Hausa NovelsSakayyah Book 2 Complete

Sakayyah Book 2 Page 27

Sponsored Links

 

                    By

*GARKUWAR MARUBUTA**SAKAYYAH book 2… Page 27*

 

        Na

*Aysha Aliyu Garkuwa*

 

Ido suka zuba kan gadon
dake hargitse ga jini dake kai sai rigar baccin Khausar da suka gani
gefen pillow.

Sai kuma suka kalli juna da mamaki gami da tausayin,

Ummi kama tuni hawaye ya cika mata ido a hankali tace.

“Toh ina take?.”

Da sauri Aunty Hajara ta rumtse idanunta ganin yadda beshid ɗin
ya ɓaci da jini, musamman wannan farin ƙyalle mai  heart dake tsakiyar gadon.

 

Da sauri ta jujjuya kanta sai kuma ta ta kalli ƙofar
Bathroom ɗin sabida jiyo mgn can ƙasa-ƙasa
da sauri tace.

“A’a Ummin Jameel kinji fa kamar mgn a cikin Bathroom
dinsu”.

 Sai kuma duk sukayi
kasake alamun kasa kunne cikin mmki Ummin ta sauƙe numfashi tare da cewa.

“Ai kamar ma muryar Babane a ciki”.

 

Shi kuwa Modibbo da duk saurin Didi ya rigasu, iso kuma da
suka zo basu shiga cikiba iyakar Jakadiya ma falo, shiyasa basu san ya dawo ba,
a zatonsu yana Masallaci kamar yadda haka al’adarsu take kafin ango ya dawo
salla biyu daga cikin ƴan uwanta da dole al’adar masarautarsunce in an kawo
amarya ma sai an bar mata biyu, masu maidawa iyayen yarinya tukuici in ta kawo
budurcinta da kuma kai hatimin mulki da za’a mallakawa mata shaidar
kasantuwarta Gimbiya kenan.

 

 Toh koda ya dawo
kawai ciɗak ya ɗagata ya nufi Bathroom da ita, yana shiga ya direta cikin ruwan
ɗumin daya haɗa mata, tun kafin ya tafi.

 

Jin yadda zafin ruwan ke ratsata ne yasa take yayyarfa
hannunta tare da sakin raunataccen kuka murya adisashe.

A hankali ya ɗan tallaɓe kanta tare da mannawa da ƙirjinsa
cikin sanyi mai cike da bayyanar asalin matsayinta dake cikin zuciyarsa yace.

“Sannu kiyi haƙuri ki zauna zakiji sauƙin ciwon sosai”.

Ya ƙare mgnar da dan ƙara zaunar da ita cikin ruwan ɗumin,

wani raunataccen ƙara ta kuma saki wanda yasa har Jakadiya
da Didi dake falo suka jiyota, cikin sauri Jakadiya ta kalli Didi tare da cewa.

“Inaga sun ɗagata bari mu ɗauko ƙyallen tarihinmu da zanin
gadonmu”.

Kai kawai Didi ta gyaɗa mata.

 Allah yasani ji take
kamar ta shiga to amman ba dama tunda Ita dai surkuwa ce.

 

A can cikin ɗakin kuwa Ummi da Aunty Hajara kam bushewa
sukayi a tsaye kamar wasu sakarkaru, suke kallon ƙofar Bathroom ɗin fuskoki
cike da mamaki.

 

Da sauri suka juyo suka kalli ƙofar jin a buɗe Jakadiya da
yanzu ta shigo, kwaryan dake hannunta ta miƙa Ummi tare da cewa.

“Gashi ta zauna ciki ammafa kada ta wuce 2 minute”.

Toh Ummi tace tare da amsa kana ta ajiye ƙwarya, sai kuma ta
kalli Aunty Hajara dake ruggume da hannun.

“Inaji mafa kamar tana tare da mijinta ne a Bathroom ɗin.”

Aunty Hajara ta faɗa.

Murmushi Jakadiya tayi tare da cewa.

“Ato shike nan ai ni bari in na ɗe…”

Sai kuma suka kalli ƙofar Bathroom jin kamar an buɗe, shi
kuwa Modibbo jin alamun surutaine yasa ya ɗan miƙe tsaye kana ya buɗe ƙofar dan
yaji surune da gaske akeyi a ɗakin.

Da sauri yayi ƙasa da kanshi ganin Ummi.

Ita kuwa Ummi cike da kunya ta miƙa mishi kwaryar nan da
Jakadiya ta bata tana mai kauda kai tace.

“Gashi ta zauna ciki, Amman kada ta wuce daƙiƙu biyu”.

Cikin tsaanin kunya yayi ƙasa da kanshi tare da amsar
kwaryar, ya juya cikin Bathroom ɗin da sauri ya maida ƙofar ya rufe ba tare da
yace komai ba kana bai bari sun haɗa idoba.

Itama Ummi cikin
kunya ta kama hannun Aunty Hajara suka fita.

Jakadiya kuwa murmushi mai cike da jin daɗi tayi, tare da
shimfiɗa wani farin leda mai taushi a gefen gadon zai kuma ta ɗan jawo  wannan farin ƙyalle mai zanen heart ta
sanyashi cikkn ledan kana ta maida shi ta liƙe ya zama kana iya ganin duk jinin
dake jikin ƙyallen sai kuma ta sa hannun ta ɗauko wani ɗan bugeggen katako  mai zagaye da gold a jiki, kana an yishi da
marfin glass daga saman an Rubuta MRS Aleeyu
Mouleey, da manyan baƙin larabci.

Sai a ƙasan kuma aka rubuta. Lalla Khausar.

Cikin ta shimfiɗa ƙyallen tare da maida marfin glass ɗin ta
rufe, sai ya zama tamkar abun aje hoto, sai kuma daga ge da gefensa da ke ɗauke
da tambarin masarautar Mouley ɗin.

Cikin sauri-sauri ta naɗa beshit ɗin kana ta zaro wani fari
mai ɗauke da alamun zanen masarautarsun ta shimfiɗa tare da sa rigunan pillow
da blanket.

Sai kuma ta ɗaukesu tare da fitowa falo da sauri.

 

Tana fita Lalla Khadijah na isowa da kaskon turaren wuta,

Da sauri ta miƙa wa Didi wannan furem ɗin ƙyallen da kuma
sanin gadon, cike da jin dadi Didinta amsa ita kuwa Jakadiya, amsa kaskon
turaren wuta  tayi ta koma ɗakin ta
ajiye.

Gefen gado kana ta jawo ledan nan, ta fito da wata dandatstsiyar
Alƙyabbata irin ta matan masarautar Mouley ɗin, sai kuma wata tattausar riga
mai gajeren hannun, dukansu kolon tutar masarautar sune sai fararen ondis.

Turarukan data kawo tajera gefen kayan.

Sai kuma ta juya ta koma falo bayan ta ƙarasa kimtsa ɗakin.

 

A nan cikin Bathroom kuwa, cikin wani irin fitinennen kallo
Modibbo ke kallon Khausar da ta tura lip inta na kasa tare da kwaɓe fuska, har
lau hawaye na tsiyaya, cikin sanyi ya ɗan tallabo kanta  da hannunsa duka biyu, manyan yatsunshi yasa
tare da fara goge mata hawayen, murya cike da taushi, tausayi, gamin da jinƙai
yace.

“Kiyi haƙuri ko, kin yafewa Yah Mu’allim dinki ko?”. Cikin
Shesh-sheƙan sabida jin yadda zafin ruwan ke ratsa mata jiki, ga wani irin
fitinennen zazzaɓi da ciwon kai da sukayi mata taron dangi, murya a disashe
tace.

“Allah zai saka min”. Da sauri ya kauda kanshi gefe jin
murmushi na gaba da subce mishi, ita kuwa kuka ta ɗan saki tare da cewa.

“Ai dama na gayawa Ummi haka zakayi ta cin zalina amman suka
ki yarda, Allah zai saka min”.

