Hausa NovelsWaminal Hoob Hausa Novel

Waminal Hoob 30

Sponsored Links

Asmy Mom Aydah??: 30

Basuyi minti goma gidan makoki ba suka fito,sabida ko sun tsaya babu wanda ya sansu,sun dauki hanyar wajen gari Areefa wacce itake driving ta kalli Aunty Siddiqa tana fadin”shi malamin naki ya rasa inda xaiyi gida sai a karshen gari,gaskiyya wannan da sake,barazana ne ga rayuwar mu to idan aka sankame mu a hanya fa.”wai Aunty Siddiqa haka kike dauriya kina xuwa har Nan tun daga unguwarku??gaskiyya na jinjina maki,kinyi kokari haka hakurinki yayi maki Rana,tunda shegen mijinki yanxu ya daina bin matan waje,an riga an kame maki Abar sai yarda kika yi daita.Areefa ta fada tana sakin dariar shakiyan ci.”wanda dole sai da Siddiqa ta saki mumurshi,sunyi sa’a sun samesa sai dai akwai layi……..Baki Areefa mansoor ta bude tana kallon manyyan motocin da sukayi parking a kofar gidan da bai wuce daki biyu ba aciki,manyyan hajiyoyi taga suna shiga suna fita.da sauri ta kalli Siddiqa aunty Siddiqa duk wannan manyyan hajiyoyin da nake gani wurinsa suka zo?tayi maganar sounding so very confused.”kadan ma kika gani in dai akan aekin malam mai bushasha ne,baya ma harka da kananan mutane,yafi son manyyan hajiyoyi masu kaisa aekin Hajji da umra,auhhh dama zai iya zuwa aekin Hajji kuma yana xuba wannan shirkar,shegen kudi ne dashi har manyyan motoci yana da,to meye Amfanin haka yana zaune cikin irin wannan matsiyaci gidan.”Siddiqa ta tabe Baki tana fadin”Ni dai mu shiga kar ayi mana cin layi.da haka suka kutsa kansu cikin gidan,kallonsa kurum Areefa keyi tsoho ne Sosae sai shegen gemun da ya kusa sauka har a kirjinsa fari sol.”wata big hajia taga ta aje masa jikar kudi,ya girgixa kudin yana fadin miliyan biyu ne aciki hajia,idan aeki yayi zaki dawo ki cika sauran ladarsa,hajiar ta russuna a gabansa tana famar xuba masa godia,jiki sanyaye Areefa mansoor taja Siddiqa gefen tana fadin”naji yana fadin manyyan kudi aunty Siddiqa nida iyakar kudina baifi dubu dari ukku ba,ki kwantar da hankalin ki,da haka tajasa gaban malam mai bushasha,ya kalli Siddiqa yana fadin.”wannan itace kanwar taki??cikin girmamawa take fada masa itace,ya kalli Areefa yana fadin”ta basa hannunta na dama,da sauri ta mika masa hannun ya dade yana kallon hannun,
Kafin ya Runtse ido ya shiga jan tasbahar hannunsa,yafi minti biyar a haka kafin ya bude,yana fadin mekike bukata?”da sauri Areefa ke fadin”dama ina son na shiga familyn waxeer ne,kuma inada ciki so nake duka familyn su yarda da Aliyu yayi cikin,haka ina so na xauna cikin su har lokacin da xan haihu ,ina son na juya yaron da uwarsa,haka ina son a dauki son dunia a ?orawa cikin jikina musamman uwarsa,ina so Aliyu ya rinka bin duk wani umurnina…….”kallonta malam mai bushasha ya tsaya yanayi kafin ya Runtse idonsa ya shiga jan doguwar casbahar sa wacce batayi kama da ta sallah ba ko kadan,dan tashi tana dauke da karafuna a cikinta ,ya shiga ambaton wasu kalaman tsafi ya bude idonsa yana kallon Areefa mansoor yace ladan aekin miliyan daya da dubu dari biyar,ta xare ido tana kallon Siddiqa mansoor xatayi magana Siddiqa ta rigata tana fadin toh Malam xamuje mu hada kudin nan da kwana biyu xamu dawo,daga kai yayi alamar ya gamsu.suna fitowa ta kalli Siddiqa mansoor hankali tashe take fadin”kin haukace ne Aunty Siddiqa Ina xan samu wannan kudaden yanxu??”Ni dai na fasa gaskiyya ,
