fadin kai nakeso kuma irin shigar da kakeso kenan,ae Ammah bata da Matsala tana son Abunda kake so.”ni kuma manyyan kaya suna takurani ae kasan da haka.” Ta fada cike da Rashin damuwa a fuskarta,
Shigewar sa falo yayi ya barta nan tsaye yana gafda shiga master bedroom dinsa ta cimmasa,rike kofa yayi yana kallonta.
“Kije gida gobe xan shigo……..kullum haka kake fada,ni baxan iya bari har gobe ba.” Ta fada da damuwa a fuskarta,
OK ranar da kika shirya ki kikirani naxo banda yau bana son hayani ya fada yana buga kofar a fuskarta….

PAID BOOK
ASMY#??

Haske Writer’s Association.. #

Back to top button