Cikin sanyi ya ɗan tsuke fuska kana yace.

“Zo nan, zo ki shiga cikin wannan inji Ummi”.

Da sauri ta rumtse idanunta jin ya tallabota ya ɗagota, sai
kuma yayi saurin ruggume ta, jin yadda ta saki wata ƙara mai cike da alamun
galabaita.

A hankali ya zaunar da ita cikin kwaryar.

Da ƙarfi ta saki ƙara tare da cakumo wuyanshi ta matseshi
gam a jikinta da yake rawa kar-kar sabida zafi gami da raɗaɗin da jininta ya ɗauka.

 

Rumtse idanunsa yayi da ƙarfi dan ba ƙaramar shaƙa tayi
mishi ba, sai kuma ya fara sauƙe ajiyan zuciya jin ta fara sassauta cacumar da
tayi mishi, ido ya zuba mata jin yadda take ta sauƙe ajiyan zuciya a jere a
jere, sai kuma wani irin fitinennen zufa daya keto mata tako ina a jikinta.

 

Lumshe idanunta tayi tare da jingina kanta da ƙirjinsa.

Tana mai ci gaba da sauƙe numfashi, a hankali yace.

“Da sauƙi ko?”.

Bata kulashi ba, sai idanunta dake rufe domin duk abinda
yake mata bata buɗe idanunta ba.

Sai yanzu da taji ya ɗagota cak daga cikin kwaryar da sauri
ta buɗe idan, sai kuma ta rufesu ganin shima ita yake kallo, ɗan murmushin
gefen baki yayi tare da cewa.

“Toh kiyi niyan wankan tsarki”.

Bata kulashi ba, shi kuwa a hankali ya koma gefen bakin
bathtub din ya zauna.

A hankali ta buɗe idanunta tare da ɗan kallon ƙofar fita,
sai kuma tayi saurin cewa.

“Ni ka daina kallona kuma, ka fita zanyi wanka”.

Bakinshi ya ɗan motsa bata dai ji me yaceba, ta daiga ya
rufe idanunshi alamun bazai fita ba kena, ganin haka yasa tayi niyan wankan,
tare da fara yin wonkan a suffatul ijjiza, kawai ruwa ta sakarwa kanta.

Daga zaune ta gama wonkan, kana tayi al’wala, a hankali ta
yunƙura ta tashi tsaye ga mamakinta kaso 65 ɗari na zafin da takejin ya tafi.

Zafin da takejin ya tafi har wani tsukewa taji jikinta yayi.

Sai kuma tayi saurin da hannunta ta kare ƙirjinta ɗaya
zubawa idanu, da sauri kuma ta maida hannun nata ƙasa ganin yadda ya tsura
wurin ido.

Shi kuwa towel ya jawo tare, da rufe matashi kana ya dauketa
suka fito.

Bisa bakin gado ya ajiyeta, sai kuma ya jawo kujerar dressin
mirror d mai a fabanta ya zauna.

Tare da lakatan mai ɗin ya murza a tafin hannunsa kana a
hankali ya fara shafawa ƙafarta.

Ita kuwa cikin sanyi da rawan jiki tace.

“Yunwa nakeji”.

Yana mai ci gaba da shafa mata mai ɗin yace.

“Toh acici kazar birni, ai ni ya kamata inyi kukan yunwa
nida kika kwana ƙwaƙulewa”.

Cikin mamaki ta zuba mishi ido tare da mgnr zuci.

“Motar sherri”.

Ga mamakinta sai ji tayi yace.

“Ni ne motar sherri”.

Da sauri ta jujjuya kai, tare dacewa.

“A’a da kaina nake”.

Hannunta ya kamo ya shafa mata mai ɗin kana ya juya ya gaban
dressin mirror yana mgna cikin ranshi.

“Komai ma ki, kirani zan amsa, tunda nayi laifi”.

Da sauri ta dauki pant ɗin dake gefenta ta saka.

Sai kuma ta jawo tattausar doguwar rigar nan.

Ta zura, hannunshi yasa ya jawota tsaye, tare da ɗaukar
alƙyabar nan.

Ya zira mata.

Sai kuma ya dawo ta gabanta tare dasa hannunshi kan caɓullenta
ya ɗan matsa a hankali da sauri ta rumtse idanunta.

Sai kuma ta fara jujjuya kanta jin abinda yace.

“Yau ma suna miki ƙaiƙayin ne, in sosai miki”.

Murmushi ya ɗanyi ganin yadda gaba ɗaya jikinta ke karkarwa.

Turarrukan ya fesa mata kana yasa mata hulan rigar sai kuma
ya jawo hulan alƙyabar ya rufe mata kanta.

Bisa sallaya ya jawota.

Ita kuwa idanunta ta rumtse da karfi sabida yadda in ta daga
ƙafarta zafin ke ɗan tsargarta.

 

A hankali ya dawo bakin gado tare da cewa.

“kiyi salla”.

Ya ƙare mgnar yana dafe kanshi da hannun bibbiyu da shima
zazzaɓin yakeji da ciwon kan da yasan rashin baccine ya jaza mishi.

A hankali ta miƙe tsaye bayan ta idar da sallan

Dai-dai lokacin kuma Jakadiya tayi sallama, ɗan tsaki yaja
tare da amsa sallamar kana ya mata izinin shigowa.

 

A gefe ta rusuna cikin girmama ta gaidashi ba tare da ya
kalleta ya amsa.

“Bisa umarnin Didi tace Lalla Mouley tazo mu tafi wurinsu
Ummin Jameel”.

Ta fadi tana kallon Khausar, tare da tura kaskon turaren
wutan da ta shigo dashi a hannunta da kuma wata ƴar ƙaramar kwalba dake cike da
turaren wutan tsuguno na musamman.

Shi kuwa Modibbo. Cikin tsuke fuska yace.

“Uhm”. Ita kuwa hannun ta miƙa Khausar tare da cewa

“Ki tsuguna ki turara jikinki da turaren wutan nan, sai mu
tafi.

 murya na rawa Khausar
tace.

“Bazan iyaba”.

Da sauri Jakadiya ta juya ta fita jin Modibbo yace.

“Kije zan kawota”.

 

Tana fitowa falon ta gaya musu yadda sukayi hakan ne yasa,
duk suka fita Ummi da Aunty Hajara suka koma masauƙinsu, Didi da Jakadiya da
Lalla Khadijah kuma suka nufi kasan.

 

Dai-dai lokacin kuma Lalla Hafsat da Rahama dake kitchen da
kansu suka shiryawa Khausar breakfast mai rai da lfy, wanda natane ita kaɗai,
sai kuma na Abualeey da Modibbo da suka shirya da ban sai kuma nasu duka.

 

Shi kuwa Modibbo a hankali ya miƙa tare da kallonta jin tana
cewa.

“Zan faɗi”.

Hankali ya jawota jikinshi ya ruggume mata tsam, cikin sanyi
ya cusa kanshi a wuyanta yana mai shaƙan daddaɗan ƙamshin jikinta,

Bakin gado ya ajiye ta, kana ya dawo ya ɗauki kaskon da
turaren wutan, ya ajiye gefenta ta inda zai zauna tattare jallabiyar jikinshi
yayi ina ya zauna, hannunshi yasa ya kamo nata tare da jawota gaban shi, cikin
karkarwa da rawan murya tace.

“Ƙafafuna rawa suke bazasu iya ɗaukata ba“.

Kanshi ya ɗan ɗago ya kalleta sai kuma ya ɗan sunkuyo
turaren wutan ya danga mai ɗan yawa ya zuba a cikin kaskon, sai kuma ya jawota
gaban shi sosai tare da sa hannun ya ɗan buɗa sawunta, da sauri ya yawota gaban
shi sosai hannunshi ɗaya yasa ya tallabo ƙugunta, kana ya manna kanshi da
cikinta yayi mata Garkuwa Da kyau dan ya lura zata iya faɗin.