Baxan iya wannan hasarar ba,xanje kawai na fadawa Ammah.nasan baxata goyi bayan zalunci ba.”Siddiqa ta fashe da daria tana fadin”Ashe kuwa xaki rasa sa,wannan karon Siddiqa mansoor ce mai tukin,tana fadin”ban san baki da hankali ba sae yau Areefa kina tunanin kinga sirrinsa kuma kice kin fasa aeki dashi baxai ma yuyu ba,kibari xanyi magana da Ahmad ko aron1 miliyan zamu samu a wajen sa ,bakin ce kina da dubu dari ukku a hannunki ba,ba’a rasa dari biyu a hannun na ba sai a hada ba.ta gama da matsalar Aliyu sauran Sufyan mansoor da Abbanta,tasan taurin ran Sufyan mansoor xai iya kashe Aliyu waxeer idan yaji akwai cikin Aliyu waxeer a tare daita,hanyar tsayar dashi kawai xata nema.har suka kai gida ta rasa madafa,har Farhaan ya cika kwanakki ukku da rasuwa kullum su Ammah na zuwa gidan gaisuwa basa dawowa Sai da magrib haka sun samu zuwa ganin mami A asibiti itama Alhmdullh tana karbar sauqi a wajen Allah .sai dai har yanxu bata magana sai dai ta rika bin kowa da kallo ,sai kuma hawayen da basa gajia da sauka a kan fuskarta,ranar da Nooriyah taga mami a matsayin mahaifiyar Farhaan Shagari wandda Farhaan din gaba dayan sa mami ne,mutuwar Farhaan ya dawo mata sabo ,mota ta koma da gudu.ta shiga rera sabon kuka.cikin kwana biyu suka gama hada kudin suka damkawa malam mai bushasha yana kara tabbatarwa da Areefa mansoor bbu ita babu da nasanin aeki tare dashi,wani bakin kwaliyya ya bata yace kartayi wasa dashi duk ranar da ta shirya shiga familyn waxeer kai tsaye xata shiga ta tabbata ta shafa kwallin nan acikin idanunta,Haka duk bayan kwana bakwai zata rika shafasa, karta yi kuskuren ketare ranar shafasa,
Damke kwallin tayi a hannunta tana yimasa godia,tun kafin su shiga mota ta wani rungume Siddiqa mansoor tana fadin”ina farin ciki ina farin ciki.”Aunty Siddiqa ,ta fada sounding so very happy,Siddiqa mansoor taja cheek’s dinta tana ware mata ido,itama murmushi dauke a fuskarta,shirin tafia Abuja sukayi dan tun karar Abba da kuma Sufyan mansoor.
Zuciyar Areefa ta riga da ta bushe ko Sufyan mansoor bai isa ya dakatar daita ba,da murna Aunty ta tarbesu wacce ke auren mahaifinsu tun bayan rasuwar mahaifiyarsu,Aunty ta kalli Areefa tana kama baki take fadin”kin ga yarda Kaduna ta kar?e ki naga kinyi wani uban kiba da kumatu,
Me Siddiqa mansoor ke baki, murmushi kurum Areefa tayi tana fadin”Aunty Yah Safwan fa,tun safe bamu hadu ba.daga waya tayi ta kirasa bai daga ba ta kara kira nan ma bai daga ba,duk tabi ta shiga damuwa,tana kallon kofa sukayi ido biyu da Sufyan mansoor ,wanda da ka gansa kaga fuskar Areefa mansoor shima fari ne sol”tamkar balara be,
Ya bude hannuwa gamida ware mata ,ido murmushi tayi gamida make kafada ya karaso cikin parlorn yana fadin.”ku wannan irin tafiya haka,kuma kina ta kirana a waya ,muna tare da Adee shiyasa ban daga ba…….toh fadamin yar gidana meya faru ina son Jin good news,shi wannan mutumen da kika bi kika nacewa ya shirya yanxu ko har yanzu.”hawaye yaga suna cika idon Areefa mansoor tasan sune weakness din Sufyan mansoor,ke lafia meya faru??”duk yabi ya rude,siddiqa Mansoor ta kallesa ido cikin ido tana fadin”Yaya cikine jikin Areefa kuma cikin Aliyu waxeer.”girman kalma Sufyan mansoor yakeji tana masa nauyi cikin kirji,cikin shege ajikin kanwarsa.”ya mike a fusace ya xsbgawa Areefa shegen mari ya shakota lokaci daya,tana jin sha?ar da yayi mata tana tabata Amma ko kadan baxata karaya ba,mekake yi haka yaya akwai ciki ajikinta kayi hakuri ka saketa kar kayi mata illah,jikin Safwan mansoor babu inda baya rawa,haka tana hango soyayyarta da kuma tashin hankali lokaci daya acikin idanunsa,sakinta yayi ya juya Yabar dakin ba tareda ya kara kallon su ba,na gama da matsalar Sufyan mansoor bana tunanin Abban,sabida nasan xai fadawa Abban…..har ishai basu kara saka sufyan mansoor a idonsu ba,
Har washe gari,hakurin Areefa har ya kare da safe ta gaisheda Abba sai dai bai nuna mata komai ba,,hakan na nufin Sufyan mansoor baiyi magana da Abba ba,
Wlhi na gaji ki tashi kawai mu kama hanya na karasa saurin aeki na,,meyasa bakya bin komai a hankali.”komai kiyi tayi masa gaggawa.”Siddiqa ta fadawa Areefa tana kallonta ta dakune fuska tana fadin”na gaji da wannan jiran Aunty Siddiqa kawai mu koma Kaduna idan ya gama fushinsa sai ya samemu acan,abu daya ne baxan iya dauka ba,yace xai taba Aliyu………..”baxan iya daukar hakan ba ina son kayana a haka,kuma bana son yace xaiyi Shari’a da Aliyu Dan wallahi duka arzikin gidan nan xai kare Ni kawai ki fada masa kamar yarda muka tsara ba shikenan ba.”wayar Siddiqa mansoor ce ta fara ring ganin me kiran ta kalli Areefa da sauri tana fadin”Yaya ne…..da sauri Areefa tace ki daga kiji me xai ce,ku same mu a parlorn Abba da haka ya datse kiran,
Toh tashi muje maybe ya fadawa Abba komai,sun samu Aunty a parlorn tana ha?awa Abba tea,ko kadan Areefa bata so hakan ba,duk harkar ta bata son yinta da Aunty,kafafunta taji suna rawa ganin irin kallon da taga Abba nayi mata,haka ta kasa karasawa cikin parlorn,Sufyan mansoor ya daka mata tsawa yana fadin”akwai sa’anki anan da baxaki karaso ba,da rarrafe Areefa ta karaso ta xauna akan carpet,cikin rawar murya Abba ke fadin”da gaske ne da gaske ne Areefa akwai cikin shege jikin ki??”dagawa Abba kai tayi,ya kalli Siddiqa mansoor yana fadin”baxata zauna min a gida ba da dan shege ya kalli Aunty fuska bbu walwala,
Yake fadin a hada komai nata yau baxata kwanar min a gida ba,
Ku kaimin shegiya kauye kai Safwan ka fara shiri yanxu,ihu Areefa ta fasa tamkar mai jinnu take fadin”baxan je kauye ba Abba !!”kauye kauye fah.”ta fada tana fashewa da kuka,
Cikin sanyi murya Aunty Siddiqa ke fadin”Abba ae idan aka kaita can asirin mu xai tonu kasan mutanen kauye da saka ido,Ni xan bada shawara,mexai hana akaita gidan su wanda yayi mata cikin,suyi renon tsiyarsu acan idan ta haihu dole ya yarda ya Aureta.”haka ya kamata ayi Abba dan baxai ci bulus ba wallahi .”Sufyan mansoor ya fada yana kallon Abba,daga kai Abba yayi yana fadin”ku fara shiri har saratu tabiku ku damka masu ita,kar ta dawo min a gida har sai ranar da naganta da auren yaron nan akanta.Alh.mansoor ya fada da bakin ciki a muryarsa,har suka isa Kaduna acikin motar sufyan mansoor kallonsu kurum Aunty keyi,haka kawai take ji ajikinta ba gaskiyya Areefa da Siddiqa suka fada ba,yarda tasan Aliyu waxeer da mutunci sa da martabarsa,xaiyi wuya ace dan cikin jikin Areefa nasa ne,sai dai yawon da takeyi da maxan banxan da ta saba hurda dasu,suka yi mata ciki ita kuma ganin manyyan kudin dake ga Ali da familyn su xatace cikin jikinta nasa ne ,a gidan Siddiqa Safwan ya saukesu yana fadin”sai da dare suje familyn waxeer,da dare shine dai-dai haka kuma yafi sirri,
Saiti daya tayi na kayan da xata tafi dasu gidan waxeer ,sauran tarkace tasan daga baya xata mallaki fiye ma da irin su a familyn waxeer,ko abincin ta kasa ci duk da cikin bai bata wani wahala sai dai yana yawan sakata cin abinci da kuma kwalama.tun bayan Rasuwar Farhaan take zaune a gidan Ammah,suna ta xuba ido suga me Ammah xata yanke akan auren su,har yanzu taki magana haka ta hana nooryn ta koma dakinta,Matakin farko da Ammah ta dauka shine hukuncin rabasu da junan su,daga ranar da akayi sadakar ukkun Farhaan,ta hana Aliyu kwanar mata a gida,