Da sauri ta rumtse idanunta tare dasa hannunta ta kamo
hannunshi ɗaya da taji ya zira cikin rigar ta yana jan pant ɗinta yanayin ƙasa
dashi.

Jin yadda ta riƙe mishi hannun ne yasashi ɗan jujjuya kanshi
murya a tausashe yace.

“Ki bari in cire shi, hayakin zaifi shiga jikinki da kyau
yayi miki aiki“.

Ya ƙare maganar da yin ƙasa da shi baki ɗaya.

Sai kuma yasa sawun shi duka biyu tsakanin nata sawun.

Wanda haka yasa dole ta zare ƙafarta ɗaya, sai kuma ta saki
ƙara da ƙarfi jin ya ware sawun nashi da yasa dole ta zauna kan cibiyoyinsa,
manna kanta tayi da ƙirjinsa tare da rufe udanunta hawaye na kwaranyo mata
sabida zogin da takeji.

Shi kuwa Modibbo cikin sanyi ya ɗan sunkuyo tare da gyara
zaman kaskon sautin jikinta sai kuma ya tattare rigar nata ya buɗashi ya
bazashi bisa guiwowinshi ya zamana ta zama ba komai a jikinta ta ƙasan, sai
kuma ya ƙara ɗanƙo turaren wutan ya saka a ciki.

Ai ko kai tsaye kan jikinta hayakin ke tashi, a take ta fara
sakin numfashi da ajiyan zuciya sabida wani irin daɗin da taji a jikinta sai
kuma ta lumshe idanunta sabida jin yadda jikinta ke mata wani irin daddaɗan
ƙaiƙayi alamun ciwon na workewa ne, bisa ƙarfin magungunan dake cikin turaren
wutan.

Numfashi mai sanyi ta fesar tare da ɗan buɗe idanunta.

Idonta ta ɗan zubawa lips inshi da yake ɗan motsawa alamun
mgn yake sonyi, kuma mishkilanci ya hanashi, fahimtar hakane yasa ta ɗan tura
baki tayi tare da hararanshi ta ƙasan ido.

Da sauri ta kalleshi jin yasa hannunsa duka biyu bisa
ƙugunta ya riƙe da kyau kana murya can ƙasan maƙoshinsa yace.

“Anya kuwa kina son ki rabauta, ki samu jannatul firdausi”.
Cikin kwaɓe fuska sabida yanayin yunwa wahala da bacci tace.

“Ina so mana”.

Kamar cikin raɗa yace.

“Kin san dai sai na ɗaga ƙafa zaki shiga ko?”.

Ya ƙare maganar cikin wata iriyar murya mai nuni da shima
zazzaɓin ne a jikinsa kana ya tsareta da matattun idanunsa, ita kuwa Khausar
cikin sanyi tace.

“Eh nasi”.

Kanshi ya ɗan manna da ƙirjinta a saman lips inshi yake

“Toh bakya son shiga kenan?”.

Ya ƙare maganar yana shafa sajenshi kan haɓarta.

Cikin sanyi tace.

“Toh bazaka ɗaga min in shigaba kenan?”.

“Eh in baki bar tura min baki da jujjuya fitinannun idanun
nan naki ba kam bazan ɗafaba”.

Da sauri tace.

“Kayi haƙuri bazan ƙaraba”.

Kanshi ya ɗan jujjuya tare da cewa.

“Naƙi”.

Cikin zubda hawaye murya na rawa da alamun tsoro tace.

“Ai dama na sani baka sona ka tsanane kai zakama fi son in
shiga wuta”.

Murmushi mai cike da jin daɗi yayi kana a hankali yace.

“Sorry yi shiru in dai kina min duk abinda nakeso, to zan ɗaga
miki, ki shiga ba ke ba wuta jinki ko Minha”.

Ya ƙare maganar tare da manna fuskarshi da tata, a hankali
ya ɗan zaro harshensa cikin sanyi ya fara lasar hawayenta tare da shaƙan
ƙamshin jikinta.

Allah ya sani so yake suyi bacci, amman ya lura tana cikin
galabaita, ga jikinta zafi kana ko muryarta bata fita, gashi tun ɗazu take
ƙorafin yunwa, kuma ga umarnin Didi.

A hankali ya ɗago kanshi ya kalleta jin tana cewa.

“Yunwa nakeji, kamar zan faɗifa kaina ciwo bayana ciwo,
ƙuguna ciwo, idona ciwo”.

cikin wata amintacceyar murya yace.

“sorry Minha vidaa Bazaki faɗiba bari in kaiki kici abinci
mu tafi asbiti”.

Sai ya ɗan tsaida ita tare da sa mata pant ɗin kana ta gyara
mata rigartan.

Sai kuma ya sunkuyo.

Cak ya ɗagata tare da mannata da ƙirjinsa,  sassayan numfashi ya fesar tare da fitowa da
ita ya nufi Side ɗinsu Ummin.

 

Dai-dai lokacin ɗin da suka iso ƙofar falon dasu Ummin suke
tace.

“Ka sauƙeni a nan zan ƙarasa da kaina”.

“Naƙi”. Yace yana mai kutsawa cikin falon.

Da sauri ya sunkuyar da kansa dan kusan duk su Ummi suna
falon cikin wani irin fitinennen kunya
ya direta bisa 3 sitter kai a sunkuye yayi musu gaisuwar ƴan kasuwa tare
da juyawa ya fita.

 

Yana fita yaci karo da Didi da Lalla Hafsat da Jakadiya, a
hankali ya raɓa jikin gini tare da sosa ƙeyarsa.

Cikin kauda kai Didi tace.

“Kaje ƙasa Khadija ta baka abinci”.

Cikin sanyi yace.

“Toh”. Sai kuma ya nufi ƙasan.

 

Ita kuwa Khausar yana fita ta kife kanta bisa cinyar Ummi da
tazo ta zauna kusa da ita, cikin rawan jiki da muryar data disasha yasa bata
fita sosai tace.

“Ummi yunwa nakeji, kaina ciwo zazzaɓi nakeji”.

Sai kuma ta saki sabon kuka.

Dai lokacin kuma Didi suka shigo.

Da sauri ta matso gabansu shafa kanta tayi cike da kulawa so
da tausaya take mata sannu tare da tambayar Ummi me  ke damunta.

Kai ta jinjina jin abinda Ummin ta gaya mata, kana cikin
kulawa tace.

“Hafsat sauƙa kije ki cewa Ibraahim yaje ya ɗauko Dr
Jameel”.

Da sauri tace to kana ta juya ta fita.

 

Ita kuwa Ummi a hankali tacewa Khausar.

“Tashi kici abincin to”.

Cikin rawan jiki ta tashi zaune da taimakon Aunty Rukayya
dake jera mata sannu.

A hankali suka kalli gefen da Hajia Bunayyah take sabida jin
wani dogon tsakin da taja tare da juyawa ta bar falon.

 

Cikin zubda hawaye Khausar ta kalli Asma’u dake ta sakin
murmushin tare da sune kanta.

Sai kuma ta kalli Dija ta kuna kalli Aseeya.

Cikin muryar kukan tace.

“Ummi ki ganifa dariya su Asma’u kemin”.

Da sauri Asma’u da Dija suka nufi cikin ɗaki sabida daƙuwar
da Ummi tayi musu, Asiya ma bayansu tabi.

Hajja Nana kuwa cikin dariyar mugunta a fili tace.

“Yar nema ba cewa kikayi Ni Modibbo nake so”.

Cikin Shesh-sheƙan kuka murya na rawa tace.

“Wallahi na fasa, ni dai Wlh ku maidani wurin Mommy na ta
kare mgnar da iyakar gskyar zuciyarta”.

Dariya ce ta kubcewa Aunty Hajara da Rukayya Hajja Nana da
Innayi kuwa tafa hannu sukayi.

Ummi kuwa da sauri ta jawota jikinta.

Didi kuwa tea mai zafi ta fara haɗa mata.