Shi kuma yaki bude baki ya fadawa Ammah matarsa yake so,xuba ido kurum Khaleel waxeer yayi yana ganin sabon salon da Ammah ta dauko,da taga Aliyu ya shigo mata parlor inhar noory na xaune a wajen xata mata umurnin ta tashi ta wuce daki.ba karamin hurting dinsa hakan keyi ba,ko dan kisising din da yake samu yana rage zafi Ammah ta rufe ko wace kofa,
Itama a bangaren nooryn hakane,sosai take kewar mijinta,duk da mutuwar Farhaan yasa ta dan rage kula Aliyun,Haka karya take tace batayi missing kowane happy moments dinsu da sukayi enjoying tareda Aliyu ba.”ko yanxu tana kitchen Bayan magrib suna shirya abinci dare itada Ammah,mai aekin ta
Nana ta shigo wacce ke yiwa Ammah wanke-wanke kwata-kwata yarinyyar baxata wuce shekaru goma sha ukku a dunia ba,da ladabi take fadawa Ammah tana da baki.Ammah ta kalli noory tana fadin.”bari taje ta duba da haka ta fice daga kitchen din,Jin tayi anyi hugging dinta ta baya,wani irin ihu ta saka da sauri ya rufe bakinta cikin sanyi murya yake fadin”ke nine fah.”Jin kamshin turarensa yasa ta sauke ajiyar xuciya ,ya dawo gabanta yana kallonta da idonsa da suka fada lokaci daya,
Da sauri ta kalli kofa tana tunanin ta ina ya shigo,dan Allah ka tafi kar Ammah taxo pls,ta fada tana kallon kofa,make kafada yayi yana hadata da jikinsa,yake fadin”Yaushe kika xama muguwa haka.”ta bude ido tana kallonsa,ba sai ki fadawa Ammah gidan mijinki xaki koma ba,
Kinji yarda nayi missing manyyan kayana,ya fada yana tsare kirjinta da ido,
Gabanta na mugun faduwa take fadin”dan Allah ka rufamin Asiri Aliyu kar Ammah taxo ta ganmu,zo muje gida.”ya fada yana jan hannunta ,fisge kanta tayi cike da tashin hankali take fadin ka rufamin Asiri Aliyu.”wai meyasa kake haka?”ya girgixa kai yana fadin”so kike na mutu kenan?ya isa ga gas ya kashe gas din ya dawo gabanta ya shiga kokarin cire botin farar shirt din jikinsa yake fadin”babu damuwa ko acikin kitchen xan iya shan kayana kin ga idan Ammah taxo ta ganmu a haka ,sai tayi tunanin bani matata .da gudu taxo xata bar kitchen din ya wani fisgota ya hade ta da bango,yana kaima wuyanta wani irin deep kisses,lalubar xip din rigarta ya shigayi ya xugesa iya karfinsa,xatayi masa musu ya hade bakinsa da nata,Haka hannunsa ya sa cikin rigarta ya shiga murxa abunda yafi kauna da so a dunia,wani irin rikesa tayi tana jin leg’s dinta na kasa daukarta.sunfi minti goma a haka babu abunda ke tashi acikin kitchen din sai saukar breath dinsu,a haka Ammah tayi mugun gani.da sauri taja da baya tana buga kofar,
Fisge kanta tayi da sauri tana fashe masa da kuka,tana girgixa kai take fadin”shikenan Ammah ta ganmu,Ya shafa sumar kansa yake fadin”duk ddin da kika gama sha yanxu sai ki bude baki kina kuka,ya dage kafada yana fadin”Allah yasa Ammah ta ganmu na fison haka,ya fita daga kitchen din Yana fadin”ta hado masa black tea Yan……kasa karasawa yayi ganin irin kallon da Ammah keyi masa,juya kaxo da matarka muna da baki da haka Ammah ta juya tabar wurin…..

Littafin waminal Hoob na kudi ne#500
Idan baki biya ba kika karanta ban yafe ba.”

Account Details
0004157137
Jaiz Bank
Asma’u Buhari Aliyu
Katin wayar MTN.ta wannan lambar#09060259200
Shaidar Biya ta wannan lambar#08086207764

*The game has just started now,who is ready for d actual Journey???”*

Back to top button