 

A can ƙasa  kuwa
kwance kan 3sitter Lalla Hafsat ta samu Moddibo
jikinsa cike da zazzafan kasala gaba ɗaya yayi so weak baki ɗaya bashi
da kuzari saboda yayi abinda bai taɓa yi ba a tsawon rayuwarsa duk jikinsa
amace yake ga wani fitinennen zazzaɓi da yakeji yana ratsa ƙasusuwan jikinsa,
yayinda cinyoyinsa kuwa gaba ɗaya jinsu yake kamar ba nasaba, a hankali ya
kishingiɗa da jikin Kujera yayin da ya manna kansa da jikin Kujeran yasa
hannunsa duka biyu ya riƙe sabida zazzafan zazzaɓi yake ji wanda yasa har
jikinsa ke rawa ga kuma ciwon kai wanda alamun kukanda yayi tayine da rashin
bacci suka haifar masa da ciwon kan.

Cikin kula ta isa wajen tare da ɗaura hannunta na dama kan
goshinsa jin hannunta agoshinsa ne yasa ya buɗe Idanunsa dake lumshe ya
kalleta.

Cike da kulawa tace.

“Jikin ka zafi,Zazzaɓi kake jine?”.

Kai ya gyaɗa tare da maida idanunsa ya lumshe.

 Cikin kulawa ta kalli
fuskarsa tare da cewa.

“Subhanallah Sannu”.

Sai kuma ta juya ta kalli Ibraahim da yanzu yake shigowa
tare da cewa.

“Yawwa Ibraahim dama yanzu Didi tace in faɗa maka kaje ka
kira Dr Jameel yazo ya duba Khausar bata jin daɗi.

Shima Aleeyu gashi yanzu naji duk jikinsa da zafi ga yanda
ya zama wani so week haka nan!”.

Jin abinda ta faɗa yasa Moddibo buɗe Idanunsa ahankali tare
da faɗin.

“Dr Jameel kuma?.”

Kai ta gyaɗa mishi alamun eh.

Cikin ɗan rawan sanyin zazzaɓin yace.

“Ba Dr macene? Bana so Dr Jameel ya dubata, a nemi mace”.

 

Kai Ibraahim ya gyaɗa kana yace.

“Toh Shikenan bari naje na taho da Dr Jameel,Da Dr Isha in
yaso Dr Jameel sai ya duba ka ita kuma
sai mace ta duba ta”.

Kai Moddibo ya gyaɗa kana Ibraahim ya juya ya tafi…

 

Acan ɓangaren su Didi kuwa sauri Didi ta Sanya hannunta ta
karɓi plate ɗin da Khausar ta ke miƙawa Hajja Nana mata alamar ta ƙoshi ita
kuwa Hajja Nana harara ta watsa Khausar tare da cewa, nicema zan karɓi ragowar
yunwarki ai shi daya jinyataki sai shi zaiyi jinyarki, Ni ko sannuma zaki samu
a wuri nane,.

 

Murmushi Ummi da Didi sukayi, cikin kulawa Didi tace.

“Ki hutama Hajia ni zanyi jinyar ɗiyata”.

Murmushi suka kumayi baki ɗaya.

 

Ita kuwa Khausar a hankali ta koma baya tare da jingina
kanta da jikin Kujeran ta lumshe manyan idanunta da suke ɗan kumbure kana sunyi
ja saboda yawan kuka da rashin bacci.

Sai kuma ta fesar da sassayan numfashi sabida cikinta yayi
mata tib saboda yanda abincin ya mata daɗi taci sosai musamman ma naman ya dahu
yayi lugun gashi yayi yaji yadda take so.

Anutse Didi ta sake miƙa mata kofin tea mai kauri tare da
cewa.

“Karɓi ki shanye”.

Sunkuyar da kanta tayi kana tace.

“Cikina ya cika”.

Ummi dake gefenta tace.

“Karɓi ki shanye ki kafa kai kawai ki shanye”.

Cikin lumshe idanu ta karɓa tare da kafa bakinta ta shanye
tass.

A take zufa ya shiga tsats-tsafo mata tako ina.

Cike da kulawa Ummu ta kalleta tare da faɗin.

“Sannu”.

Kai ta gyaɗa tare da lumshesu so take ta gyara zamanta amman
tsoron yadda zata motsa take, sabida har yanzu tanaji zogi.

Gajiya da zaman ne yasa ta ɗan kishingiɗa.

Ummi na gyara zamanta tace.

“Kwanciya kike sonyi?”.

Langwaɓar da kai Khausar tayi kamar za tayi kuka ta gyaɗa
mata kai tare da faɗin.

“Eh jikina ba ƙarfi,Ummi baki daya jikina amace”.

Numfashi Ummi ta fesar ganin yanda take ciccije baki alamar
tana jin ciwo ajikinta tace.

“Toh ki kwanta”.

Kai ta gyaɗa tare da kwanciya.

 

Zama Didi ta gyara tare da kallon Hajja Nana dake cewa
Innayi.

“Dan Allah nikam Innare yau dai kam ki faɗa mana meye ne
sirrin Al’amarin tafiyar ku gari ya garire kuka je kuka zauna har wancan
ƙasar”.

Kallon Didi Innayi tayi alamar kin amince in basu labari.

Kai Didi ta Jinjina tare da faɗin.

“Ki faɗa musu”.

 

Zama Innayi ta gyara tare da juyawa ta fuskancesu baki ɗaya
kana ta fara basu labari kamar haka…

Masarautar Mouley ta kasance Masarautace mai girma da ƙarfin
iko kana da matsayi a yankin Africa baki ɗaya, sannan su su Abualeey sarki
Youseep kenan su goma ne acikin Mahaifin su suna da ƴan Uba su kuma su huɗu ne
kaɗai acikin Mahaifiyarsu maza biyu mata biyu Sarki Youseep Muhammad Mouleey
sai Haroon Muhammad Mouley, sai Salma Mouley da kuma yar autarsu mahaifiyar Dr
Jameel.

Sannan Mahaifiyarsu ta kasance itace Uwar gida mahaifinsu
tun yana da rai yayii Murabus aka ɗauki mulki aka bawa Sarki Youseef kasancewar
shine babba sai suka fara fuskantar ƙalubale ƴan Uba sukayi ca akansu bayan
yayi Aure dai duk abin bai bayyana sosai ba, saida suka fara haihuwa, aihuwarsu
ta forko aka samu, Lalla Khadijah lafiya lau aka raineta har aka yayeta. Kana
aka haifi Lalla Hafsat lafiya lau itama aka yayeta, amma tunda aka fara haifan
ƴaƴa maza sai ya zama duk Namijin da aka haifa baya wuce kwana arba’in a duniya
tun yana kwana talatin zuwa arba’in ɗin ake sace yaro, baya wuce kwana uku sai
a tsinci gawar yaro a tsakiyar fada, an kashe shi.

Masarautar Mouley gaba ɗaya ta shiga ruɗanin wannan
al’amari, sai da Gimbiya Didi ta haifi ƴaƴa maza uku duk ana kashe su kafin ta
haifi Moddibo da aka haifi Moddibo kuma dai-dai lokacin Mahaifin Moddibo ya
kamu da ciwo ya zama kamar irin Kiɗimamme haka ya rasa gane Ainihin abinda ke
damunsa har aka ɗauki Sarauta aka maida ita hannun Ƙaninsa.

Ƙanin shine ayanzu yake kwance kusan shekaru ashirin da
biyar bashi da lafiya.

Sanin danayi ana haifar yara basa wuce kwana arba’in ake ɗauke
su yasa nayi niyya taimakon uwar ɗakina da uban ɗakina da kowa yasan yanayin
jikinsa akwai alamun sa hannun magauta.

Kasan cewa nice Jakadiyar Didi yawan zama da ita da yaranta
da take musu fulatanci yasa na iya yaren sosai tunda alokacin ma munyi kusan
shekaru goma sha uku tare, dan a lokacin shekarun Lalla Khadijah 12 cib Hasfat
10. Haka yasa nayi niyyar ɗaukesa naje wani waje nayi rayuwa dashi ya zama
zakaran gwajin dafi kafin na dawo dashi shiyasa na rubuta wasiƙa sannan na ɗauki
sandarsa wanda tsarin Masarautarne duk Amaryar da aka aura ranar da akayi First
night ɗin ta idan aka sameta cikakkiyar budurwa za’a bata wannan sandar Amma
sandar za’a ajiyeta aɗakin Tarihi na Masarautar inda ake ajiye ƙyallayen budurcin
matan masarautar da sarautar ke hannunsu, sai randa ta haifi ɗa Namiji ya kai
shekara ɗaya aduniya za’a ɗauko shi akawo mata shi matsayin sandan godon
sarautar, dan haka ne na ɗauki sandar sannan na shiga ainihin ma adanar
masarautasu kasancewata amintacciyar Jakadiya yasa nasan duk shiga da fitan
Masarautar shiyasa na shiga na ɗibi Silalllan Gwal ɗinna kafin na rubuta wasiƙa
da yi musu cikekken bayanin ba sace ɗansu akayiba ni na ɗauleshi na tafi dashi
kuma in dai yana raye ina raye wata rana zan dawo dashi.

Na basu cikekken tabbacin Cewa zan dawo musu da ɗansu in Sha
Allah su kwantar da hankalin su nayi musu alkawarin zan kula dashi sannan zan
bashi tarbiyya za kuma yi mishi duk abinda uwa da uwa zasuyiwa ɗan su bazaiyi
kukan rashinsu a kusaba susa aransu zan dawo musu da ɗan su lokacin da yafi
ƙarfin magautan su a kuma lokacin da sukafi buƙatar sa kusa dasu…

 

Nan’nauyan ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe sai kuma ta juya ta
kalli Hajja Nana dake cewa.

“Sai kuma ki rasa inda zaki je sai garin mu”.

Murmushi Innayi tayi kana tace.

“Eh saboda lokacin da aka kawo Didi ƴar Nigeria ce jahar
Adamawa sheik Jabeer ya kasance Aminine ga Sarki Mohammed Aliyu Mouley shiyasa
suka haɗa Auren ƴaƴan su.

Shiyasa dana tashi na tafi Nigeria naje na zauna ta yankin
dake magwabtaka da yankinsu kuma shiyasa nake hana Modibbo zuwa Adamawa, sai a
sace yaje sau ɗaya nanma da naji nai ta kuka haka yasa yayi min alƙawarin bazai
sake zuwaba Marocco ma nice ke hanashi zuwa da tuni yazo, niko nasan duk wanda
yasan iyayensa to dole in ya ganshi gane ɗansune”.

Murmushi kawai Didi keyi tana sake jin ƙaunar Innayi aranta
ta yanda ta riƙe mata amanar ɗanta ta kuma bashi tarbiyya.

Innayi kuwa idanunta akan Hajja Nana ta cigaba da cewa.

“Daga nan kuma ban san meya faruba a masarautar Mouley bayan
tafiyata ba”.

Numfashi suka sauƙe kowa yana sake jinjina girman ikon Allah
aransa da yanda al’amarin ya kasance kana suka haɗa baki wajen cewa.

“Ikon Allah rabo nefa.

Rabon Aurensa da Khausar ne ya jasu”.

Amintaccen murmushi Didi ta Saki kana tace.

“Aikam Al’amarin Ubangji ya wuce wasa sai godiya”.

Sai kuma ta ɗan kalli Innayi tare da cewa.

“Bayan tafiyarku da wata biyu Sarki Muhammad Mouley ya rasu,
kana a ranar Unclee Haroon ya cika shekaru biyu a karagar mulki ƙanin Abualeey
kenan. kasancewar jinyar Abualeey gaba gaba kawai takeyi, to shekarunsa huɗu a
kan mulki yayi haɗari shida Baban Jameel da kuma Mamin Jameel ɗin.

A lokacin Yusuf ɗinshi ƙaramine, haka yasa dole aka bawa
Unclee Yazidu. Shekaransa ɗaya rak bisa mulki, a lokacin kuwa wannan dokin Rinƙas
yana tsaka da ƙuruciya, abin mamaki dokin nanne ya kasheshi har lahira a
tsakiyar fada, bayan rasuwarsa aka ɗaura ƙaninsa Zarid, shima shekararsa ɗaya
dokin ya kasheshi irin kisar da yayiwa ɗan uwansa zuwa lokacin kuma Allah ya
bawa Abualeey sauƙi duk larurar dake tare dashi haka yasa akace shi zava
maidawa mulki, shi kuwa yace shi baya buƙatar mulki a lokacin jinyar ɗan uwansa
shine a gabanshi mu kuma Alhamdulillah an haifi Ibraahim an raine shi lfy haka
yasa,

Yace a bawa ƙanin Zarid Isman abin mamaki ba yadda ba’ayu da
isman ya karɓi mulkin nanba fir yace shi baya so, da aka matsa mishi sai cewa
yayi kawai shifa bazaiyi mulkinba tunda sauran yayunsa duk wanda aka bawa
mutuwa yakeyi, kawai sai ya rinƙa faɗin duk abinda sukayiwa Abualeey yace sune
suka so haukatashi kuma sune suke kashe mun yarana uku duka, kuma sunema suka
kashe mahaifinsu daga nan ya zama mahaici yanzu haka shi yana raye ko yaushe
yana tsakiyar fada ranar da Aliyu yazo ma Allah ne ya tsaresa dan Aliyu da
dokin ya kashisu dan shi ya kashe mahaifiyarsu ma Lalla Adir tohfa haukacewarsa
da sirrinsu da yake ta tonawa ne yasa muka gane cewa Rinƙas yanayi mana faɗa da
magautanmu ne, duk da ƙanensu mata da suka haɗa uban su dai kamar ba a’lamun
cutarwa haka yasa aka matsawa Abualeey akan ya amshi mulki.

bisa dole dai, ba don yasoba aka sake daurashi kan mulkin
Alhamdulillah yanzu dai masarautar Mouley babu wasu bayyanannun magauta sai dai
ɗan abinda ba’a rasaba wanda tsoron yasa suka bari daga forko dai tsoron Allah
bai sa sun tubaba, sai tsoron rinƙas da yasa suka rusuna amman zuwa yanzu sun
gane cewa Allah shine abin tsoro zuƙata sun tsarkaka ko nida abokan zamana bamu
da wata matsala asalima Gimbiya Sahra ita ke shirya komai na Khausar saidai ita
batama taɓa haihuwaba sai ta ukun mu kuma ƴaƴanta duk matane, ta hudun kuma
ƴaƴanta yarane amman ita duk mazane mu dai Alhamdulillah”…

Sai kuma duk suka sauƙe nannauyan numfarfashi Khausar kuwa
ido cike da alamun bacci da ciwon ta lumshesu

 

Dai dai lokacin kuma Dr Eshaa da Lalla Hafsat suka shigo wacce
bisa duk kan alamu tayi mata bayani.

Shogowan sune yasa suka rufe maganar tare da yi mata sannu
da zuwa amsawa tayi tare da gaishe su cike da ladabi.

Cikin kulawa ta zauna kusa da Khausar tare da ɗan shafa
gefen fuskarta.

“Sannu Allah ya sauƙa”.

Amin Ummi da Didi suka amsa.

Hajia Bunayyah kuwa baki ta taɓe a ranta tace.

“Allah shi ƙara”.

Ita kuwa Dr Isha cikin kulawa ta muƙawa Didi

Magunguna tare da faɗin.

“Lalla Hafsat tamin bayani, a bata magungunan tasha yanxu In
Sha Allah duk wani zugi ko zazzaɓi da ciwon kai zata daina jinshi”

Amsa Didi tayi tare da fara ɓalla kana tace.

“Ai yanzuma kuwa zan bata”.

Gyaɗa kai Dr Isha tayi tare da sallamansu ta fita.

Didi kuwa maganin ta bawa Khausar tasha kana ta miƙe tabi
bayan Dr Isha da bata tsaya duba ko Khausar ta samu rauni ba, dan tasan ko ta
samu rauni tsumin tsarin masarautar da turaren wutan zasu haɗeta…

 

Acan Falon Didi kuwa Dr Jameel ne  ya bawa Moddibo magunguna kana ya koma gefe
yana amsa kiran da aka masa daga asibitinsu.

Ahankali Moddibo ya miƙe ya nufi ƙofar da sai kashi Side ɗin
su, dai-dai lokacin kuma Didi ke dawowa daga Side ɗin su Khausar.

Kallonsa tayi tare da cewa.

“Ina zaka je?”.

Cikin yanayin zazzaɓin da yake ji ya fesar da numfashi kana
ya motsa laɓɓansa tare da cewa.

“Zanje In kwanta ne”.

Tsayuwarta ta gyara kana tace.

“A’a muje dai kaje kaci abinci tukunna”.

Ba musu ya gyaɗa kai kana ya nufi dining tana biye dashi
zama yayi tare da ɗan rumtse idanunsa.

Gefensa ta zauna kana tayi serving ɗin sa,

Sai kuma ta kalli Dr Jameel tare da cewa yazo suci abinci.

A hankali Modibbo ya kalleshi jin yana cewa.

“Didi Azumi nakeyi”.

Kai Modibbo ya ɗan jinjina dan zuwa yanzu dai ya fara
gamsuwa da sauyawar Dr Jameel, musamman yadda ya dage da azumi dan daƙushe
sha’awarsa.

 

Ita kuwa Didi kai ta jinjina sannan ta sawa kanta  suka fara cin abincin, yana ganawa ya miƙe.

Da sauri tace.

“ina kuma zakaje, kasha maganin ne?”.

Dai-dai lokacin Dr Jameel ya iso wurin kujera yaja ya zauna
yana cewa.

“Eh Didi yasha”. Sai kuma ta juyo ya kalli Modibbo tare da
cewa.

“Amman fa kamar ba zazzabin kawai ke damunsa ba na lura yana
yawan miƙa kamar wanda jikinsa ke masa ciwo, bini bini ya dafe ƙugunsa”.

Da sauri Didi ta miƙe tare da turawa Dr Jameel ɗin womers ɗin
abinci gabansa kana tayi cikin falon dan tasan ba ƙaramin aikin Dr Jameel bane
yayi ɓaram-ɓarama, a gabanta haka yasa ta ma mance yace yana azumi.

shi kuwa Modibbo wani irin harara ya rabkawa Dr Jameel tare
da cewa.

“Ace mutum shi bakinsa baya iya shiru”.

Murmushi Dr Jameel yayi tare cewa.

“Na lura baka taɓa sanin maceba, da alamu jiya kuma kayi
yaƙin fatauci shiyasa ƙugu da jinyoyi suke ciwo, ah aini da na ɗauka kai kam ba
abinda zakayi da mace yadda kake wasu abu kamar waliyi, shine tun ba’aje ko
inaba kaje kai ta karya ƙugu ka kwashi Gara, yanzu kuma jiki magayi dan na lura
baka sararawa yar mutaneba”.

Sai kuma yayi saurin dage kansa tare da sakin kara jin yadda
Modibbo ya kaiwa bakinsa bugu.

Dariya ya fashe dashi tare da bin Modibbo da ido kana ya
dawo tsakiyar falon.

 

 A hankali ya nufi
Side ɗin sa saboda wani irin bacci da yake ji ga zazzaɓin ya fara masa yawa
alamar maganin ya fara kokawa da Zazzaɓin yana shiga ya kwanta bisa 3 sitter…

 

Jakadiya kuwa kai tsaye ɗakin Tarihin Masarautarsu takai
ƙyallen budurcin Khausar.

anan aka ajiye wannan frame ɗin kana ta ɗauko sanda da
Jigidan Zinare mai tambarin Masarautar Mouley sai chain na ƙafa shima na Zinare
ne  kuma munduwa mai tambarin Masarautar,
da dai  wasu kaya masu masifar kyau da ɗaukar
hankali kai tsaye sashen Didi ta shiga kana ta kalli Didi dake zaune kan 2sitter
daga ƙasa Carpet ta zauna tare da faɗin.

“Yawwa Didi gashi an gama haɗawa”.

Sanyayyan Murmushi Didi tayi hakan ganin abin sai ya tuna
mata da lokacin da aka kai mata nata cikin sauƙe ajiyar zuciya tace.

“Toh shikenan mu tafi mu nunawa Niyna daga nan mu tafi da
ita”.

Miƙewa Jakadiya tayi suka nufi Side ɗin Niyna daga nan
kuma  suka shiga sashin abokan zamanta
suka nuna musu kana suka wuce wurinsu Ummi.

Hajja Nana, Innayi da Hajja Umma suka samu azaune suna hira.

Yayin da Ummi Khausar Asma’u Dije da Asiya ke bedroom.

Zama Didi sukayi kana suka sa aka kira su Ummi,Hajiya
Bunayya,Aunty Ruƙayya, Aunty Hajara duka suka fito falon Jakadiya ce tayi musu
bayanin cewa.

“Ga wannan Sandar amma yanzu dai an nuna muku ne saboda
tabbacin cikekken tukuicin da aka samu daga Masarautar Mouley ce”.

Wani irin farin ciki ne ya mamaye baki ɗaya ilahirin
zuciyoyinsu saɓanin Hajiya Bunayya da take jin wani sabon kunci da tashin
hankali aƙahon zuciyarta.

Jakadiya kuwa cike da alfahari ta cigaba da cewa.

 “Kuma yanzu za’a sake
mai dashi cikin karagar masarautar tarihin gefenta sai sanda aka samu ɗa namiji
ya cika Shekara ɗaya ranan za’a mallaka mata sandar ahannunta saboda sandar
shine zai nuna shaidar Lalle gadon Masarautar a ɗakinta yake”.

Cike da matsanancin farin ciki Innayi tace.

“Alhamdulillah abinda ake ƙi dai shi ya tabbata in  Allah yaso Sarauta dai tana nan ta tabbata a ɗakin
Lalla Didi”.

Niynah kuwa murmushi take tare da faɗin.

“Alhamdulillahi burin magauta bai cika ba”

 

Acan ɗaki kuwa Asma’u ce ta kalli Khausar tare da ƙyalƙyalewa
da dariya kana tace.

“A’a manya gari yane duk bakinki ya mutu. Yah Moddibo yayi
aiki kenan”.

Kallonta Khausar tayi tare da tura baki cikin yanayin jin
bacci saboda magungunan data sha ta harareta da kumburarrun idanunta sai kuma
ta murguɗa baki.

Ware idanu Asma’u tayi tare da faɗin.

“Eh lallai yarinyar da sauran ki har yanzu Yah Moddibo bai
ladab tar dake ba tunda har kika samu idanun harara da bakin tsiwa”.

Wani kallo Khausar tayi mata cikin dishsheyar murya mai cike
da sanyi da rauni alamun ko yanzu tana iya kuka a hankali tace.

“Hmmm Ladabtuwa na nawa kuma, sai dai kuma in kasheni ya
rage yayi”.

Sai kuma ta lumshe idanunta hawaye masu zafi suka zubo
ahankali ta taune lips ɗin ta na ƙasa tare da cewa.

“Naji azabar da tunda Uwata ta haifeni ban taɓa ji ba, salon
mugunta kuwa babu wanda Yah Moddibo bai haddace ba bayan makarantar Hadda da
yaje ina ga har da na koyon mugunta da zalumci yaje yayi Mater’s ya iya salon
mugunta iri da kala, Ni dai Allah ya sani ba abinda zance sai Allah ya saka min
kuma inyi ta Addu’a Allah ya tsareni da sherrin muguntarsa”.

Ta kare mgnar murya na rawa, da kuma iyakar gskyar
zuciyarta.

 

Wani sabon dariya Asma’u ta ƙyalƙyale dashi harda riƙe ciki
kana tace.

“Uhm lallai su Fattanah anji maza wato har Master’s Yah
Moddibo yayi a fannin mugunta”.

 Cikin kauda kai
Khausar ta runtse idanunta tare da cewa.

“Ayyah am Asma’u kiyi dariya son ranki kema kwana nawa ne
zaki zo irin wannan Matsayin?”.

Murmushi Asma’u tayi tare da miƙa mata wayar kana tace.

“Gashi naga Mommy ke kiran”.

  Tana karɓan wayar ta
fashe da kuka.

Shiru Mommy tayi tana jin shesh-sheƙan kukanta kusan minti
biyu ta ɗauka tana kukan kafin cikin rawan murya tace.

“Momy ina kwana”.

Ajiyar zuciya Momy ta sauƙe tare da cewa.

“Kin gama kukan?”.

Kamar jira take sai kuma ta sake fashewa da sabon kuka cikin
sauƙe numfashi Momy tace.

“Meyesa bakya girma ne Mamana. ai rayuwar nan da kike gani
hakuri ake musamman mace dole abubuwa suzo maka ayanda ba kayi zato ba, ki koyi
dauriya Khausar agaban surkunan ki kike fa, kinga za’a barki agarin da babu
kowa naki ki iya dauriya ke macecefa wata rana ma haihuwa zakiyi”.

Kuka ta kuma fashewa dashi cike da rauni tare da cewa.

“Wallahi Mommy ni nafasa Auren zan biyosu in dawo wallahi ni
na fasa bazan zauna ba zan biyosu bazan zauna a garin nan ba kasheni zaiyi”.

Sai kuma taja ajiyar zuciya tare da cigaba da faɗin.

“Dama shi mugune sannan kuma an kawo ni inda ba kowa nawa
zai cigaba da yimin mugunta”.

Cikin sauƙe numfashi Momy tace.

“Kul kada In sake Jin kin faɗi haka abakin ki bana so, ce
miki akayi aure wasa ne,  ina Umminki?”.

Cikin Muryan kuka tace.

“Tana falo”.

Kai Mommy ta gyaɗa tare da faɗin.

“Toh bawa Asma’u ta kai mata”.

Miƙawa Asma’u wayar tayi ta karba kana ta fice ta kaiwa
Ummi.

 

Bayan sun gaisa da Ummi fuska ɗauke da yalwataccen farin
ciki Ummi tace.

“Kai Alhamdulillah Momyn Khausar yau muna cike da farin ciki
in Sha Allah gobe zamu dawo, zamu dawo da tukuici mafi tsada da daraja na
munduwar masarautar Mouley shaidar yarmu ta kawo budurcinta ”.

Wani banzan kallo Hajiya Bunayya ta watsa mata Ummi kuwa
cikin farin ciki ta cigaba da cewa.

“Khausar ɗin mu ta kai budurcinta gidan miji sannan Sarauta
wanda muke da yaƙinin in Sha Allah aɗakin Khausar zai kasance”.

A wannan karon ƙwaffa mai ƙarfi Hajiya Bunayya tayi ta
sunkuyar da kanta ƙasa yayin da idanunta suka kada sukayi Jawur cike da takaici
bakin ciki da hassada tace.

“Uhmm ai duk gaggawar asara ta dai jira samu”.

Da kallonta suka bita sabida su dai fulanine ba wata
cikekkiyar hausace garesu ba dan haka basu wani fahimceta ba bare su damu.

 

Mommy kuwa cikin hayaniyar da take jiyowa tace.

“Naji kamar kina cikin mutane”.

Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin.

“Wallahi ina cikin mutane farin cikine ya hanani in haɗiye
abun da zamu tattauna”.

Mommy na murmushin Farin cikin tace.

“Toh ki bari sai kin nutsu zamuyi waya amma ya jikin ƴar
taki?.”

Zama Ummi ta gyara tare da faɗin.

“Jiki da sauƙi anzo an bata magunguna yanzuma ina ga bacci
zatayi su Asma’u ne suka hanata bacci da surutu”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da faɗin.

“Toh shikenan Allah ya ƙara sauƙi”.

Ameen Ummi ta amsa kana sukayi sallama.

 

Acan gadon Khausar kuwa ganin ta samu bacci ne yasa Asma’u,
Asiya Dije fitowa.

Fitowar su yayi daidai da ɗaga wayar Lalla Hafsat ta manna
akunnenta maganar minti biyu tayi kana ta janye tare da kallon Asma’u da
shigowanta Falon kenan tace.

“Asma’u kizo mu tafi kina da baƙo A Side ɗin Didi”.

Kai ta gyaɗa tare da kallon Ummi batare data bita ba.

Ummi data fahimci tsayuwar da take yasa tace.

“Kije mana”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da bin bayan Lalla Hafsat da ta
fara ta fiya tana isa Falon ta saki ɓoyeyyen ajiyar zuciya ganin Dr Jameel dake
zaune kan 3sitter Lalla Hafsat kuwa direct bedroom ɗin Didi ta wuce.

Cikin tsira mata ido da tarin ƙaunarta dake ratsa duk wani
magudanan jinin jikinsa wanda yake uzzura jabarsa ɗaya danne yayi alƙawarin
tsakaninsa da Allah bazai ƙara kusantar zinaba, ganinta ya sashi sauke numfashi
mai sanyi tare da lumshe idanunsa kana ya buɗe su akanta tare da cewa.

“Ƙaraso ki zauna anan”.

Ya faɗa yana nuna mata gefensa cikin wani irin yanayi mai
tattare da kunya ta nufi gefensa ta zauna kana ta gaishesa amsawa yayi yana mai
tsira mata idanu tare da shaƙar daddaɗan ƙamshin hunran data shafa Cikin sauƙe
numfashi yace.

“Albishir My Asmeey”.

Idanunta aƙasa ta motsa laɓɓanta tare da faɗin.

“Goro”.

Yana binta da wani sihirtaccen kallo yace.

“Fari ko Jaaaaa”.

Murmushi ne ya subce mata asaman laɓɓanta jin yanda yaja
kalmar Jaaa ahankali tace.

“Fari ƙall”.

Zamansa ya gyara fuskarsa ɗauke da ƙayataccen murmushi dake
bayyana farin cikin dake ciki yace.

“In sha Allah gobe, da Abualeey, Galadima, Waziri da Abban
Zakariyya da ƙanin Abbanshi zaku tafi, saboda za’a je ayi tambayar Aurenmu”.

Tafin hannunta ta sanya ta rufe fuskarta kana ta saki
murmushi mai ɗauke da kunya kafin ta ɗago kanta tare da cewa.

“Allah ya kaimu Allah kuma ya mana zaɓin abinda yafi
Alkhairi”.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum amma dai kinyi farin ciki ko?”.

Kai ta gyaɗa still hannunta na saman Fuskarta.

 

Cikin son janta da hira ya gyara zamansa tare da cewa.

“Kuma harda batun Asiya da Zakariyya ma duk za’a yi tambayar
kinsan shi Zakariyya ya riga ya koma Indi’a amma in Sha Allah yace bazai daɗe
ba zai dawo saboda yana so ayi abin cikin ƙanƙanin lokaci in Allah ya yarda”.

Ahankali tace.

“Ayyah Allah dai ya mana zaɓi mafi Alkhairi”.

Cikin tarin ƙaunarta yace.

“Ameen nan suka ɗan ci gaba da hira”.

 

Lalla Hafsat da Lalla Khadijah kuwa, duk suna ɗakin Didi
hadimai na shirya musu kayansu dan yau da dare Lalla Khadijah zata koma
gidanta. Lalla Hafsat kuwa ƙarfe shida na safe na safen gobe jirnsu zai tashi
zuwa Mexico.

 

Su Ummi kuwa ƙarfe sha daya zasu tashi.

Wanda kuma da pravate
jet zasu tashi so kai tsaye Adamawa jirginsu zai sauƙesu, wanda tunima
sun samu amincewa da sahalewar sauƙansu a Yola international airport, kassn
cewar abune na manya ga kuma su Sheykh Jabeer da sune masu Jihar.

 

 

Acan ɓangaren Khausar kuwa bacci ne mai nauyi mai cike da
gajiya takeyi.

 

 Yayin da aɓangaren
Moddibo ma hakan ne ya kasance sosai yayi bacci kiran sallar la’asar ne ya
tashe sa yana tashi yaji jikinsa yayi sakayau alamar zazzaɓin ya sauƙa, cikin
jin daɗi yasa hannunsa bisa mararsa yana shafawa jin maransa tayi sakayau wani
makirin murmushi ne ya subce mishi sai kuma ya lumshe idanunsa wani irin farin
ciki yake ji mara misaltuwa gami da nitsuwa salama kwanciyar hankali da
cikekkiyar lafiya sai kuma zazzafan shauƙi.

Da Zaran ya tuna wasu abubuwa da suka gabata sai ya saki
murmushin.

A fili yace.

“Wai Wayyo Didi zai kasheni Yah Mu’allim zan mutu”.

Sai kuma ya ɗan jujjuya idanunsa tare da cewa.

“Farar kura ba, *Minha Vidaa* ga tsoro ga ban tsoro, ga
tsiwa ga raki ”.

ahankali ya shiga toilet ya sakaraa kanaa ruwan ɗumi kana ya
daura alwala ya fito cikin wani tattausan yadi fari ƙall ya shirya kana ya
feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi a bedroom ɗinsa yayi sallan
azahar daya riskeshi yana bacci, kana ya wuce masallaci yana mgnar zuci.

“Sai na hukuntaki da sani makarar samun jam’i da kikeyi
kuwa”.

 

Khausar kuwa kafin akira La’asar ta farka tana tashi Ummi ta
sake bata abinci taci kana tace.

“Toh tashi kiyi wonka kiyi salla”.

Kai ta gyaɗa tare da miƙewa tsaye ga mamakinta sosai ciwon
yayi sauƙi sai kaɗan-kaɗan da takeji alamun mgni yayi aiki.

Bayan tayi wanka ta sauya kaya tayi sallan azahar da la’asar
ɗin.

Tana bisa sallayar Ummu ta ɗauko mata Magungunan _Aunty
Aysha Aliyu Garkuwa_ ɗan bokatjn wata gumbar madara mai haɗe da kwakwa ta miƙa
mata, ba musu Khausar ta karɓa ganin yadda Aunty Hajara ta tsareta da idanu.

A hankali ta fara ci tana haɗawa da kwakwar gumbar nada ɗan
karen daɗi shiyasa ta ci mai ɗan yawa.

 Sai kuma ta amshi
gorar da take miƙamata wanda na tsumin riɗine da kuma tsimi zuma a cup ta haɗa
mata su.

Cikin tura baki tace.

“Ayyah Aunty Hajara cikina ya cika fa”.

Da sauri ta ɗan sa cup ɗin a baki sabida hararar data watsa
mata.

Ajiye kofin tayi bayan ta shanye.

Sai kuma ta kalli Ummi dake cewa ki shiga Bathroom na haɗa
miki ruwan ɗumi ki zauna a ciki, kai ta gyaɗa kana ta shiga.

 

Toilet ta tayi tsarki da ruwan ɗumi kana ta shiga cikin
wanda Ummi ta haɗa matan.

Wanda yaji turaren tsarki
ta fito.

Tana baza ƙamshi ita kanta in ta ɗan sunkuyo da kanta sai ta
Lumshe idanu sabida yadda take baza ƙamshi ga kuma kullacar sirri da yafi komai
mata daɗi, shiyasa take nace masa wurin shafawa ganin ba kowa a ɗakin ne yasa
ta fita falon tana jin zazzaɓin ya sauƙa kana zugin da ƙasanta ke mata ma ya
ragu sosai.

 

Haka dai yinin wannan ranan Khausar da Moddibo sukayi yinin
jinya kuma Alhamdulillah jiki yayi sauƙe…

 

Moddibo kuwa yana dawowa masallaci part ɗin Didi ya wuce.

Allah ya sani so yake ya ganta yaga yanayin jikinta amman ya
rasa ta yadda zai nematan haka yasa ya miƙe da nufin zuwa side ɗin dasu Ummin
suke kuwa sai ya sauya hanya tare da komawa side ɗinsu Allah ya sani kunyasu
Ummi yakeji, kuma tsoron wannan tsohuwar mai Shegen baki yakeji kada ta
kunyatashi.

 

Bayan sallan isha akazo aka ɗauki Lalla Khadijah ta koma
gidanta.

 

Misalin ƙarfe tara da kwata, Ummi ta kalli Khausar dake
kwance gefenta tace.

“Khausar kada kiyi bacci
anan fa, tashi ki tafi dakin mijinki”.

Cikin tsinkewar zuciya ta zazzaro idanunta waje, tare da
saurin kallon Ummi tana mai girgiza kai kana tace.

“Na shiga uku Ummi dan Allah, ki barni in kwanan ni bazan
koma canba wlh anan zan kwana”.

Kai ummi ta girgiza tare da faɗin.

“Nan kuma Khausar bayan gacan ɗakin mijinki a’a bazai
yiwuba. maza tashi ki tafi”.

Da sauri Ummi ta zuba mata ido jin ta fashe kuka tsakaninta
da Allah kuwa take kukan. dashi tana yarfe hannu tace.

“Ni dai dan Allah Ummi ki barni mu kwana anan, wlh tallahi
bani da lafiya dan Allah ki barni in kwana kusa dake”.

Asma’u dake gefe tayi murmushi tare da gyara kwanciyar ta.

Ummi kuwa ganin yanda take kuka da faɗin baza ta je bane
yasa tayi shiru…

Sai kuma ta jinjina kai jin Innayi na cewa.

“Ba komai Ummin Jameel barta ta kwana a nan ɗin, gobe ina
zata ganku”.

Ita kam Khausar ido ta rufe tana mgnar zuci.

“Yoh ai tarema zamu tafi dan wlh ni dai bazan zaunaba”.

 

Zuwa lokacin karfe goma harda kota….

 

Washe gari da asuba ana fita masallaci Aka kai Lalla Hafsat
da Hakim Airport.

Bayan ta sallami su Ummi.

Bakwai dai-dai jirginsu ya ɗags zuwa Mexico.

 

 Abujan Nigeria, karfe
takwas dai-dai Unclee Naseer ya bar gidan.

Tun fitansa kuwa Amina ke konce a tsakiyar falon bisa
Carpet.

A hankali take sauke numfashi sabida ɗan baccin ɗaya fara
fizgarta.

Cikin baccin da ya fara nisan, ta rinƙa jin hucin macijin
nan, sai kuma tayi saurin buɗe idanunta sabida jin sanyin jikin macijin yana
ratsa cikinta yana ɗan jujjuya kanshi tare dayin sama da kan nashi da ya shigar
ta ƙasar ƴar rigar dake jikinta.

Wani irin fitinennen karkarwa jikinta ya fara, tare da
zazzaro idanunta baki ɗaya lokacin da taji macijin nan ya manna bakinshi kan
nimple dinta na hannun dama yayiwa nimple din wani irin damƙa da karf….

 

 

*Littafin Sakayya dai na kuɗi ki biya  karanta cikin aminci da salama ba haƙƙin kowa
a kanki 1k ne kacal 0661110170 gtbank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo min
shaidar biyanki ta wannan number 09097853276 in tura Miki ki karanta cikin
aminci*

Leave a Reply

Back to top button